Showing 75001 words to 78000 words out of 323952 words
arbain, duk motocin babu na banza, duk sai daukan ido suke kaman baa taba hawan titi dasu ba, har da escort da manyan securities saboda tsaro, kou kadan tasleem batayi kuka ba da aka fito daita daga dakinta, ana shiga dakin mom dinta ta daga idanuwa ta zuba cikin na mahaifiyarta kou kiftawa batayi, kawai irin kallon nan dake nufin you said you love me and you're taking to inda zaa kasheni kawai take mata, kawai sau hajiya zainab ta fara kuka tare da rungume yarta tana mata adua, tasleem kam kou gizau, vata kuma rungume ta ba, she's so cold and tender, tamkar babu any flesh jikinta haka ta ji jikin yarta, sai da aka fara yi mata fad'a sannan ta saki tasleem datayi mata tsaye kikam. Nan akayi waje daita zuwa wajen hajiya Asabe, wannan dai kallon na baku sona baku kaunata kawai take mata. Saga nan aka saka ta mota, yana kallon Mota zai tashi ta saki wani irin matsanacin ihu Mai daukan hankali, sai kalle take kaman tana neman hanyar kufcewa, duk cikin motar manyan mata ne babu yarinyar, duka daga aminan Mom dinta sai sister din mom dinta, tsawa wata tayi sai ta saduda tana nishi sosai, in ka ganta sai ta baka tausayi, Sai kalle kalle take, ganin hanyar fada aka nufa yasa ta samu Dan sauki, tun gate din farko zaka gane irin taron da ake a gidan yafi ba gidan alhaji mussadiq, koina cike da mutane, gate na uku aka bude masu, babu inda zaa shiga da mota saboda shimfida ne na alfarma koina mata na zazzaune, tasleem sai kalle kalle take ta cikin abinda aka lullube kanta dashi, babu abunda ake sai guda da kirari kala kala, kawai ita adu'ar ta Allah yasa nan ne destination dinta, tasan koma Meye zai zo mata da sauki, babu wasting of time aka fara shigowa da kayan gara kaman yanda alada ya tsara, manyan mata dake zaune Wanda duk family ne su aka dankawa amanar tasleem akayi budan Kai in a grand way, nan fa aka shiga da ita wajen hajiya Amina da dukda da tana cikin tarin mutane b'ata da gurin daya wuce ta saka tasleem a idonta, ana shigowa daita ta Mike tsaye itama tasleem kaman ba ita ba ta tafi da gudu ta fada jikinta nan ta fara kukan da ta dade batayi ba, kou voice dinta bai fita sosai balle taji abinda take cewa, sai da hajiya ta Kai kunne saitin bakinta taji tana cewa.
"ummah...dan Allah ...nan.... zan... zauna... " take maimaita mata cikin voice da bai fita, ummah ta matukar tausaya mata da har tayi dana sanin shuru datayi har alhaji ya hadasu, Don taga yanda tasleem ta koma kaman ba ita ba, she became more skinny than before, nan hajiya ta dinga rarrashinta tana shafa bayanta, babu mai jin abinda suke cewa, hakuri kawai ummah take b'ata gami da yi mata adua sanann tana tabbatar mata da she's in a good hand and yarima bai isa ya kou harareta ba. Ba karamin tashin hankali tasleem tayi ba yayin da zaa kaita gidanta, rike ummah tayi gam kaman itace mahaifiyar ta, har tsinkewa ummah necklace dake wuyanta tayi garin kiciniya, sai da taji ana cewa zaa zaneta sannan ta saki, har falo ummah ta rakata tana mata adua in a loud way that shows she's her love, su ummy kam suna gefe suna kallon komai, wato new wife In the family. Daman ta samu kwnaciyar hankali yanzu data tabbatar babu rashida da tasleem, da b'ata San inda zata da wannan abun kunya ba, kullum sai ta kira taji if rashida tana gida, in taji ance ta fita zuwa wajen da take service mussanman take aika driver dinta yaje ya bincika mata if da gaske tana chan kuma Achan din ake tardata, saidai rashida tayi murmushi duk sanda taga driver din ummy yazo tasan she's asking him to spy on her. To show how serious ummy is saida ta aika a tambayi Masu gadin gidan su tasleem if rashida is coming, da suka nuna basu San who is rashida ba sai da ta bada picture dinta aka nuna masu nan aka fad'a mata ta dade b'ata zo ba. Sai fa nan ta samu kwnaciyar hankali, ummy is a kind of person da batason abin kunya, if it is some greedy people hanyar samun Aliyu zatayi wa kanwarta Don su dangwali arziki tare dukda suma ba daga baya ba amma kou kadan b'ata da selfish attitude, she's a straight forward person.
