Showing 222001 words to 225000 words out of 303099 words
d'a na ya fi karfin sauran ciwo, ta ina xai fara rayuwar aure da ita ta talauta min shi da ciwonta" ranan dai Umma yanda taga rana a gantale haka ta ga dare, babban damuwarta da tashin hankalinta me xai faru idan gari ya waye, tasan da kyar idan Hajiyan Marafa baxa su taho gidan tare da duk yaranta su risketa ba, tasan Safeenah ta gama sanar masu duk abinda ya faru da yanda ta dinga kokarin hana auren Imaan da Sadeeq, Umma ta mike xaune ta rike kanta tana kiran Allah ya kawo mata dauki xuciyarta, ni kam nace lallai ma. A bangaren Ammi kuwa sllh ta dinga yi daren ranan don ita ma neman baccin tayi ta rasa rabonta da shiga tashin hankali haka har ta manta, da dadewa ta sha addu'ar kada Allah ya kaddaro masu rana irin ta yau tun daga lkcn da ta lura shakuwan Mujaheed da Imaan ya fara wuce hankali ya dauka, shi yasa ma ta dinga taka ma Imaan burki sai gashi lkci daya bbu notice abinda take gudu ya faru, da yau Yusuf aka hada da Imaan me xai dameta, sai ma ta fi kowa farin ciki da hadin amma Mujaheed kam ya fi karfin 'yar ta. Imaan na cikin duvet ita din ma ba bacci take ba sai juye juye kawai take, xuwa lkcn kukan ma ta kasa wani mugun xaxxabi take ji sosai, duk joints dinta ciwo suke mata ga headache da backache, tasowa Ammi tayi ta nufo ta bayan ta idar ganin juye juyen da take, ta cire duvet din jikinta tana kallonta kafin tace komai taji xafin da jikinta yyi ba kadan ba, Imaan ta mike xaune da kyar ta jigina da gado a hankali tace "Ammi bana jin dadi" Ammi tayi shiru tana kallonta, can ta mike ta wuce kitchen ta hado mata shayi sanin da daddare bata ci abincin kirki ba ta kwanta, ta dawo ta mika mata shayin tace "Ki sha in samo maki paracetamol yanxu" Imaan ta karbi cup din hannunta na rawa, Ammi ta fita xuwa dakin gwaggwo, sllh ta sameta take yi ita ma, ta bude gun da take ajiye magungunanta ta dau pain reliever da man xafi da ta gani ta fita, duk yanda Ammi tayi da Imaan ta sha shayin kin sha tayi wai amai take ji, hakan yasa ta bata paracetamol din ta shafa mata magani duk jikinta ta sa ta kwanta sannan ta lullube ta. Da safe Abba bai hakura da kiran layin Mujaheed dake kashe har sannan ba, lkci daya jikinsa yyi sanyi a nan kuma ya fara considering d'an nasa, to ko shi ma baya son auren ne, yasan dai ko Mujaheed baya so xurfin cikinsa ma baxae bari ya fada ba, shigowar Umma ya sa ya ajiye wayar hannunsa, Umma ta duka kan kneel dinta tana kallon Abba dake kallonta shi ma, Cikin rawar murya tace "Alhaji na xo neman alfarma ne a gun ka ba wai don na isa ba don ni din a ko da yaushe mai laifi ce na sani amma don Allah kar ka biye ta halina kayi ma girman Allah ka saurareni kuma ka min alfarmar da na xo nema" Abba na kallonta yace "Ina jin ki" tayi kasa da kai a sanyaye tace "Alhaji wannan auren da ku ka hada kayi ma girman Allah ka raba sa, na farko Aisha ba son auren take ba, ita Imaan din ma haka, shi kuma Mujaheed sbda tashin hankali kaga ba shi ba labarinsa, ban san inda ya shiga ba, don Allah ka yi min rai kayi abinda ya kamata a wannan batu..." Abba yace "i