Showing 204001 words to 207000 words out of 303099 words
ka fito da xancen aure ba yanxu" A hankali Sadeeq ya mike ya nufi kofa ya fita parlon Mummy ta bi sa da kallo, Alhaji Ahmad yace "In sha Allah daurin aure babu fashi ranan juma'ah..... No one is tarnishing my image" direct Sadeeq part din Step mum dinsa ya wuce, Aunty na dakinta ya sameta, ta ajiye abinda take yi tana kallonsa tace "Ango kayi scarce, ya shirye shirye" ya karasa kusa da ita ya xauna ya rike kansa, da mamaki tace "Me ya faru Abba?" Da kyar ya dago yana kallonta da idanuwansa da suka kada yace "Pls Aunty kiyi ma Abba magana a daga bikin nan, wllh naji gaba daya am not ready to be a family man, wani lkcn sai ayi amma ba yanxu ba" Bude baki Aunty tayi tana kallonsa, da wani expression tace "Are you alright Sadeeq? Kana da hankali kuwa, biki saura few days kace a daga, waye kake son maidawa kananun mutane, ubanka dai koh? Kai ma kasan Abban ka will never support this, wani laifi fatiman tayi maka ne?" Ya girgixa kai a hankali yace "Ni bata min komai ba, kawai naji bana ra'ayin aure yanxu, ba cewa nayi a fasa ba, a daga kawai nake so... " Aunty ta saki baki tana kallonsa with much surprise, can ta girgixa kai tace "Don Allah ka rufa mana asiri, kada ka maida mu kananun mutane a idon jama'ah Abba, haba Sadeeq this is very unusual of you, me ya same ka haka, ko dai gantalallun frnds dinka ke xuga ka??" Rasa ma me xai ce mata yyi, can ya mike kawai ya fice daga dakin ta bi sa da kallo baki bude. Mummy ta gama hada duk kayan da suka ma Imaan kala uku masu tsada, daya na dinner biyu kuma na events idan xa su yi a gida, immediate din Sadeeq Annur ta samu a dakinsa ta mika masa tace "Gashi ka kai ma yayanka yana garden, kace nace ya tafi ya kai masu yanxun nan" daga haka ta fita dakin. Bayan Magrib Sadeeq yyi parking kofar gidansu Imaan ya kashe motar ya fito ya dau ledan kayanta dake bayan motar, ya fi minti biyar tsaye jikin motarsa ya ki kiranta a waya, can kawai ya shiga cikin gidan kamar mai counting steps dinsa, direct part din Inna ya nufa, yayi sallama bakin kofar parlon, Inna ce ta amsa sannan ya shiga, Mama Hadiza dake xaune parlon tana cin abinci suna hira da Hajiya Bilki mai gyaran jiki, ta rufe abincin ta ajiye gefe ganinsa, Inna ta mike ta shimfida masa darduma tana masa sannu da xuwa, sauke kansa yyi kasa yana d'an murmushi ya ajiye ledan hannunsa ya xauna a hankali ya gaida su gaba daya, Mama Hadiza ta amsa tace "Sannu da xuwa Sadeeq..." yace "Kun xo lafiya mama?" Tace "Alhmdllh, ya shirye shirye?" Yace "Alhmdllh" Inna tace "Kaga yanxu kuwa ta fita taje raka wannan yarinya Maryam su gaisa da Ahmadu ko a kira maka ita a waya?" Yace "A'a kaya ne dama na kawo mata" Inna tace "Atoh ai shkkn sai in ajiye mata, kana dai cin abinci kuwa Bukar naga kai ma ka fige kamar amaryar taka" murmushi yyi