Showing 225001 words to 228000 words out of 350584 words
ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.
Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.
Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.
🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*
By
*GARKUWAR FULANI*
Wani irin maraitaccen numfashin suka ja kana suka sauƙe a tare,
Kerma da kerketa jikin Jannart ya fara wanda yasa ta fara kokawa da nnumfashindake gab da barin gaggan jikinta.
Shi kuwa Rayyern wani amintaccen lasa yayiwa tsinin hancinta, kana a hankali ya kauda fuskarsa gefe kaɗan ya manna lips ɗinshi gefen kuncinta.
Tare da fara ƙoƙarin buɗe narkakkun idanunsa,
da sauri ya ɗan janye jikinsa baya kaɗan ganin yadda hawaye ke kwaranya a fuskarta wani na korar wani, tsoro da firgicin data faɗa ya bayyana ƙarara.
A hankali a kuma jere ya fara sauƙe numfarfashi.
Fuskanshi ya kauda gefe tare da taune laɓensa na ƙasa.
“Lfy lau.”
Yayi maganan cikin wani irin yanayi mai wahalar fassaruwa, tare kuma da zuba mata narkakkun idanunsa, way’anda suka haifar mata da kasala, lokaci daya kuma tsikar jikinta suka shiga mimmik’ewa.
Kasancewar ba zata iya jurewa Kallon cikin idanunsa bane kuma, yasa ahankali tayi kasa da kanta, tare kuma da fesar da wani irin numfashin da ta samu ya dai-dai-ta fitar numfashin ta, yayinda mamakinsa ke ratsata ganin yadda ya wani basar kamar ba shiba.
Duk sai taji ya cika mata idanu, Yayinda yayi mata kwarjini na gasken gaske, sanadiyar kayan dake jikinsa, way’anda sukayi matuk’ar yi masa kyau da tsare fuska da yayi yana mai lasan Chocolate din hannunsa.
Shikuwa Rayyern dake tsaye har yanzu kallonta yakeyi, baya ko k’yafta idanunsa dake kokarin lumshewa, sosai yakejin wani irin abu na musamman na yawo acikin jikinsa wata iriyar fitinenneyar kasala yakeji tana lullubeshi lasan Chocolate ɗinsa yake tamkar zan cinye da ledan.
K’amshin jikinta dake ratsa cikin hancinsa ne kuma, ke kara kashe masa jiki, tare da narkar masa da zuciya.
Ahankali batare kuma da ta d’ago ta kalleshi ba, Cikin sanyin murya tace.
“Abbana yace na gaisheka.”
“Uhummm ngd.”
Ya fad’a kasa-kasa tare kuma da, ci gaba da tsare ta da idanunsa, yana meyi mata wani irin kallo, mai dauke da abubuwa daban-daban kana yana jujjuya tsinin harcensa akan Chocolatinsa.
Kallon da yasa duk takejin kanta arikice, haka kuma Kallon da yasa kirjinta soma bugawa da sauri-sauri.
Yayinda acikin zuciyarta kuwa so take ta janye jikinta baya, daga kusancin da suka samu ita da shid’in, amma kuma kwata-kwata ta kasa yin hakan.
Saboda hakanan taji batason yin nesa, da k’amshin turarensa wanda yake gauraya da numfashinta.
Idanunta ta kuma lumshewa, saboda jiyo sautin bugun zuciyarsa da tayi ne kuma, yasa ahankali tace.
“Kaci abinci?”
Yanayin yanda tayi maganan da rauni ne, yasa shi kasa amsa mata, saima idanunsa daya lumshe tare da karyar da wuyansa gefe sabida wani irin fitinennen abu da yaji yana rufeshi.
Jannart kuwa jin bai amsa mata bane yasa asanyaye ta sake cewa.
“Kaci abinci?”
Again shiru yayi bai amsa taba, saidai kuma ya bud’e idanunsa, inda ya zubawa kyawawan lips dinta idanu.
Itakuwa jin yayi shiru akaro na biyu ne, yasa ahankali ta d’ago Kanta ta kalleshi.
Hakan kuwa shi yasa idanunsu sarkewa dana juna.
Tamkar Wacce aka jonawa shokin haka taji jikinta, saboda Kallon nasa da tayi, duk da hakan kuwa da taji baisa ta iya janye Idanunta daga cikin narkakkun idanun nasa ba.
