Showing 177001 words to 180000 words out of 303099 words
ganin auren nan ya fasu wllh, wato shi sa yarinyar ke ganin kowa banxa, ita a dole xata auri yaron Bulasawa to taga samu ta ga rashi tunda har labari ya xo kunne na kuwa" Umma tace "Wllh da kin gama min komai a duniya idan har muka hadu muka tarwatsa lamarin nan, Kinga wahalar da na sha gun uwar yarinyar nan wllh kwakwalwarki baxai dauka ba, ta dalilin uwarta aka min kishiya, aka kuma sakeni...." Nan umma ta fara giggila ma Safeenah karya da gaskiyar abinda ya hadata da Ammi, tana kai wa aya, Safeenah ta gyada kai tace "Ki kwantar da hankalin ki Umma, ai tunda har labari ya xo kunnena an gama komai, dama kwata kwata na tsani yarinyar tun daga ranan da na fara daura ido kanta, ki manta da ko wani shiri da kike a da ki sa min ido" Umma tace "Atoh, shkkn.. Amma fa baxan mance shirin da nake ba, don kunya ba kadan ba nake son Uwar yarinyar ta kwasa a hannu, yanxu dai ki shirya anjima kije ganin kayan kada a dago komai a rai" Safeenah tace "A'a rashin xuwan kawai ya fi, ban gani ba balle raina ya kara 6aci" sai kusan yamma umma ta bar gidan ko digon ruwa bata sha ba, amma ko a jikinta. Yau tun safe Mujaheed ke xaune garden din gidansa har wajen sha biyu na safe, Safeenah ce ta shigo garden din cikin shiga ta alfarma tana taunar cingam tana kallonsa tace "Doctor d'an baccin weekend din ma gaba daya baka yi ba yau, ni dai yanxu fita xan yi, xan je can gida daga nan kuma in tafi gidan ku in gaida su umma" Daga kai yyi ya kalleta calmly yace "Baxa ki ba" Safeenah ta gwalo ido tace "Baxan je ba kuma, mahaifiyata da taka xan je gaidawa fa" ya mike a d'an tsawace yace "Nace baxa ki fita gidan nan ba Safeenah..." Daga haka ya wuce ya bar ta wajen tsaye, ta ja tsaki tace "Don kana fama da miskilancin ka kwana biyu sai ka sauke kai na, Toh wllh sai na fita" Kiran Umma tayi da wayarta ba a dau lkci ba Umma ta daga, ko gaisuwa babu Safeenah tace "Toh gashi dai ya ki bari na in fita wllh kuma yau ya kamata mu yi abinda ya kamata, kusan sati daya kenan Mujaheed magana da kyar yake min a gidan nan, ni ban damu ba don dama haka yake wani lkcn amma na wannan karan yyi yawa, tun asuba yake xaune garden yau wllh kamar maraya, during weekdays kuwa dama sai nayi bacci yake shigowa ya fice kuma da sassafe washegari, kwata kwata na rasa gane kansa ban san me ke damun sa ba, ni duk wannan ba wani damuna yyi ba don a sauki na, amma yanxu gaskiya ki kirasa ki masa magana don idan har ban fito ba yau shirye shiryen mu ya ruguje ne kawai" Umma tace "Kyaleni da shi kawai, mu ma nan ai ya fi satin bai xo ba, Ina ga halinsa na da ne ke kokarin dawowa" daga haka umma ta katse wayar, Safeenah ta tabe baki ta wuce cikin gidan, tana ta xaune parlor har bayan minti talatin ganin bai sakko ba ta mike ta wuce sama, ya fito wanka kenan ta shiga dakin, yana mata wani kallo yace "Kin xata kiran da kika sa mahaifiyata tayi min xai sa ko fita gidan nan ne yau??" Ta nufesa tace "Wai me ke damun ka two days ne Mujaheed, dubi fa you look so pale, and ni dai nasan lafiyar ka qlau" Ko kallonta bai yi ba ya bude press dinsa ta rungume sa ta baya tana shafa chest dinsa cike da shagwaba tace "Ni dai wllh ka gaya min meye damuwarka mijina" Bata jira cewarsa ba ta juyo da shi ta rungume sa gam tana shige masa and she really turn him on....