ya sunkuyar da kansa yace "Ina ci Kaka" da damuwa Inna tace "Aa ku dai yi hakuri ku kwantar da hankalin ku ko kwa yi kyan gani da biki don Allah..." Shi dai bai ce komai ba, Bude kofar parlon aka yi Mujaheed ya shigo da sallama, sanye yake cikin kananun kaya hannunsa rike da makullin mota, Tunda ya shigo Mama Hadiza ke kallonsa, yyi murmushi yana shafa kansa ya karasa cikin parlon, sai da ya fara ba ma Sadeeq hannu sannan ya xauna kusa da Mama Hadiza a hankali yace "Kun xo lafiya mama?" Ta rike ha6a tace "Kayi rashin lafiya ne ba a gaya min ba Muhd?" Yace "Ae naji sauki yanxu, kwanaki ne nayi rashin lafiya, tare da Maryam ku ka xo?" Inna dake kallonsa da kyau tace "Toh dai yau ga ni, ga Mujaheed, ga Hadiza da katuwa mai gyaran jiki, ga kuma yaron nan Sadeeq, sai Mujaheed ya ji tsoron Allah ya fito ya gaya ma kowa abinda na masa a parlon nan yanxun nan... Don ni ban san abinda na masa ba, idan Mujaheed bai saka min da abun kirki bautar da na masa ba yana yaro ai baxai guje ni ba yanxu da tsufa na, Hadiza yau kusan wata shidda kenan ban sa Mujaheed a ido ba, ba laifin tsaye balle na tsaye, ba lafin fari balle na baki, ko na kirasa baya dauka to ni dai gaskiya ya fito ya fadi abinda na masa ko in bar sa da Allah..." Ko kallonta Mujaheed bai yi ba sai juya makullin hannunsa yake, Hajiya Bilki dai sai dariya take kasa kasa, Mama Hadiza ta kasa cewa komai sai kallon Inna take ganin yanda ta ci serious ta tsuke fuska, Sadeeq dai idonsa na kan wayarsa da yake dannawa, cikin rawar murya Inna tace "Ko don nace matarsa mayya ce ya kullace ni ban sani ba, toh banda haka me na ma Mujaheed, wllh ban masa komai ba, ko wani kaga xai mance da ni haka a rayuwa kai ba mai tare min bane balle kai da kanka, gashi duk ka wani fige kamar kazar Hausa kuma ace yarinya ba mayya bace.... Ni dai ba ruwana" Mujaheed na kallon Mama Hadiza yace "Ba ku taho da su El-Ameen ba?" Mama Hadiza ta sauke ajiyar xuciya tace "Xa su taho tare da babansu xuwa jibi, xai xo daurin auren shi ma" Inna ta bude baki tace "Toh shi Mujaheed ba mutum bane da ya ki xuwa nasa daurin auren?" Mama Hadiza tayi murmushi tace "Inna kar ki manta Imaan ita kadaice gun Yaya, banda haka ma da ba lallai nima in xo ba tunda yaushe na xo bikin Mujaheed, to wannan dalilin yasa babansu Maryam ma xai xo daurin auren nata...." Inna ta tabe baki tace "Ku dai ku dinga tsoron Allah, ku dinga abu saboda Allah, wato shi Mujaheed bai cancanci a xo nasa ba sai na Imaan, to ubansa ya sha Mama ya bar ma ubanta, duk babu wani banbanci" dariya kawai Mama Hadiza tayi bata dai ce mata komai ba, shi dai Sadeeq idonsa na kan wayarsa, Maryam ce ta fara shigowa parlon Sadeeq ta fara gani ta gaishesa da fara'a, ya amsa yana murmushi yace "Kun xo lafiya Maryam?" Tace "Alhmdllh Dr, ya shirye shirye" yace "Lafiya lau" ta wara ido ganin Mujaheed tace "Ya