Saima kwaɓe fuska da tayi, tare da dan yin rau-rau da idanunta da suke fidda sheƙi na musamman alamun hawaye na tsastsafo wa, cikin yanayin kula mai had’e da rauni murya a sanyaye tace.
“To ba Inata maka magana kuma kayi shiru ba, Kaci abinci?”
Ta kai karshen maganan tana me Kallon, faffad’an chest d’insa, kasancewar bai ida sa aninayen gaban rigar duka bane, kuma yasa take iya hango hasken fatan kirjin nasa.
“Naan..”
Ta kuma kiran sunansa a dan tsorace, saboda kasa amsa mata da taga yayi sai take zaton ko ciwon ne, kana idanunta nuna mata suke kamar bai fidda numfashin ma, Shi kuwa Rayyern gaba ɗaya azabebbiyar kasala da bakon yanayi yakeji yana kashe dukkanin sassan jikinsa gaba ɗaya, haka yasa yake jin lips ɗinsa sun masa nauyi bare ya iya amsa mata, saima kallonta da yake tamkar yaga bakuwar halitta.
Idanun nasa dake kallonta ya rufe tare da fesar da numfashi lokacin da yaga hawayen idanunta sun kwaranyo, shi kadai yasan me yakeji aduk sanda tayi masa magana, da muryar rauni mai haɗe da shagwab’ar da ita batama san tanayiba, ba a iya jikinsa kawai ba, har dick d’insa motsawa take, yakanji sa awani yanayi na daban.
Labb’an bakinsa ya dan motsa kana ahankali yace.
“Baki banibaaa.”
Yanayin yanda taji sautin muryar tasa ne, kuma yasa ta d’agowa ta kalleshi.
Shikuwa batare daya bata daman ganin cikin idanunsa ba, ya d’an rab’a ta gefenta ya fita zuwa falo yana mai tafiya cike da kasala.
Bayansa tabi da kallo, kana ahankali itama ta rufa masa baya, Ganin ya zauna akan kujera ne kuma yasa ta wucewa kitchine.
Plate ta dauka tare da wani cup, wanda ta tari ruwan zafi acikinsa ta dispenser, bayan ta saka ruwan zafi acikin cup dinne kuma, ta bud’e roban zuma ta d’an zuba mai d’an dama aciki.
Bayan ta kammala ne kuma ta dawo falon hannunta rik’e da plate da kuma cup din ruwan zafi da zumar.
Yana nan zaune a inda tabarsa, saidai idanunsa alumshe suke, Yayinda ya daura kafafunsa akan table kana ya jingina kansa saman kujera.
K’arasowa inda yake din tayi, hade da durk’usawa ta zauna akan k’afafunta.
Spoon din dake cikin cup din ta dan motsa, kana ahankali kuma ta d’ago Kai ta kalleshi.
“Naan.”
Ta kira sunansa cikin tausasa murya.
Kanshi ya d’ago ya fuskanceta, tare da fesar da sassayan numfashin lumsassun idanunsa ya bud’e tare da sauke su akanta.
Itakuwa Ganin hakanne yasa ta miko masa, cup din tare dayi masa alama akan yasha.
Cup din da kuma y’an yatsun hannunta dake rike dashi, ya kalla kana ahankali ya kuma dawo da kallonsa gareta, saidai ayanzu Kallon da yake mata, ya banbanta da sauran, domin kallone mai dauke da alamar tambaya.
Fahimtar abunda yake nufi ne kuma yasa ta, kwantar da kanta asanyaye tace.
“Take it please zai taimaka wajen, rage maka ciwon ciki, kuma Abbana ne yace kana sha saboda yana magananin ciwon ciki.”
Ta kai karshen maganan tana me sake miko masa cup din.
Shikam idanu kawai ya zuba mata, aransa yana me mamakin wai, black tea ne zai rage masa ciwon ciki hmmm dan baisan da zuma a cikiba.
“Naan kasha mana please.”
Ta yi maganan saboda ganin har yanzu ita yake kallo.
Ahankali yasa hannu ya karb’i cup din, akokarinta na sakar masa cup dinne kuma, hannunsu ya hade awaje daya.
Da sauri ta zare nata hannun saboda koyaya, Idan wani sashi na daga jikinsa ya taba ta.