Shi kam Aliyu tunda aka daura aure dayake a cikin fadan aka daura aure, ya samu ya dinga ratsawa ta cikin mutane, daman ya fadawa Mai yi mashi hidima wato umar ya samo keys daga din empty parts d babu kowa daga hannun sarkin gida, bayan ya samu yasa ya gyara wajen, tou ana gama daurin aure ya samu ya sulale zuwa wajen wannan part dake Bayan gida, nan ya fara cire the expensive cap dake kanshi sannan ya fara babban riga dake jikinki wanda yasha aikin hannu Mai tsadan gaske, yana cirewa yaji kaman an cire dutse daga jikinshi saboda nauyinsu, tsayuwa yayi ya rike waist dinshi looking so lost in thought, babu abinda yake tunani sai yau shi akayiwa aure, inda yau wata yarinya ce daban wacce bai san ta ba yasan zaije ya kwashi abinda ya dade yana nema amma sanin tasleem ce yasa kou wani abu baiji, one thing he knows for sure us tana da abunda za ta bashi, he knows how tender her skin is her how full her chest is amma shi Aliyu ya tunkari tasleem da wata bukata nashi is something he never think he will do, kawai he never dream kou sau daya ya nemi wani abu wajen tasleem, never.
Rigar dake ciki ya cire ya rage daga shi sai singlet fari tas tare da wandon kayan, ahankali ya zauna kan kujera ya cire expensive and elegant cap dake kanshi, nan ya kwanta tare dayin pillow da hannunshi, kou kadan bai wani rame ba sabida yasan no shaking, he's the king and the ruler and the faith of tasleem rest in his hands, at tines in ya zauna shi kadai ya tuna shi zai aureta sai ya saki dariya, yasan he won't beat her saboda kullum babu abinda hajiya take fad'a mashi sai.
"fav.. In har ka taba gimbiya ban yafe ba... Ban yarda ka doketa kou ka sa gidanka ya zama wajen tashin hankali gareta ba...duk hakkin miji dake kan mata ka b'ata... wallahi daidai da sau daya ka shiga hakkinta ban yafe ba... Nasan tasleem bazata kalleka tayi maka rashin kunya ba... Don haka you won't have any reason to give Don haka wallahi ka kula daita... Pls na baka tasleem try and eradicate duk wani tsoronka da take ji... Make her feel at home Dan Allah... Am begging... " wanann shine maganar da mom dinshi take fada mashi, Don haka yasan kou giya yasha bai isa ya taba tasleem ba amma kuma he won't fold his arms and look at her,
"there's many ways to kill a rat... " ya fad'a yana lumshe idanuwa tare da sakin kasaitaccen murmushi, tunawa yayi da wayarshi na a kunne, da sauri ya dauki wayar ya kashe Don kar a fara nemanshi Don yasan da akwai friends da yawa, babu abinda suke jira sai a watse daga wajen daurin aure su shashe, aikam sai suka ga wayam sannan layinshi bai shiga. Babu abinda suke cewa sai wannan auren dai baiyi ba. Mahboob ne yace.