M.A..." Imaan ta shigo parlon hannunta rike da fruit salad da Ammi ta bata ta kawo ma Mama Hadiza, ganin Mujaheed xaune parlon ta tsaya tana kallonsa ko kiftawa babu, daga kai yyi ya kalleta, bata san lkcn da ta ajiye bowl din hannunta ta nufesa da sauri ta xauna kusa da shi tana kallonsa ta wara ido tace "Yaya..." Ya shafa kansa kamar baxai ce komai ba sai kuma ya d'an ja hancinta yace "Kanwar Yaya..." dariya ya bata, ganin yanda take dariya yyi murmushi yana kallonta, rungumesa tayi a hankali tace "I missed you" Kallonsu kawai Sadeeq yake, Mama Hadiza ta dinga ma Imaan wani kallo amma imaan ko sanin tana yi bata yi ba, Inna tayi tagumi ta rasa abun cewa sai yan idanuwa, Can a fusace tace "Ke dai gantalalliya ce wllh, katuwa da ke ki fada jikin mutumi wai Yaya, yanxu fa ke matar wani ne, da ba don mijin naki ya san alakar ki da Mujaheed ba me kike tunanin xai faru yanxu? Kawai mata daga shigowa ki dare kan mutumi kice Yaya???" Da sauri Imaan ta sake Mujaheed ta juyo, sai a nan suka yi ido hudu da Sadeeq, sosai gabanta ya fadi ta xamo kasa tana kallonsa, Mama Hadiza dai ta kasa cewa komai amma gaba daya kunya ya isheta, Inna tace "Toh waye kuma Yaya Allah na tuba ke ba yarinya ba yanxu, mutumi yyi aurensa kema xa ki yi naki, ai kuma sai a hakura haka sai 'ya yanku su ci gaba da xumuncin, ni dai ban taba ganin haka ba...." Sadeeq ya d'an yi murmushi ya mike yace "Kaka ni xan koma yanxu" Inna tace "Au to baka sha ko ruwa ba Bukar" yace "Ae daga gida nake Kaka" Inna tace "Toh shikenan Allah maka albarka, kuma ka dinga cin abinci kaji" yace "In sha Allah" Yana kallon Mama Hadiza yyi kasa da kai yace "Mama xan koma, Allah huce gajiya" Mama Hadiza tace "Toh ka gaida mutan gidan Sadeeq na gode kwarai" kofa ya nufa, Inna na kallon Imaan tace "Ae sai ki tashi kusa da mutumin nan ki tafi ki sallami mijin ki koh" Kin tashi Imaan tayi, Mama Hadiza na ganin Sadeeq ya fita tace "Baxa ki tashi ki fita ba shashashar yarinya, kawai ki kama ki rungume mutum a gabansa sbda baki da natsuwa" a fusace Inna tace "A'a ke kuma bana son fadan rashin gaskiya, wa gareta da xata rungume banda Mujaheed din, a haka suka taso abun su dama can, shi ma mijin ai ya sani, ko ce maki aka yi bai sani ba, sarai ya san yayanta ne bata da kamarsa a duniya ko kun haifa mata wani yayan ne ban da shi Mujaheed din?? Ni bana son fadan rashin gaskiya wllh, kinsan yaushe rabon mu sa Mujaheed din a ido ne? kuma ta gansa baxata nuna farin cikinta ba, kullum sai ta min xancensa don ma Ina gwaleta kamar bai dameni ba alhalin kullum da daddare sai nayi mafarkinsa, kawai mata daga xuwa ki hau yar mutane" Hajiya Bilki ta dinga dariya tana kallon Inna, a hankali Imaan ta mike ta bi bayan Sadeeq Mujaheed ya bi ta da ido.
*Imaan isn't for free* it's 300 via
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788
73.....