To haka zatana jin tsikar jikinta na tashi.
Plate din da ta kawo din ta dauka, tare da bud’e ledan Sabor de la vidda restaurant din daya kawo, ta zuba masa abincin acikin plate, hade da kawo masa gabansa ta ajiye, Ahankali kuma ta d’ago ta kalleshi.
Ganin idanunsa ba’a kanta suke bane, yasa ta komawa tadan zauna akasa kusa dashi, tare da zubawa yatsun k’afarsa idanu.
Duk abunda takeyi din kuma yana kallonta ta gefen idanunsa, Yayinda ahankali kuma yake sipping black tea din da takawo masa wanda yaji zaƙin zumar ya mishi daɗi toh dama ya Rayyern da zak’i.
Kasancewar tea din baida yawa, shiyasa in a few minute ya shanye, tare da ajiye cup din.
Ahankali ya dan kalleta ta gefen ido, tare kuma da daukan spoon ya soma cin abincin da ta ajiye masa.
Daga gefe guda kuwa anutse yake karewa, shigar dake jikinta kallo, musamman yanda dogon gashinta ya kwanta akan gadon bayanta.
Y’an yatsun hannunta da ta d’aura akan, carpet ya kalla kana ahankali kuma ya janye plate din abincin daga gabansa.
Kasancewar kuma tana Dan yawan satan kallonsa, shiyasa ganin ya ture plate din abincin gefe, yasa ta daukan sachet din maganinsa, dake kan table ta b’are magungunan tare da mik’a masa.
Babu musu kuwa ya karb’a hade da zuba, k’wayan maganin abakinsa, kana ya bi da ruwa.
Agogon dake daure atsintsiyar hannunsa ya kalla, Ganin 5:00 dai-dai ne kuma yasa shi mikewa tsaye, tare dasa hannu ya gyara aninayen gaban rigarsa.
Ganin hakanne kuma yasa ta d’ago, da kanta ta kalleshi cikin tausasa murya tace.
“Fita zakayi ne?”
Kansa ya gyad’a mata alaman “Eh.”
Batare kuma daya juyo ba ya nufi hanyar fita daga falon.
Itakuwa Jannart bayansa tabi da idanu, cikin sanyi hade kuma da tausasa murya tace.
“Adawo lafiya Allah Ya tsare.”
Saboda jin abunda ta fad’a d’inne kuma, ya sashi tsayawa da tafiyan nasa, Ahankali ya juyo ya sauke idanunsa akanta.
Domin Wannan shine karo na farko, da yaji tayi masa addu’a alokacin da zai fita.
Idanunsa ya lumshe tare kuma da sauke ajiyar zuciya, cikin kuma wani irin yanayin daya samu kansa ya amsa mata da.
“Amin.”
Kaitsaye kuma ya fice daga cikin falon, yana me Dan kad’a car key din dake hannunsa.
Jannart kuwa harsai da ya fice sannan ta janye Idanunta, daga kansa Ahankali ta sauke ajiyar zuciya, tare da jawo plate din abincin daya rage ta soma ci.
Hakanan duk sai takejin kanta wani iri, saboda nasihan da Aunty Fauziya D Sulaiman din tayi mata.
Wanda Ada ko sau daya bata tab’a jin, cewar ba akan dai-dai take ba, kasancewar batasan ya rayuwar aure yake ba, akullum kawai tana rayuwa ne kamar yanda, Rayyyern din ya nuna mata, rashin kulasa da kuma rashin shiga sabgoginsa sabida ita ta rayune akan a bata umarni tabi, yadda mutun keso haka take masa.
Ahaka dai ta kammala cin abincin, bayan ta kimtsa wajenne kuma, kaitsaye ta wuce bedroom d’insa.
Koda ta shiga bedroom din, komai nasa need yake babu wani datti.
New bedsheet ta shumfud’a masa, tare kuma da blanket mai taushi, kana ta kunna turare mai dadin kamshi acikin dakin.
Cikin yan mintuna kadan ta kyale masa dakin, ga kuma kamshi da yake tashi tako Ina.
Bayan ta kammala gyaran dakinne kuma, ta wuce toilet inda ta wanke masa shi tsab.
Koda ta fito daga toilet din, yalwataccen hasken dake cikin dakin ta kashe, tare kuma da ficewa ta jawo kofar ta rufe.