"kawai Allah ya basu zaman lafiya shine the most important thing ba wai worldly lavish dinmu ba... " ya amsa masu. Kou sallah magrub nan dakin yayishi, ya fadawa Umar kar ya sake ya fadawa kowa yana gidan. Don haka in aka ganshi aka tambayeshi ina uban gidanshi sai yace shi bai sani ba.
A gidan tasleem kam wajen karfe takwas aka watse aka barta ita kadai sai masu aiki har uku, biyu daga wajen mom dinta sai kuma daya daga wajen ummah, cikin Wanda aka dauko mata daga gidansu kam har da Hindu wacce suke age mate da tasleem Kuma sun shaku sosai, Hindu ce ta dinga rarrashinta, daman a aladarsu baayin walima tunda anyi budan Kai, so she's fully a house wife now, babu sauran shagali, yanzu saidai tayi visitors kou kuma ita tayi visiting. wayarta ta dauka ta kira mum dinta tana rokonta tazo ta dauketa daga wannan gidan,
"babyna kiyi sallah...sai ki fadamin abinda kikeso.. Sai su Hindu su samo maki..." ta fad'a knowing da wuya Aliyu yace zai kawo mata wani abu sannan tasan da wuya ita kanta tasleem din taci wani abun
"mummy... Ni ban so... Gida nakeso..." ta fad'a tana kuka sosai amma voice dinta bai fita.
"do as I tell you... " ta fad'a mashi atakaice, nan ta kashe wayar. Da kyar ta samu ta Mike tana kuka ta shiga bathroom, kou kadan b'ata damu ta kalli environment dinta da uban dukiyar da aka zuba mata ba, kawai ita a maidata gida. Bayan kaman minti goma ta fito tana dafa bango, b'ata San inda zata fuskanta tayi sallah vba, haka yasa ta sake kiran mum dinta, nan mum dinta ta kira mahboob ya bincika mata sannan ta kira tasleem ta fad'a mata, nan tayi sallah ta kashe wayarta ta kwanta nan kan carpet, wayarta ne a fara ringing taga rashida, picking tayi ta dora a kunnenta daga nan inda take kwance,
"babe albishirinki .." ta fad'a mata, idanuwa tasleem ta lumshe tace
"Meye... " ta fad'a voice dinta chan ciki
"zan dawo gobe.. " rashida ta fad'a sounding very real,
"dan Allah da gaske kike?.. " tasleem ta fad'a mata
"eh wallahi... Am coming back tomorrow... Nayi missing dinki... " inji rashida,
"me too... " tasleem ta amsa mata,
"my besty kar ki damu da wani abu..tunda na dawo yanzu komai zanzo in dinka tayaki... I will pay for the time am not around ..." ta fad'a mata sounding so concrete,
"hmmm ni kam yanzu me zakiyi min.... Am gone already... " ta fad'a tana fashewa da kuka in a low voice,
"pls besty enough of this tears... Just wait and see how things go.. Nasan babu abinda zai faru sai alkhairi... Sannan I will be there to help you all through the way... Zan tayaki girki... Zan tayaki gyara gida... Zan tayaki gyara Bangaren shi... Har wankinshi in dai zaice kiyi just call me... "rashida ta fad'a sounding very very happy
"ai da akwai masu aiki... " inji tasleem,
"na sani kou da Mai aiki da akwai a abubuwan da ya kamata ke kiyi da kanki... Like dafa mashi abinci da kuma kula da Bangaren shi... Kinga da rana in bai nan sai in zo muyi komai.. Pls kar ki damu kanki..." rashida ta fad'a sounding very calm, tasleem dai shuru tayi Don tasan bazai Kai GA tati mashi girki kou ta gyara Bangaren shi ba, haka suka dinga hira rashida na confusing tasleem da fake love tana. Fad'a mata kabali da baadi ita Kuma tasleem is all attentive, the last thing data fad'a mata is
"in yazo ya neman wani abu wajenki kar ki yarda Kinji..." shuru tasleem tayi for moment tana tunanin abunda tace,
