Showing 90001 words to 93000 words out of 350584 words
hauhawa yake, tayaya ne za’a samawa al’umma sauk’i, musamman manoma, wanda sune ma suke noma abincin amma kuma Idan ya shigo kasuwa sai yazo yafi karfinsu, shin wacce shawara zaka iya bawa manoma?.”
Numfashi ya dan fesar ta bakinsa, saboda yanda yaji labbansa sun soma gajiya da yawan motsasu da yake.
Hakanne kuma yasa batare daya dago ya kalli ko cameran ba, saidai atausashe yace.
“Shawarar da zan iya bawa Manoma itace, duk wani manomi Idan har ya noma abunda zaici, To kada yayi gangancin saidawa, har sai ya tabbatar daya ware ishashshen abincin da zai isheshi, har na tsawon wata shekarar da zai sake noma wani abincin, kafun nan sai yazo ya saida wanda zai sayar, saboda gudun kada ayi gaban mai haƙar rijiya. kai ka noma ka gama shan wahala, sannan kuma ka tattara ka sai dashi lokacin da yake araha, bayan y’an wasu watanni sai yayi tsada, ga kuma wanda kake dashi ya riga ya k’are ga damuna ta sako sama ruwa ƙasa ruwa, fita nemowar ma wata rana sai ya gagara, kaga kenan nakan daka saida shi zaka sake zuwa ka saya, akan farashi mai masifar tsada, kenan Kai Manomi kaine ka wahala a banza.
Sannan kuma ya kamata manyan kamfanoni su dinga tausayawa talakawa, su daina yi musu irin wannan hawan k’awaran, zuwa su sai abincin manoma tun yana gona basu shigo dashi gari ba su kuma manoma ku farga da wannan sagegeduwar da akeyi muku.
Sannan kuma su manoman kansu, su daina sayarwa masu manyan kamfanoni abincinsu tun yana gona, saboda wasu tun abunda suka noma yana yabanya suke saida shi, atunaninsu ko da ace abun da suka noma din baiyi kyau ba ko sanadin fari ko tsuntsaye ko kwari ko tsutsa, su dai sun samu kudi, da yawan mutane basu san al'barkar dake cikin kayan gonansu ba, saboda haka yana da kyau, ka dinga girbe abunka kana gyarawa da kanka, ka kididdige abinda ka samu ka ware na buƙatunka kafun ka mik’ashi ga wasu, sannan kuma duk wani manomi yayi kokarin saida abincin daya noma, akan farashi mai kyau, saboda ko yaya guminsa ya keci.
Domin shi kadai yasan wahalar daya sha wajen noma ta, sannan yanzu Idan akayi dubi, gaba daya manoma da talakawa su suke shan wahala, musamman Idan aka shiga cikin damuna, haka komin ruwa da iska zasu tsaya neman abunda zasu rufawa kansu asiri suyi noma dan ciyar da al'umma duk kudinka fa, in manomi baiyi noma koda kuɗin ka bazaka samu abincin ba, shin zakaci kuɗin naka ne!!!?. Sannan ku kuma y’an kasuwa da kamfanoni masu karawa kayan abincinsu kudi, ba komai kuke ciba face *RIBA* haramtacciya, wanda kuma kowa yasan hakan ba abubane mai kyau bane, ga wanda suke sayan abinci su b’oye sai yayi tsada su fito dashi, suma duk Allah naganinku, kuma Allah da kansa baya tausayawa wanda baya tausayin na kasa dashi.”
Kai gaba daya mutanen dake boye abayan cameras din suka jinjina, hatta MD da kansa shima ya samu cikakkiyar gamsuwa da bayanan da suka fito daga bakin Dr. Rayyern din.
Ba kuma a iya cikin tv station din ba, har acikin gaba daya k’asar tamu, mutane da yawa dake Kallon Live Program din sun samu cikakkiyar gamsuwa, Yayinda kalaman Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din ya ratsa zuk’atansu, ciki kuwa harda mafiya yawan manoma da suke kallon shirin, sabida Tashar Arewa 24 TV tayi zarran birni da ƙaune suna kallonta maza da mata manya da yara.