*Imaan isn't for free* it's 300 via
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788
63......
Safeenah na gama shirinta ta daura dankwali ya xauna dass a kanta ta feshe jikinta da turare, ta juya ta kalli Mujaheed dake kwance idonsa rufe, karasawa kusa da shi tayi ta xauna gefensa tana ta6a dogon hancinsa ta kai bakinta fuskarsa a hankali tace "Dear ni xan wuce fa" Bude ido yyi calmly yace "I said you are going no where Safeenah" ta xaro ido tana kallonsa da mamaki don duk tunaninta ya hakura, can ta marairaice tace "Haba dear, wllh fa ba dadewa..." Ya katse ta ya mike xaune fuska daure yace "Nace baxa ki fita ba, am telling you this wllh idan kika fita gidan nan yau xaki san wanene Mujaheed" Yana fadin haka ya mike ya shige bathroom, tagumi tayi xuciyarta na tafarfasa ta bi sa da ido, can ta mike ta fice daga dakin rai bace ta kira Umma tace "Toh wllh ya ki bari na in fita Hajiya, taurin kan Mujaheed har tsoro yake bani" da mamaki Umma tace "Ya ki barin ki kifito kuma??? To ina Ina xuwa..." daga haka Umma ta katse wayar, Ba a dau lkci ba ta sake kiranta tace "Toh ai wayar tasa a kashe yake" Safeenah tace "To ya kashe kenan..." Safeenah ta tabe baki, Umma tace "Toh ki kai masa wayar ta ki" Safeenah tace "A'a ni kam baxan iya kai masa ba, don he is very serious, ki bari dai in ta lallabasa anjima xan kira ki" daga haka ta katse wayar. Imaan na xaune dakinta sun gama waya da Sadeeq kenan ta shimfida darduma ta dau Al-quran dinta ta ajiye a kai ta xauna kan darduman ta tankwashe kafa ta bude qur'anin, ba karamin missing din islamiyya take ba yanxu, ji take da ma bata yi saukan ba, Bude kofar dakin aka yi Ammi ta shigo, Imaan ta daga kai tana kallonta, Ammi ta xauna gefen gadon tace "Karatun kike ko kin gama" Imaan tace "A'a ban fara ba" Ammi tace "Kin ma ci abinci kuwa" Imaan tace "Ehh na ci" Ammi tace "Ohk, kina ji na Imaan?" Imaan na kallon mahaifiyar tata tace "Ehh ina ji Ammi" Ammi tace "Pls Ina son ki dage da azkar sosai kuma a ko da yaushe, make that a part of you, kuma da daddare xan dinga shigowa ina tashinki kiyi sallah...." Da mamaki Imaan tace "Ammi me yasa" Ammi ta buda ido sosai tace "Me yasa, dama sai da dalili mutum xai rike addu'a da tsayuwar dare, ae yanxu ne kika lalace baki yi, amma da ai kina yi sosai" Murmushi Imaan tayi bata ce komai ba tana bude kur'anin gabanta a hankali, Ammi tace "Ga kuma jarabawar ku ya kusa shima sai ki dage da addu'an samun nasara kin ji" Imaan tace "In sha Allah Ammi" Ammi tace "Good" daga haka ta mike ta fita dakin, imaan ta fara karatun Qur'anin gabanta cikin cool voice dinta. Da magrib ta tafi kai ma Inna abincin Inna ta ki barinta ta tafi ta dinga sauke akwatuna tana bude mata tana cewa "Sai kace ba kayan ki ba yau kusan kwanan su biyar kin ki ganin abinda ke ciki, ni dai ba ruwana, karere ma da abun bai shafesu ba duk suna ta xuwa gani balle ke" xauna ni dai ki duba, su Ahmadu da Bukar ma duk sai da na fiddo masu suka gani filla filla, Imaan dai ta d'an yi murmushi ta xauna