"kinji...pls kar ki yarda... Ki ja mashi aji yanda ya ja maki....kuma Kinga ba mutunci gareshi ba... So kema ki rama..." ta fad'a mata cikin kishi, kawai she want yarima kuma in ta san wani abu ya shiga tsakanin ta da yarima tana iya mutuwa saboda bakinciki, tasleem still shuru tayi, babu abunda ke dawo mata sai training da ta sha wajen Dr aysha, she never give time to Think about it,
"Kinyi shuru... Kou zaki bashi hadin Kai ne bayan duk abubuwan da yayi maki?.. " rashida ta sake tambayar ta sounding very angry,
"ni aa... "inji tasleem out of words
"ban gane ke aa ba... Zaki bashi kenan... Babu Dan Jan ajin bayan yanda kika ce ya mareki ya zalunce ki... " rashida ta fad'a voice dinta na rawa
"nasan... Babu... Abinda zai faru ai...ni ki bar min wannan maganar pls... " ta fad'a mata cikin low voice,
"ai besty you can't tell... Namiji ne shi.. Ba kunya garesu ba... Kina iya ganin bayan komai ya shigo maki...kawai don't accept.. If possible ki kulle kofarki...dan Allah on no account zaki yarda dashi.... Kina jina kou.... " ta fad'a sounding a bit commanding ( I know some people will be like how is this possible... Well it's possible, da akwai wayanda friends ke manipulating dinsu into misbehaving. Ni nan ganau ce, da akwai yarinyar da har da degree dinta amma duk abinda kawayenta sukace tayiwa saurayinta shi takeyi, at times zata basu wayarta su kirashi suyi mashi shegantaka main while in real sense suna son wannan Saurayin because his already made guy so wasu abubuwan are happening, in har zan rubuta abu then believe me da akwia gaskiya ciki, I don't write only for fantasy but facts)
"bai shigowa... " tasleem ta amsa mata cikin sanyin murya
"ya akayi kika sani... Nidai kiyi min alkwarin you won't give your self so cheaply... "
"promise... Balle nasan Bazan fara ba... " ta fad'a mata sai lokacin sukayi Sallama. Ajiye waya tasleem tayi thinking qbout abinda rashida tace kou kadan vata GA anything wrong with her advice ba, asalima gani take ciki so da kauna ne.
Shi kam yarima wajen karfe 8 ya leka waje ya kira Umar, kudi ya dauko wnada shi kanshi bai saj nawa bane yace
" kaje cikin gari ka sayi Nama da fruits da drinks ka Kai chan gidan... " ya fad'a yana lumshe idanuwa alaman he want to sleep, amsan kudin Umar yayi sai yayi shuru kuma yayi tsaye bai motsa ba, juyawa yarima yayi ya kalleshi
"go now... " ya fad'a mashi, Dan sadda Kai kasa yayi alaman respect amma sai yayi tsaye, kugu yarima ya rike yana kallon ikon Allah,
"toufa... Ya zaayi in aikeka kayimin tsaye kaman gunki... Kou you have suddenly become deaf... " ya fad'a sounding very angry, cikin natsuwa Umar yace
"ranka shi dade... Kayi hakuri.... Bani ya kamata in kaiwa matarka abinci ba... " bai k'arasa ba yarima yace
"what the fuck... So Umar kana questioning authority dina?.. Ni zan saka aiki ka tsaya kana min magana?.. Lallai ka samu waje... I don't blame you... " da sauri Umar ya durkusa cikin girmamawa yana cewa
"ranka shi dade... Meye amfanina a gareka in har Bazan baka shawara ba... Nasan ka Sake Dani..." yarima bai Bari ya karasa ba yace
"Wanda hakan yasa zaka rainani ba... Ai baka da laifi Sam... Duk laifina ne... " ya fad'a sounding very very angry,
"Allah ya huci yariman da babu kaman shi a wanann masaurata... Kayi hakuri in abinda nayi ya b'ata maka rai... Amma ij fulani tasan Ni ka aika zuwa Kai mata abinci hakan zai b'ata mata rai... Sannan a addinace ma bai kamata ba..."