Adai-dai lokacin kuma Abba Kabir zaune yake agaban tv yana Kallon shirin, shi kansa ya gamsu da kalaman Dr. Rayyern din, saidai kuma sosai zuciyarsa ta cika da tsananin mamakin, ganin da wanda Jannart din ke hira yau.
Acan babban falon gidansu Jannart din kuwa, Alhaji Idi Sale Dakata, Dr. Lukman da kuma Alhaji Abdu Tababa ne, zaune sun zubawa babban TV plasma din dake cikin falon idanu.
Wanda kuma yanzun akayi musu kira na musamman, akan su kunna tashar Arewa24 Dan Ganin hirar da akeyi da Dr.Rayyern din.
Hakance kuma ta kasan a wurare da dama yadda wasu ke kiran wasu manyan ƙasar suna shaida musu su kunna tv tashar Arewa 24 TV suga program ɗin da akeyi da Dr Rayyern Mai-nasara.
Jin abubuwan da Rayyern din ya fad’ane kuma, yasa Alhaji Abdu Tababa yin k’wafa, kana cikin takaici yace.
“Amma dai wannan yaron anyi d’an iska, mai tsaurin ido, kujifa abunda yake fad’a, wai gwamnati ta rushe asibotin kudi ta inganta nata, Lallai yaron nan bashi da tsoro.”
“To shi nashi asibitin na uban meyene, shegen yaro mai jajayen kunnuwa.”
Cewar Dr. Lukman da yakejin kansa kamar ya kurma ihu yayi fiffige yaje ya shaƙo wannan yaron.
Yayinda Alhaji Idi Sale Dakata kuwa ya rumste idanunsa, saboda shi ayanzu ko son Ganin yaron bayayi, hasalima gaba daya tunaninsa ya tafi ne akan yanda zai ga bayan Rayyern din, saboda al'ƙawari ne da yayiwa kansa cewar saiya b’atar da yaron daga Doron k’asa.
Acan cikin tashar ta Arewa24 kuwa, Jannart ce ta sake gyara zamanta, batare kuma da ita ma ta d’ago kanta ta kalli Dr. Rayyern MAI-NASARA dinba tace.
“Toh Doctor mu dan koma baya.
Kaba da shawara akan cewar aduk’ar da asibitotin kudi, a tada na Gwamnati, ta hanyar zuba ingantattun likitoti da kuma kayan aiki, To irinku fa masu asibitotin kudi yaya zakuyi kaida ire-iren ka masu privet Hospital's, kodai kuma zaku dawo aiki a asibitotin Gwamnati ne! Ku watsar da naku asibitocin!!?.”
Cikin gamsuwa da yarda da kai yace.
“Kwarai kuwa, saboda ai hakan bawai gazawa bace, Indai muka had’e hannu da Gwamnati dan musamar da ingantaccen kulawa ga al’umma, To mu hakan kamar alkhairi ne agaremu, ba kuma najin hakan zai tauyemu ko ya ragemu da wani abu.”
Ya fad’a atak’aice saboda ya fara gajiya da amsa tambayoyin yarinyar mai shegen baki cai-cai surutu tuni yawun bakinsa sun kafe.
Hannunshi yasa ya ɗan shafa sajenshi har zuwa kan lips ɗinshi sabida ji yayi kamar bakinshin yayi tsawo ne da surutu.
Jannart kuwa, again cikin sanin makamar aikinta tace.
“Amma kamar baka goyon bayan duk wani privet hospital, in na fahimceka.
Kuma naga kaima kana da naka hospital din, wanda kuma bana gwamnati bane, ya akayi to hakan ta kasance? meyasa baka had’a hannu da Gwamnatinba!? kun ingata Koda asibiti daya ne!!!?”.
Wannan Tambayar ta saka duk magautan
Dr. Rayyern Mai-nasara dake Kallon tv suka saki Murmushin mugunta, saboda atunaninsu yarinyar ta kawosa makura inda bazai iya amsa tambayoyin nata ba Alhaji Idi Saleh Dakata kuwa.
Saida yaji tamkar ya shiga TV ya goya ɗiyar tasa Jannart, sai yakeji kamar dan su tayi mishi wanna tambayar dan ta kure musushi.