don't have any say on this matter any longer Rukayya, Sai abinda Inna ta ce, yanda tace haka xa ayi...." Umma ta fashe da kuka tana kallonsa tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wllh Alhaji Mujaheed dina baya son auren nan, tun jiya fa har yau wayarsa a kashe bamu san inda yake ba" Abba ya mike yace "Yana lafiya in sha Allah" mikewa Umma tayi tana shessheka ta fita tana tunanin meye mafita, don ita da Mujaheed yayi aure da Imaan fa gwara ko da bata mutu ba ta yarda ta rasa komai nata a duniya. Karfe tara Abba da Daddy suka isa gidan gwaggwo, Gwaggwo ta fito daki bayan mai aikinta ta kirata, da fara'a ta amsa gaisuwar su tana masu sannu da xuwa, Gwaggwo ta xauna saman kujera tace "Ya aka ji da taro da hidindimu??" duk suka amsa da Alhmdllh an gode Allah, Gwaggwo tace "Toh madallah Allah maku albarka, Allah kuma yasa abinda ya faru shine mafi alkawari gare mu gaba daya" Abba yace "Ameen, dama xuwa muka yi mu baki hakuri a bisa wannan hukunci da muka yanke baki da masaniya, abubuwan ne suka xo a haka gwaggwo, ayi mana afuwa...." Gwaggwo tace "A'a ba komai wllh Ahmad, ai duk an xama daya, wannan aure kuma da ku ka hada Allah yasa shine mafi alkhairi, Allah maku albarka, su kuma Allah ya basu xaman lafiya, kada ku biye shiriritan matan ku, abinda ya dace shi ku ka yi, anjima in sha Allahu ni da kai na xan maida Fatimar gida, idan Allah ya yarda" Abba yace "Toh Alhmdllh Allah ya kara girma gwaggwo, ita Hajiya Aishar fa??" Gwaggwo tace "Ta d'an fita siyo mata magunguna da yake jiya da xaxxabi ta kwana amma da sauki sosai yanxu, bacci ma take" Abba yace "Toh Allah ya sauwake, xa mu koma Gwaggwo, mun gode kwarai, Hajiyar ma tace a gaishe ki" Gwaggwo tace "Toh Ina amsawa, Allah ya maku albarka" duk suka amsa da Ameen suka mike, Daddy ma yyi mata sallama suka fita parlon, a bakin gate suka hadu da Ammi ta dawo pharmacy, kallo daya tayi masu ta dauke kai ta gaida Abba, Abba ya amsa yace "Ya mai jikin ta kara ji Aisha" Ammi tace "Alhmdllh da sauki" shi dai Daddy kallonta kawai yake, Abba yace "Toh Allah ya bata lafiya" Ameen ta mayar masa ta shige gate din gidan, murmushi Abba yyi ya bude front seat, daddy ya xaga ya shiga maxaunin driver suka bar anguwar, Abba yace "In sha Allahu xa su sakko gaba daya, kuma xa su fi kowa farin ciki da wannan aure nan gaba" Daddy bai ce komai ba har suka hau saman titi, sai kuma yace "How do we reach Muhd, I am disturb about him barrister" Abba dai bai ce komai ba don shi ma bai san inda xai samo Mujaheed ba balle su ji ta bakinsa a kan auren. Mota biyu Hajiyan Marafa suka yo da yaranta mata su uku, da yan uwanta biyu da kawayenta biyu sai Safeenah da har wani rama tayi sai yan idanuwa da suka kumbura suntum dan kuka, da ta tuna wai mijinta Mujaheed aka hada da Imaan sai ta fasa wani ihu kamar mahaukaciya har tsakar dare haka ta dinga masu kamar tababbiya, ta girgixa ne ba na wasa ba, gate mai gadi ya wangale masu a xatonsu masu xuwa biki ne, Hajiyan Marafa ce ta fara sakkowa motar sannan yaranta, kawayenta da Yan uwanta suma duk suka fito daga tasu motar ko wannen su fuska a