tana kallon kayan da Inna ke fiddowa amma bata ta6a ba, Inna tace "Ni dai naga abinda ya isheni, to ki daga mana ki dudduba ke fa babu abinda ya hadaki da fulanawa, ubanki bahaushe ne gaba da baya, uwar ki ce bafillatana sai uwarsu Mujaheed, ban san me yasa suka nace sai fulani ba, nima dai ubana bafillatani ne amma uwata bahaushiya ce, mijina kuma bahaushe" Imaan ta turo baki ta dinga daga kayan tana kallo, Inna tace "Wannan ai jaraba ne ke da kayan ki baxa ki duba ba, ga gwal din can na hada da dankunnen da ya ta6a baki, bari in dauko ki gani" Daga haka ta shige daki, Imaan na ganin haka ta mike cikin sanda ta nufi kofa ta fice parlon da gudu ta sa takalminta tayi gaba, a hanya ta kusa cin karo da Mujaheed, ta xaro ido ta juya masa baya da sauri xata bar wajen ya kamo hannunta ya juyo da ita, kin yarda su hada ido tayi tace "Ina yini" ya dawo da ita jikin bango ya dago kanta yana kallon kwayar idonta, kallonsa ita ma take, lkci daya ta sauke idonta kasa a hankali, Murya can kasa yace "Me yasa kike gudu idan kin gan ni Imaan" ta turo baki tace "Ni fa ba komai yaya" ya kamo hannunta yace "A'a ki gaya min pls, me yasa kike gudu" kasa cewa komai tayi, yace "Imaan" da sauri ta kallesa jin yanda ya kirata, yace "Talk to me plss" Boye fuskarta tayi tace "Ni bana son ka min fada shi sa nake gudu" yace "Fadan me?" Kin cewa komai tayi ta sunkuyar da kai tana murmushi, ya kara kiran sunanta, kamar xata yi kuka tace "Abinda nayi mana" Bai iya yace komai ba sai kallonta yake, Jin shirun yyi yawa ta daga kai ta kallesa suka hada ido, ta wara masa idonta tace "Amma dai baka da lafiya ne Yaya" Ya sauke idonsa kasa yace "Probably" cike da damuwa tace "What's wrong with you yaya?" Da kamar baxai ce komai ba sai kuma a hankali yace "Akwai wani abinda ke shirin faruwa that will cause me lot of harms a rayuwata, and sure that will be the end of my happiness..." Da damuwa sosai tace "Subhanallah, what's that Yaya? Meye shi ka gaya min" jingina yyi da bango bai iya yace mata komai ba, ta dawo tana facing dinsa ta kamo hannunsa kamar xata yi kuka tace "Yaya don Allah ka gaya min meye shi, meye xai faru and how are you to prevent it from happening" Taku da suka ji toward direction dinsu yasa tayi saurin sake masa hannu bayan sun yi ido hudu da Abba dake tahowa xai tafi part din Inna hannunsa rike da leda, Mujaheed ya ja baya da sauri, ita ma hakan tayi, tunda Abba ya kallesu sau daya ya dauke kai, sai da ya isa daidai su.. Mujaheed ya sunkuyar da kai cike da karfin hali yace "Sannu da dawowa Abba" Abba yace "Yauwa Muhammad ya family" Imaan ta sunkuyar da kai ita ma tace "Ina yini Abba" Abba ya amsa sannan ya wuce xuwa part din Inna. Imaan ta kalli Mujaheed tace "Yaya mu je plss ka gaya min" Bata jira cewarsa ba ta kama hannunsa ta xaga baya da shi, ta xauna kan wani dakali tana nuna masa gefenta tace "Oya xauna" murmushin karfin hali yyi ya xauna, ya jinginar da kansa da nata yana kallonta ta gefen ido, tace "Toh ina ji, tell me what's it kuma ka gaya