Dr Lukman kuwa hannunshi ya dunƙule tare da jinjinawa Jannart harda yimata alamar kiss dan masifar daɗi.
Ita kuwa Jannart batama san sunayi ba, kuma bada wata manufa tayi tambayarba sai dan dacewar hakan tunda tasan yanada asibitin.
Shikuwa Rayyern ko ajikinsa baiji wani abu ajikinsa dangane da tambayar da Jannart din tayi masa ba, hasalima Dan gyara zamansa yayi, cikin kuma kwarin guiwan da ako yaushe yake tare dashi yace.
“Banyi karatun likita Dan yin aiki akarkashin wani ba, asali Tubalin karatuna shine Idan na kammala na raya asibitin, dake gine tun kan zuwata duniya.
saboda amfanar al’umma, bawai iya mai kudi ba kawai harda talakawa, saboda babu wani wanda, asibitin Mai-nasara Hospital yafi karfin zuwansa, koda kuwa bashi da karfi, Mai-nasara Hospital muna da foundation na taimakawa marassa karfi dashi mukeyin dukkan taimakon daya dace, sannan kuma Mai-nasara Hospital bawai irin asibitotin nan ne da kowa ya sani ba, Ina da confidence akan Hospital dina, ako ina kuma zan fada batare dajin na fadi ba daidai ba!!!.”
Kai Jannart ta jinjina, saboda ayanzu kam amatsayinta na y’ar jarida ta gamsu da duk kalaman mutumin, musamman da ta fahimci with full confidence yake magana, ba irin na wasu mutanen ba, da mafi yawancin maganansu Kame kame da kuma k’aryane.
Domin sometimes ma suna fad’an karyane Dan su kare kawunansu daga titsen yan jarida.
Daga can gefe kuwa, Asiya ce dake tsaye take ta aikin bankawa Jannart d’in Harara.
Yayinda takejin wani irin kuna da radadi acikin zuciyarta, Lallai Tabbas taso ace itace ta samu wannan damar, taso ace yau itace akan stage din tare da mutumin da kyau, nutsuwa da kuma haibarsa suka matuk’ar tafiya da hankalin ta, kana kuma mutumin da take ganin cewa, samun daman magana dashi ma wani matakin nasara ne.
Kamar kuwa yanda Asiya ke jin tukukin bakinciki acikin zuciyarta, haka ma Dr Lukman, yakejin kamar ya shiga cikin tv’n ya shak’o wuyar Dr Rayyern.
Abunda yasan bazai taba samun daman aikatashi ba a gaske kenan.
Kallonsa ya mayar gasu Alhaji Idi Sale Dakata, cikin takaici yace.
“Lallai wannan Dr Rayyern din shege ne, ko ta Ina so yake ya tauyeni, bakinsa baya tab’a mutuwa, kowacce tambaya akwai amsarta acikin kansa.”
Murmushin daya fi kuka ciwo Alhaji Idi Sale Dakata’n yayi, cikin takaicin daya lullub’e zuciyarsa yace.
“Nan kusa wannan bakin nasa bazai sake motsawa ba, wannan alk’awari ne na daukawa kaina.”
Murmushin Jin dadi Dr Lukman da kuma Alhaji Abdu Tababa sukayi, saboda sanin hali irin na Alhaji Idi Sale Dakata da sukayi, Domin sunsan duk abunda yace zai aikata saiya aikata Tabbas.
Ab’angaren Gidansu Rayyern kuwa, Abba Mamy, Ramadan da kuma Riyyam-nsra ne zaune afalo suna kallon shirin, gaba daya sun bada hankalinsu akan shirin, musamman ma Abba, da tunaninsa ya rabu izuwa wani waje na daban.
Kallon Rayyern da kuma yarinyar da takeyiwa Rayyern din tambayoyi yake baya ko k’yaftawa, Yayinda acikin zuciyarsa yakejin wani irin abu na daban.