murtuke, Rahma ce ta tafi dakin umma ta sanar ma ta xuwan su Hajiyan Marafa da suka ki shigowa ko da parlor ne wai a kira masu Hajiya Rukayya, Umma ta katse wayar da take da Hajiya Saude jikinta ya hau rawa tace "Kice masu bana nan, tun daxu na fita...." Rahma tace "Har fa da Hajiyar da kanta" cikin tsawa Umma tace "Ki fita kice masu bana nan nace, ko uban me xan masu da suka xo min nan, ko ce masu aka yi ni na daura ma Mujaheed aure???" Rahma ta fita dakin umma ta mike da sauri ta sa makulli hannunta na rawa, xaunawa tayi gefen gado xuciyarta na bugawa, Allah kadai yasan abubuwan da xa su fada yau, saukin abun ma Abba sun fita tun daxu da kaninsa, Aunty da Mama Hadiza dama suna can part din Inna tun safe, dialing Number Hajiya Saude ta kara yi ta sanar mata Hajiya Mansura ta xo tare da tawagarta a motoci, Hajiya Saude tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un... Toh yanxu ya ake ciki??" Umma na share xufar da ke keto mata tace "Tonon asiri nake tsoro Saude, nasan yar duk ta kwashe ta sanar masu yanda aka yi, Saude kar su fasa kwai a gidan nan in shiga uku dadin abun ma Alhaji bai nan, Amina da Hadiza kuma suna gun tsohuwar amma kinsan yanda Hajiyan Marafa ke magana, wllh dole su ji hayaniya su fito, ni dai nace Rahma tace bana nan" Hajiya Saude ta sauke ajiyar xuciya tace "Ni wai Rukayya tun farko me kika ga tattare da family din Hajiyan Marafa kika hada d'an ki da yar su??" Umma tace "Aa kawai don ace d'a na na auren yar masu kudi mana, sunan nake so dama, kuma ai haka ma mutane ke cewa" Hajiya Saude ta ja tsaki tace "Toh me kika karu da a kudin su?" Umma tace "A'a ki bari, wllh ynxu haka akwai wani sarka da dankunne xai yi miliyan daya da rabi haka Hajiyan Marafa ta bani kyauta kwanaki da naje, sannan ta dalilin auren nan matan governor kalilan ne ban sani ba, duk taronsu sai naje, manyan kasan nan yanxu daddaya ne ban gani ba ido da ido amma a mata, Kai har wasu maxan ma...." Xaro ido Umma tayi jin hayaniya a tsakar gida tace "Gasu can Saude, xa mu yi magana anjima" daga haka ta katse wayar ta tafi ta bude labule a hankali tana lekansu.... Hajiyan Marafa ce tsaye tana cewa "Duk inda Rukayya ta shiga yau sai ta fito wllh, in har na bar gidan nan to Rukayya ta fito ta fallasa kanta ne, 'ya ta xata yaudara a hada baki da ita a mata kishiya??? Toh wllh wllh yau sai ta san tayi da Hajiya Mansura, yanda ban xauna da kishiya ba haka diyata baxata xauna da kishiya ba, malamai da bokayen da take bi yau duk sai ta fito tayi bayani ta tona kanta ta fadi abinda tayi aka fasa auren yarinyar gidan nan har aka hada auren da mijin diyata...." Hajiya Baturiya yarinyar Hajiya Marafa ta fari cikin tsawa da daga murya tace "Ta fito da bakinta ta fadi abinda tayi aka fasa auren da aka lika ma mijin Yar uwata, ta fito nace idan ba haka ba yau wllh wllh sai mun tada gidan nan in ga shegen da ya tsaya ma mutan gidan....." Kawayen Hajiya marafa suka yi cikin parlor suna cewa "Ae duk inda ta shiga sai ta fito wllh, sai ta fallasa kanta anji mugun abinda take yi tun ba yau ba, yau xata ga karshen boka da malamai...." Mama Hadiza ce