"bullshit...you're speaking rubbish... Baka da ikon da zakayi meddling da private life dina...the only reason dayasa na baka kudi ka sayo masu abinci is because amana aka bani... If not bani da hadi da ita.."
"kayi hakuri ranka shi dade... Mahakurci mawadaci... " Umar ya fad'a mashi daga inda yake durkushe. Shuru Aliyu yayi for a moment yana shafa goshinta looking so confused, cikin fushi ya taka zuwa inda umar ke durkushe yace
"tunda bazaka bani kudina... " ya fad'a yana kwace kudin daga hannunshi. Shi dai Umar baiyi niyyar zuwa VA kuma bazashi ba, cikin fushi yarima ya saka hannu cikin aljihunshi ya fiddo keys ya Kama hanyar waje yana cewa
"ba dai ni kayiwa hakan ba... Sai dai ka nemi wani uban gidan... " ya fad'a yana wuce Umar dake durkushe cikin serious temper.
Thanks.[3/14, 6:28 AM] +234 703 008 7807: 25🧡❤💜💙💚
Sak'aci
🧡💛❤💜💚💙
®Zuwairat (ummumaryam)
2⃣5⃣
Yanda yake tafiya kasan cikin fushi yake, sai sussuna Kai kasa yake kaman mara gaskiya wai Don kar a ganshi, har lokacin gidan cike yake da mutane Don mutane sunzo from different states and even country kasancewan babanshi is among the powerful ruler in the north. Kaman daga sama yaji ance.
"wai Kai meke damunk.... " da sauri ya daga manyan idanuwanshi, ciroma ya gani ya nufoshi, tsaye yayi bai sake yunkurin sake taking another step ba,
"babu inda baa nemeka ba yau... Ashe kana gidan nan... Wato dai wannan shegen taurin kan nan naka ba dainawa zakayi ba kenan... "
"yaya... Ni yanzu na... Shigo... " ya fad'a kanshi kasa
"if yanzu ka shigo what happened to your phone.... Ummah tasa a nemoka yafi sau goma... Like wise shima abba That want to introduce you to some people... Wallahi duk wanann haukan da kake karshe kaine zakaji kunya... Now kaje wajen abba.... Daga nan kuma ka dawo wajen ummah..sauran kuma inji tana cigiyar ka" yayi commanding dinshi, babu word guda yarima ya Kama hanyar main fada, tun a door step yaga mutane cike, bai wani tsaya wasting time ba ya fice, bai tsaya koina ba sai a chambers din ummanshi, nan ma da akwai mutane, yana lekawa wata kanwar Mamanshi da ake kira da uwani tace
"aa aaf. .ga angon da ake ta nema kou ina... " da sauri Aliyu ya maida kanshi zai fita tace
"Kai dawo nan... AI babu inda bamu nemeka ba amma bamu ganka ba.... Maza shigo dare na sake yi... " yaji ana fad'a mashi, ajiyan zuciya ya saki tare da busar da numfashi sannan ya shiga dakin, duk yawancin su family ne, sai
"ango.. Ango... " suke kiranshi, cikin ranshi yana tunanin kou basu san shi bai son wannan auren ba oho, cikin mutane ya ratsa heading to her bedroom, nan MA da akwai mutane sun Kai goma, yana shiga wata ta fad'a guda sosai tana mashi kirari, ummah kam tamke face tayi, suna hada ido da ita ya sauke Kai kasa kaman mara gaskiya, ummah vata k'ara kallon inda yake ba waje ya samu ya zauna Dan nesa daita, tunda ya zauna kou inda yake b'ata damu ta kalla ba har sai sanda Wasu daga cikin wayanda ke bed room din suka fita sannan ta maido kallonta gareshi, face dinta sam babu walwala, da ka ganta kasan