ma su Abba kuwa??" Mujaheed ya jawota jikinsa murya can kasa yace "No I didn't, and it's too late" kallonsa kawai Imaan take, kafin tace komai yace "Kin ga kayan ki da aka kawo?" Rufe fuskarta tayi da sauri a shoulder dinsa tace "Ni baxan iya ba" ya lumshe ido ya bude, a hankali yace "Yanxu dai aure kike son yi ki tafi ki bar ni koh?" Ta xaro ido tace "Toh ae kai ma kayi auren ka tafi ka bar ni" yace "Ance maki ina son auren nawa ne?" Yar dariya Imaan tayi tace "Ehh baka sonta but you are enjoying ur marriage, kuma tana haifa maka beautiful baby like her xaka fara sonta sosai" kallonta yake ko kiftawa babu, cikin sanyin murya yace "Why did u say I am enjoying my marriage imaan, how did you know??" Tana murmushi tace "Ae na gani..." da sauri yace "Kika ga me??" Taki yarda ta kallesa tace "Abinda na gani" Bai san lkcn da ya rungume ta ba yace "Noo imaan, I can neva enjoy my marriage with Safeenah, am only trying my best in fita hakkinta, ni kadai nasan abinda nake ciki imaan, bana son Safeenah, warce nake so na kokarin kubuce min which I won't allow in sha Allah" Imaan tace "Wai Aunty Farida, she told me her wedding is next week ai, xan ma je tare da Maimoon" Ya runtse ido yace "I have never loved farida, tausayinta kawai nake, kuma burina a da in hada ta su xauna da wacce aka halitto ni domin ta, sbda lalurorinta, ita ce macen da nake ma son da ni kaina ban san irinsa ba Imaan" da surprise imaan ke kallonsa jin yace baya son Farida, a hankali tace "Who is this lady Yaya? Ni ban santa ba, you've never tell me anything about her, ita ma a kd take?" lkci daya idanuwansa suka kada sosai, cikin sanyin murya yace "Na fara mata so na yan uwantaka, sannan na kasance mai tausayinta matuka, ni kaina ban ta6a tunanin soyayyar da nake mata xai rikide ya koma so na aure ba, tun bata san kanta ba nake sonta nake mata hidima, na kuma koya mata sa6o da ni...." Imaan dake ta kallonsa ta xaro ido kamar xa su fito tace "Kamar dai yanda muka sa6a ko, To wacece kuma a Ina take yaya?" Mujaheed ya dinga kallonta, Ta turo baki tace "Ni dai ka gaya min, kuma tasan kana sonta kuwa?" Ya girgixa kai a hankali yace "Taki ganewa har yanxu" Imaan tayi murmushi hade da tagumi tace "Toh nawa xaka biya ni sai ka hada ni da ita in fallasa mata sirrin dake xuciyarka, Yayana kasan fa you are very handsome..." Sai kuma ta fashe da dariya ta boye fuskarta a jikinsa tace "Wllh kana da kyau, and you are a gentle man, tall, huge, your beards are cute, so babu macen da xata iya resisting love din ka stop being afraid xaka rasa ta, kila da gudu ma xata amince maka idan ka sanar mata, wa ya sani ma ko ita ma tana sonka, it's bcos of ur handsomeness and ur personality wannan rubabbiyar matar taka ke rawan kai a kanka, take ma mutane walakanci, wllh sonka take kamar ta mutu, bata san you are only managing and just enjoying...." Sai kuma ta yi shiru da sauri, Bai san lkcn da yyi wani murmushi ba har sannan yana kallonta ya dago kanta taki yarda su hada ido yace "Enjoying what?" A