ta taho compound din da sauri jin hayaniya Aunty na biye da ita a baya, Umma dake jin su a daki ta daura hannu a ka ta dinga xagaye dakin hawaye na sakko mata tana salati tana fatan kada su Abba su shigo gidan, wani rashin tunanin ne ya kai ta hade kai da Safeenah har ta san sirrinta haka tasan abinda take ciki, tare fa suka dinga xuwa gun Malamin ashe abu xai juyo kansu yanxu ga Safeenah ta fallasa ta gun uwarta da bakinta ba shiru yake ba, ta xauna gefen gado ta fashe da kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, me ke faruwa haka ni Rukayya, Allah ka rufa min asiri kada 'yan gidan nan su jiyosu su fito, da na shiga uku yau kuwa" muryar Mama Hadiza da ta ji tana tambayar lafiya yasa ta mikewa da sauri tana xaro ido ta ji cikinta ya hautsine, Hajiya Baturiya tace "Kafff xuri'ar mu babu wanda ya taba xama da kishiya don haka baxa a fara kan kanwar mu Safeenah ba, karya ake Safeenah ta xauna da kishiya, Rukayya ta fito ta fadi abinda tayi gaban kowa yanxun nan..." Mama Hadiza tace "Tohhh, iko sai Allah ku kuma da abinda ku ka xo kenan??" Hajiya Shamsiyya ta iso wajen tana huci tace "Kwarai kuwa da abinda mu ka xo kenan, bokan da Rukayya ta biya ta sa ya wargaje auren yar gidan nan shi xata fito yanxun nan ta kai mu gunsa ya wargaje abinda yyi da har yasa tsautsayi ya fada kan 'yar mu, kin ganmu nan kaff bbu mai kishiya, kema kanki nasan baki sonta don haka Safeenah domin ita kadai aka yi mijinta baxata xauna da wata banxa wai kishiya ba...." Muryar Inna suka ji tana salati da karfi tana cewa "Naga abinda ya isheni ni patuu, wasu mahaukatan ne aka bude ma get suka shigo mana gida haka, anya ilu xai gama da duniya lafiya kuwa, banda haka ya xai bude ma lafta laftan mahaukata get su shigo mana gida suna hauka ba kakkautawa??? Ina Ahmadu da Bukar suke suga abinda shegen bakauyen da suka ajiye a bakin get yyi, ya tashi ya bude ma ta6a66u get salon su fara bin mu da duka muna gudu" Hajiya Marafa ta nufeta cike da raini tace "Hajiya mu ba mahaukata bane, amma mun fi mahaukata hauka idan aka ta6o mu, ba wani abu ya kawo mu ba Rukayya muka xo nema ta fito ta fadi abinda tayi aka fasa auren gidan nan wanda hakan yasa har aka ma diyata kishiya bata ji ba bata gani ba, wllh har gun bokan da ta je aka mata aiki duk sai ta kai mu yanxun nan gaba daya...." Inna ta xaro ido cike da masifa tace "Auzubillahi wacece wannan Kuma?? Waye kuma boka ni patuu?? Rukayyar ce ta san wani boka?? Toh tun da uwarta Hadiza ta haifeta bata san sa ba, kaji min gantalallu dai yan iska mahaukata, waye kuma 'yar ku? Safara'u ko wa? Wllh tunda ku ka ma Rukayya wannan gagarumin sharrin sai Mujaheed ya fito duk inda yake ya sake shegiyar yar ku, don baku da tsoron Allah uwarsa ku ka xo yi ma cin mutunci har gida?? To wllh sai Mujaheed ya saketa yau yau din nan, mu kaf danginmu bbu wanda yasan boka, kai ko ma ya sani Allah ya yafe masa, kaji min mutane dai yan wahala, wllh idan baku fitar mana gida ba sai na tafi caji ofis yanxun nan an xo an kwashe ku in ga uban da ya tsaya maku, Ina ruwan Rukayya da wani boka Allah na tuba, matar dake ta murna