Su Ramadan kuwa Hamman nasu suka tsurawa ido,suna mai jinjina kawunansu saboda irin amsoshin da Hamman nasu ke bayarwa, yana matukar ratsa zuciyarsu, acikin zuciyarsu kuwa babu wanda bai yaba da irin kyawun yarinyar da takeyiwa Rayyern din tambayoyi ba.
Jannart kuwa, akaro na barkatai ta d’ago ta kalli camera’s din dake haska su, mike din dake gefenta ta gyara, tare da cewa.
“Kamar dai yanda kuka sani, ayanzu zamu bud’e layukan wayoyinmu saboda, masu kira.
Dan fadar ra’ayoyinsu da tambaya, ga numbar layin namu kamar haka...
Tana gama fad’an numbers dinne kuma ta kunna wata waya mai kaman telephone dake aje agabansu, kan wani had’add’en table.
Aikuwa kaman jira ake sukunna layin saiga kiraye-kiraye suna shigowa.
Wanda manyan mutane-ne suke kiran.
Numfashi ta ɗan fesar tare da gyara zamanta.
Kana ta ɗan kalli wayar da wani kiran ya kuma shigowa tun kan ta ajiyeta.
Picking call din Jannart tayi, tare kuma da latsawa tasa wayar a hands free.
Cikin zazzakar muryarta tace.
“Assalamu Alaekum.”
Daga can b’angaren aka amsa mata, da murya irin ta manyan mutane.
Jin hakanne kuma yasa ta cewa.
“Barka da shigowa filin bakon mako.”
“Yauwa Barka dai”.
Aka faɗa daga daya sashin cikin girma.
Ita kuwa Jannart lumshe idonta tayi tare da cewa.
“Ko zamu iya sanin waye akan layi?.”
“Sunana Alhaji Abubakar Ginsau S.A protocol na gwamna, nakira ne kuma Domin na jinjinawa babban Bak’o DR. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, agame da maganganu masu amfani daya fad’a, Insha Allahu kuma maganan zata isa ga kunnen way’anda ya kamata suji, sannan muna godiya k’warai matuk’a, da irin shawarwarin daya bayar.”
Kai Jannart ta jinjina, tare da dan satan Kallon Dr Rayyern din, wanda ya kauda kansa gefe, kamar baiji ana yabonsa ba.
“Girman kai rawanin tsiya.”
Tafad’a acikin zuciyarta, Yayinda afili kuwa cewa tayi.
“To S.A protocol muma godiya muke sosai, sannan bakon mu Dakta shima yana godiya.”
Daga haka kuwa kiran S.A din ya katse, wani kiran kuma ya sake shigowa.
Cikin tashin hankali Dr Lukman ya mik’e tsaye, tare dasa hannunsa ya dafe kansa, zuciyarsa cike da takaici yace.
“Lallai wannan yaron ya shallake duk wani tunani na, ba a banza ba ake kiransa da Mai-nasara ba, tunda gashi yayi sara akan gab’a, daga maganansa har S.A da kansa ya kira, ya kuma shaida cewa maganar zata tafi har wajen governor, wannan wanne irin Dan iskan yaro ne? Mai sa'a”.
Cikin tsananin takaici tsana Alhaji Idi Saleh Dakata ya fesar da numfashi tare da cewa.
“Ai yamafi Dan iska wannan yaron da kake gani Dr Lukman, shegen yaro ne kwance-kwance yake mana, da sannu Idan bamu tashi ba, duk sai yabi ya sare mana duk wani reshen mu, b’arna babba yake aikata mana, batare da ko damuwa da hakan yayi ba, Tabbas kuma ya kafu iya kafuwa, da wayannan kalaman nasa masu ratsa zuciya yake yaudarar mutane, waishi ala dole mai tausayin talakawa, yana abu tamkar Dan siyasan da yake barar neman kujerar takara, hmmmm Lallai zanyi maganin wannan yaron, zan kawar dashi kamar yanda na kawar da way’anda suka fishi tsauri a baya.”
Alhaji Idi Sale Dakata ya ƙare mgnar yana me sakin zazzafan numfashin takaici.
Yayinda Alhaji Abdu Tababa kuwa yace.
“Lallai kawar dashi daga doron k’asa shine hanya mafi a’ala, Idan ba haka ba kuwa duk sai ya fito damu waje cikin rana daga gidajenmu.”