Kaitsaye daga dakin nasa kuma kitchine ta nufa, atsanake ta soma wanke plate din da suka b’ata.
Tana cikin wanke plate dinne kuma, karamar wayar daya bata din ta soma kara.
Ganin sunan Aunty Fauziya na yawo akan screen din wayarne, kuma yasa ta dagawa tare da kara wayan kan kunnenta.
Saidai kuma jin shiru ba’ayi magana bane, yasa ta gyara tsayuwarta tare dayin sallama.
Daga can b’angaren Aunty Fauziya ta sauke ajiyar zuciya, kana cikin kulawa tace.
“Allah yasa dai kinyi abunda na sakaki din, bawai kin tsaya nuna sanyin halinkin nan ba, Jannart nasanki da sanyi.”
Murmushi Jannart din tayi kana murya atausashe tace.
“Nayi duk abunda kikace My Aunty, yanzu ma Ina kitchine ne saboda ya fita.”
Murmushin Jin dadi Aunty Fauziyan tayi, cike dajin dadin daukar maganarta da Jannart din tayi tace.
“Masha Allah haka akeso ai, yanzu ki samu ki dafa masa abinci kafun ya dawo, kinsan maza dole sai ana kula da cikinsu.”
Shiru ta d’anyi na wasu mintuna kana asanyaye tace.
“My Aunty ai babu kayan abinci agidan, tunda mukazo ma ban tab’ayin girki ba, shi yakeyi mana order daga restaurant's.”
“Jannart ordern abinci kuma?”
Aunty Fauziyan ta tambaya da mamaki.
Jannart din kuwa jiki asanyaye, gudun kuma kar ace tayi wani laifin tace.
“Eh haka yakeyi kullum, saboda babu kayan provision agidan, kuma bawani cin abincin yakeyi sosai ba shiyasa, nafi tunanin kuma haka tsarinsa yake, saidai kafun mu taho nan din, lokacin da muke gida yakanci abinci sosai wasu lokutan.”
Ajiyar zuciya Aunty Fauziyan ta sauke kana cikin kulawa tace.
“To baga irinshi ba Jannart, tayaya kike tunanin zai iya jurewa cin abincin kasar da bata shi ba, wani abincin ma da zaki ganshi tamkar ruwa ne aka zuba masa ganyayyaki, ya zama dole ki tashi ki kula da mijinki Jannart, maganar kayan provision kuma, kece zaki fad’a masa cewar ya seyo kuna da buk’ata, duk da baizama Lallai ku samu abunda kukeso ba, amma dai ki dafa da kanki yafi ace sayowa kukayi, nasan basu da wasu kayan abinci irin namu, amma ai kin iya sarrafa girkin zamani, sai kiyi kokari kina yi muku kuna ci, dan Allah Jannart ki kula sosai, dole sai kin tashi tsaye, kin tarairayi mijinki, saboda ahar kullum shine sama dake.”
Sassanyar ajiyar zuciya Jannart din ta sauke, cikin gamsuwa da kalaman Aunty Fauziyan kuma tace.
“Shikenan My Aunty Insha Allah zanyi mishi magana, nagode sosai.”
“Babu godiya atsakaninmu Jannart, fatana dai kawai shine ki zama daya daga cikin matan, da suka San daraja da kuma kimar mijinsu, yanzu ki k’arasa ayyukan da kikeyi, watakila sai zuwa Gobe zan kuma kiranki.”
“To My Aunty ahuta gajiya.”
Jannart din ta fad’a
Cikin sauri Aunty Fauziyya tace.
“Yauwa kinga zan mance abinda yasa na kiraki ko.
Dama jiya muke mgn da Hajia Rabi'ah, kin san itama maigidanta yana Mascow to jiya da muka haɗu wurin aiki take cemin, next week zata taho wurinsa”.
Cikin jin dadi tace.
“Kai Alhamdulillah my Aunty in tazo zatazo wurina ko?”.
Murmushi Fa'iziyya tayi tare da ci gaba da cewa.
“Akwai wasu kayyakine na gani a wurin AYSHA ALIYU GARKUWA, kayane irin namu na mata da kuma kayyakin ƙamshi toh nama saya miki, na bata 80k tayi miki haɗin mai kyau nasa tasa miki komai ɗan dai-dai, in sha Allah zan bawa Hajia Rabi'ah, zata kawo miki”.