da hadin da Ahmadu da Bukar suka yi tun jiya, tun da nake Rukayya bata taba shigowa da sassafe gaisheni ba sai da aka hada auren nan, yanxu haka da kanta xata je dauko amaryar a gidan kakarta don can ta kwana... Kaji min mutane dai?? To wlh ku fita ku ban wuri kada in tsine maku" Daga Hajiyan Marafa har 'ya yanta da kawayenta sake baki suka yi suna kallon Inna, Inna ta juya ta fara wucewa a fusace tana cewa "Rukayya ai ta fi kowa murna da auren nan, dama tun farko ita ba son shegen d'an Bulasawan nan take ba, tun farko take ma Imaan kwadayin aure da Mujaheed mu ne dai ba mu yarda ba" Aunty ta saci kallon Mama Hadiza dake bin uwar tata da kallo, can duk suka bi bayanta, Safeenah ta fashe da matsanancin kuka mai ban tausayi ta durkushe wajen jikinta na rawa tace "Na shiga uku Mummy wllh ni baxan iya rabuwa da Mujaheed ba Ina sonsa, dama ashe duk yaudarata take da Mujaheed take son ayi auren nan?? Wayyo mummy ku taimakeni kada ya sakeni wllh ina son sa" Hajiyan Marafa ta dinga huci ta ma rasa abun cewa tana kallon Safeenah, sai da Inna tayi nisa ta kalli Mama Hadiza murya can kasa tace "Ba boka ba har gun masu tsafi Rukayya xuwa take wllh tllh"
*Imaan isn't for free* it's 300 via
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788
80....
Hajiya Mansura tayi wani murmushi tana kallon kawayenta tace "Rukayya ta debo ruwan dafa kanta, wato da sa hannunta da contribution dinta a yi ma 'ya ta kishiya.... To xata san da Hajiya Mansura take, xata san da sa hannunta ayi ma diyata kishiya, ita da d'an ta daga wnn lkcn sai dai hange daga nesa, kishiya kuma Safeenah baxata xauna da ita ba, kaf xuri'ar mu babu mai kishiya kuma baxa a fara a kanta ba, ku mu tafi kawai...." Hajiya Baturiya ta daga Safeenah dake rusa kuka kamar ranta xai fita tace "Babu abinda kukan nan xai amfane ki da, ki tashi mu tafi tun wuri a san abun yi, sai Hajiya Rukayya ta san da family din Alhaji Usman take...." Cikin kuka Safeenah tace "Mummy yar uwarsa mai min rashin kunya a gidana fa aka aura masa, wannan fitsararriyar ce fa mai min kallon banxa ce, Mummy ya xa ayi ta aurar min miji na shiga uku na lalace, da na sani da ban biye uwar Mujaheed ba, ashe yaudarata take da Mujaheed take son ayi auren, Mummy sai kinga yanda yake ji da yarinyar, Mummy ya xan yi da raina idan aka kawo min ita gida a matsayin kishiya, wayyoo Allah na..." A fusace Hajiyan Marafa ta buge bakinta tace "Uban wa xai kawo maki ita gida a kishiya?? ai wnn gidan naki ne ke kadai har duniya ta nade, sai dai idan ba tsatso na kika fito ba, Mujaheed naki ne ke kadai, hatta uwarsa Rukayya sai dai ta gansa daga nesa, wa ke ta wani amaryar ga babban shaidaniya annamimiya da xa mu fuskanta, in sha Allahu sai na toxarta Rukayya toxarci mai girma kuwa, sai tayi da ta sanin sani na..." Daga haka ta ja ta xuwa cikin mota tana huci, duk suka shige cikin mota suka bar gidan, Umma dake labe jikin window tana kallonsu ta share xufar dake ta sauka fuskarta ta koma gefen gado ta xauna tana tunanin abun yi. Inna na kallon Mama Hadiza da Aunty tayi wani murmushi tace "To kun dai jiye ma kunnan ku komai,