“Hakan bazaiyi wuba kuwa.”
Alhaji Idi Sale’n ya fad’a yana me mikewa tsaye.
Yayinda acan gidan su Rayyern kuwa, har yanzu su Abba basu matsa daga gun tv’n ba.
Sunanan zaune kowannensu dauke da farincikin, irin nasaran da Rayyern din ke samu.
Haka ma agidan Barrister Kabir har yanzu shima yana zaune agaban tv’nsa.
Dai-dai lokacin da ake cigaba da haska shirinne kuma, Aunty Dijat ta fito daga daki.
Zama tayi akusa da mijinnata tare da soma kokarin had’a masa coffee.
Kallon ta Barrister Kabir din yayi, kana cikin tausasa murya yace.
“Dijat kalli tv kiga, Jannart da matashin saurayin nan dake zaune agefenta”.
Da sauri ta miƙa mishi cup ɗin tare da zubawa tv ido tare da cewa.
“Masha Allah”.
Kurban coffee'n yayi tare da cewa.
“Sundace ko?.”
Ware ido Aunty Dijat din tayi ta kalli tv’n, dai-dai lokacin kuwa aka sake matso da fuskokin Jannart dana Rayyern din kusa.
“Masha Allah, ai kuwa Abban Hafeez matukar dacewa ma sukayi, kyau da kyau kenan.”
Murmushi Barrister Kabir din yayi, tare da gyara zamansa a takaice yace.
“Shine mijin dana zab’a mata, kuma shine wanda zata aura amma batare da ta sani ba.”
Ya fad’a yana me karb’an coffee din da aka had’asa masa.
Idanu Aunty Dijat ta d’an zaro waje, cike da tsananin mamaki hadi da zallar farinciki tace.
“Allahu Akhbar, Lallai girman Allah iko da buwayarsa tana da yawa, Masha Allah Lallai Jannart ta dace da hazik’in Namiji kuma jarumi, mai dauke da nagarta, Tabbas ka cika Uba nagari, ai kuwa zamusha biki yaushe ne Auren?”
Murmushi Abban yayi, tare da girgiza mata Kai, Ahankali kuma yace.
“A’a bayanzu zan gaya miki ba, abun namu sirrine.”
*GARKUWAR taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*
Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.
Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.
Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.
GARKUWAR MA'AURATA
By
*GARKUWAR FULANI*
11/15/21, 7:21 PM - Auntyna: Murmushin Jin dadi Aunty Dijat din tayi, kana cikin sakin fuska tace.
“Alhamdulillah nidai ko yaushene ma ina jira.”
Barrister Kabir dinma murmushi yayi, batare kuma daya sake cewa komai ba, ya cigaba da shan coffee d’insa.
Acan cikin tashar kuwa, zuwa yanzu kira na 15 kenan Jannart din ta amsa, wanda kuma daga kan kira na 15 dinne ta katse layin gaba d’aya, tare da d’agowa ta kalli cameras din dake jere agabansu.
“To masu kallonmu laifin dadi dai ance karewa, Domin naga lokaci yana daga mana hannu, saboda haka duka duka anan muka kawo k’arshen shirin namu Na Bak’on Mako, sai kuma wani sati Idan mai kowa mai komai ya kaimu, Insha Allah zamu sake zuwar muku da wani bak’on na musamman.”
Dan Juyowa tayi ta kalli Rayyern dake zaune, Cikin kuma sakin fuska kamar yanda ta sabayiwa kowa tace.
“Doctor ayiwa masu kallo da sauraronmu sallama.”
“Assalamu Alaikum.”
Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din ya fad’a atausashe, saboda yasan izuwa yanzu duk su Abbansa suna kallonsa.
Jannart kuwa juyowa tayi ta fuskanci Camera hadi da cewa.
“To masu kallonmu duka duka anan muka kawo k’arshen shirin namu, tare da babban bak’onmu”.
Ta ƙare mgnar da juyowa tana kallon Dr Rayyern.
Numfashi ya ɗan fesar tare da cewa.
“Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara”.
Gyara zamanta tayi tare da cewa.