rikice tace "A'a ba haka xance ba fa...." Ya lumshe ido yana shakan kamshin gashinta daga cikin hijab din jikinta murya can kasa yace "I will enjoy soon with my lil sis, amma ba da Safeenah ba...." imaan ta bude ido da sauri ta kallesa tace "Wacece?" Ya bude ido shi ma yace "Ita warce nake so mana" imaan tace "Toh are you paying me to help you out?" Yace "Ko nawa kike so kuwa, amma before then sai kinyi kokarin sa su Abba a dakatar da maganar kawo sadakin ki next week" da mamaki tace "Why? My being betrothed won't stop me from helping u out yayana" Ya girgixa kai cikin sanyin murya yace "Shine babban abinda xai sa ki kasa taimakona Imaan" Ta xaro ido tace "Yaya kai fa ka riga kayi auren ka, to ni baka son nayi auren?" Ya kalleta yace "Auren dai kike son kiyi ki bar ni" dariya tayi sosai tace "Kai ma ai ka yi" yace "Amma ai ina xuwa ganin ki kullum" tace "A'a ni dai ba wajena kake xuwa ba, wajen Inna kake xuwa" yana kallon kwayar idonta a hankali yace "Wllh duk ranan da na xo gida ban ganki ba bana iya bacci da daddare" Da mamaki Imaan ke kallonsa tace "Saboda me?" Ya sauke idonsa bai ce komai ba, tayi murmushi tace "Kaga da matarka na sona sai in koma gidan ka in yi waec a can" ya kalleta da sauri yace "A'a ba ruwanki da ita ki dawo kiyi waec din ki kawai" ta make kafada tace "Bana so, Ni fa da gaske Yaya bana son matar nan taka, I so dislike her" Yyi shiru bai ce komai ba, can tace "Yaya na fara jin yunwa fa, xaka bani lambar yarinyar ne yanxu in kirata mu yi magana?" Ya girgixa kai yace "A'a sai dai in kai ki wajenta" tace "When?" Yace "Ko xuwa gobe" tace "Toh Allah ya kai mu" da sauri ta daga kafarta tana kakkabe hijab dinta tace "Wllh Yaya sauro a nan" Mujaheed ya kunna fitilar wayarsa yana haska kafar yace "Sorry dear" yayi stretching legs dinsa ya daura nata a kai bayan ya daga hijab din yana duba inda sauron ya cije ta, shafa smooth leg din nata ya shiga yi yana kallonta, ta xaro ido ta buge hannunsa tace "Aa ni bana so Yaya" a hankali yace "Why?" Ta turo baki tace "Uhn ni bana so" tana fadin haka ta sauke kafarta kasa ta mike tace "Toh sai goben Yaya" ya mike yana kallonta yace "Mu tafi eatry tunda kina jin yunwa?" Ta juyo da sauri tace "Da gaske Yaya" yana murmushi yace "Sure, tafi ki jira ni gun mota a waje" tana murmushi tace "Toh" daga haka ta wuce ya bi ta da kallo har tayi nisa, ya lumshe ido ya bude, kamar mai tausayin kasa ya dinga tafiya har ya fita compound din ya sameta kusa da motarsa tana jiransa, yana bude motar ta shiga front seat, shi ma ya shiga maxaunin driver tana kallonsa tace "Yaya ni kaza nake son ci da drink kawai" yace "Ba sai mun je eatry ba knn" tace "A'a can xa mu je" suna isa wani eatry babba yayi ordering abinda tace, suna xaune wayarta a hannunsa tana kallon hotuna shi kuma sai kallonta yake, hotunan da suka yi tare ne kadai a camera dinsa, sauran duk WhatsApp images ne, hoton Safeenah ko kwaya daya babu a wayar tasa, Imaan ta daga kai suka hada ido, ta xaro ido tace "Why are u staring at