Cikin tsananin jin daɗi tace.
“Allah sarki my Aunty ngd Matuƙa Allah ya biyaki da mafi kyawun sakamako”.
Amin Ya Allah ta amsa cikin son yarinyar.
Daga nan sai sukayi sallama murmushi Jannart tayi
tare da zare wayar akunnenta.
D’an Jim tayi nay’an wasu mintuna, kana atsanake kuma ta cigaba da aikin da takeyi.
Bayan ta kammala wanke wanken ne kuma, ta dawo falo tare da kunna tv.
K’aramar wayar dake rike a hannun nata ta kunna, tare da yin dialing numbern Mamy.
Cikin sa’a bugu biyu kuwa Mamyn ta d’aga.
“Assalamu Alaikum Mamy barka da yamma ci.”
Jannart din ta fada cikin girmamawa.
Mamy kuwa jin muryar Jannart dinne, yasa ta fadada fara’arta, tare da amsa mata sallaman, cike kuma dajin dadin kiranta da Jannart din tayi tace.
“Yauwa Jannart barkadai, ya kuke ya mai jiki ya kuma fama da sanyi?”
Murmushi mai sauti Jannart din tayi, kana anutse tace.
“Alhamdulillah Mamy, jikin kam yayi sauki sosai, saidai amma fa muna shan sanyi, Allah Mamy duk nayi kewarku sosai.”
“Muma haka Jannart munyi kewarki sosai, ko d’azu ma saida Ramadan yayi korafin wai ya gaji, zai biyoku Mascown zaizo kiyi mishi miyan kase, nace masa Lallai kuwa bazai tab’a cin miyan kase ba ashe, indai acikin Mascow ne.”
Dariya sosai Jannart din tayi, tare da gyara zamanta, cike da kewarsu tace.
“Allah sarki Ramadan Idan muka dawo Insha Allah, zanyi mishi miyan kase, Mamy Ina Abba da Baba Maud’o.”
“Sunanan lafiya Jannart, shekaran jiya ma Baba Maud’o ke tambayanki, saboda yace Rayyern kam suna waya dashi sosai.”
“Allah sarki Baba Maud’o tunda muka tafi bamuyi magana ba, amma Insha Allah yau zan kira Ramadan sai ya had’amu mu gaisa.”
“Aikuwa da kin kyauta saboda yana ta tambayanki.”
Mamyn ta fad’a cikin kulawa.
Hira suka Dan tab’a da Mamyn kafun daga bisani sukayi sallama.
Mamyn na kashe wayar kuwa, Jannart tayi dialing numbern, Ramadan saidai jin wayar tasa bata shiga ne, yasa ta ajiye nata wayan tare da kwanciya akan kujera, kana ahankali ta maida idanunta ga tv.
Tananan cikin falon azaune kuwa, har saida aka soma kiraye kirayen sallan magriba, kafun ta tashi ta wuce daki.
Koda ta shiga dakin kayan dake jikinta ta cire, tare da wucewa toilet kaitsaye tayi wanka.
Koda ta fito daga wankan, mai da powder kawai ta shafa akan fuskarta, sai kuma oily lips stick.
Bayan ta gama shafan ne kuma, atsanake ta nufi wajen trolley dinta, bud’e trolleyn tayi tare da ciro wani riga da sket.
Mai kalan baki, Koda ta sanya kayan cib cib sukayi mata ajiki, Yayinda lafaffen cikinta ya bayyana.
Bayan ta saka d’aya daga cikin hijab dinta ne kuma, ta tada sallah, saboda zuwa lokacin tasan anshiga sallan magriba.
Koda ta idar da sallan kuwa bata tashi akan sallayan ba, har saida ta idar da sallan Isha.
Ahankali ta murd’a handle din kofar dakinta ta fito, zuwa falon.
Zama tayi akan kujera tare da lumshe Idanunta, cikin sanyi take sauraran karan tv’n dake tashi acikin falon.
Dai-dai lokacin Ya bud’o kofar falon ya shigo, hannunsa rike da ledodin Halal Restaurant.
Jin alamun shigowarsa ne kuma, yasa Jannart din bud’e Idanunta, Ahankali ta sauke ganinta akansa.
Kasancewar kuma