A hankali Imaan ke tafiya tana kallon Sadeeq da har ya kusa gate sbda saurin da yake, kafin ta fita kofar gida har ya shiga motarsa ya wuce, ta bi motar da kallo sannan ta juya a sanyaye ta koma part din inna, Mama Hadiza dai har lkcn ta ki sake fuska don ba karamin 6ata mata rai abinda Imaan tayi yyi ba, tana shigowa parlon kuwa ta dinga hararanta fuska daure, Imaan na ganin haka ta sunkuyar da kai ta wuce bedroom din Inna duk jikinta yyi sanyi, Inna ta bi ta da kallo sai kuma ta kalli Mama Hadiza tace "Toh ba shikenan ba har ta sallamesa ta dawo, amma kina neman maida karamar magana babba sbda rashin tsoron Allah, ai shi Sadeeq din ya fi kowa sanin tsakaninsu da Mujaheed, kuma yaro ne mai hankali da natsuwa, tunda nake ban taba ganin yaro natsatstse irin sa ba, gashi kwata kwata abun sa bai rufe masa ido ba, kyauta yake kamar bai san ciwon dukiyar ba, to bayan ni har ku ma baxa ku huta ba aka ce maki Hadiza??" Ita dai Mama Hadiza bata ce komai ba tayi tagumi, Inna ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana... A dinga kyakkyawan xato domin Allah, sai kace warce ta fada kan wani kato can a titi, wannan ae yayanta ne Mujaheed" Mujaheed ya mike yana kallon Mama Hadiza yace "Toh na gaishe ki Mama Allah ya huce gajiya sai na shigo gobe" Inna na kallonsa tace "Amma kai dai Allah ya xuba maka shegen rowa Mujaheed kamar uwarka, banda haka ina laifin ka riko mata Yar gasasshen kazar nan da yar lemo... ka wani shigo gansansan daga kai sai kai, inda Isuhu ya fi ka kenan gaskiya" Mujaheed dai bai tanka ta ba ya nufi kofa, tace "Toh nayi magana daxu baka ce komai ba, ina fa da labarin abinda kayi ma Seeyama lkcn bikinta, to ita Imaan ko don ba ubanku daya ba, naga har yanxu shiru baka yunkuro ba, kyansa dama kawai ka bata kudin ni nasan abinda xan mata da shi, kar ka siya mata komai ba abinda Ahmadu da Bukar basu yi mata ba, kudin xai fi mata amfani gaskiya" ya juya ya kalleta yace "In xan bata abu ae ba sai kin sani ba Hajiya, sai kace mahaifiyarta bata kusa....." Daga haka ya fice daga parlon Inna ta rike ha6a tana kallon Mama Hadiza tace "Ke me yake nufi kenan? Kaddai baxai ma yar uwarsa komai ba bikinta sukutum da guda?? To bari dai in xuba ma saurautar Allah ido, amma wllh in har Mujaheed bai bada gudunmawa mai kauri bikin Imaan ba lalacewa ta samesa duniya da lahira, kuma ban san da wani idon xai kalli ubanta ba" Washegari laraba da safe driver ya ajiye su Imaan saloon, Mai wajen da kanta tayi mata gyaran bayan ta gano amarya to be ce, Banda kallonta babu abinda ake yi a saloon din, don gaba daya she looks so new, tayi wani haske da fresh sai glowing ko ina na jikinta yake kamar balarabiya, dubu ashirin Abba ya basu na gyaran gashin su uku don Ummi da Rahma basu yarda sun biyo su ba, da kyar Maryam ta lallaba Imaan ta yarda ayi mata kitso a gashinta, imaan har ta mance rabon da tayi kitso, haka aka ta daure aka rangada mata kitsonta kanana mai kyau, sai kusan azahar suka kira driver ya xo ya maida su gida. Sosai gida ya cika da jama'ah na kusa da nesa duk da sai Juma'ah ne bikin amma kai kana ganin jama'ahn gidan kasan only child ce xa ayi ma aure, kuma ga biki ya hade biyu, gaba daya yan uwan Ammi suna gidan, daga su har 'ya yansu, Aunty ma duk yan uwanta na kusa da nesa sun iso, Bakin ciki kamar xai kashe Umma, kwata kwata taki yarda ta fito daga dakinta har da sa makulli daga ciki abun duniya ya taru ya mata yawa, anya auren nan baxa ayi sa ba kuwa?? Tambayar da ta dinga yi ma kanta kenan, wata xuciyar na assuring dinta baxa ayi ba ta xuba ido kawai. Su Imaan na komawa gida da awa daya mai lallin da Aunty ta kira ta xo gida yi mata lalle, Inna ta gama xuba ma imaan pepper soup din da Aunty ta aiko mata da abinci kenan mai lallin ta shigo tare da Maimoon, Maimoon tace "Inna mai lalli ce" Inna ta kalli mai lallin da damuwa tace "Naga jaraba, ko abinci fa bata ci ba kika xo lalle baiwar Allah.... Tun safe take garari a titi wai gyaran gashi ynxu kuma daga ta fito wanka na xuba mata abinci sai ki xo kice kin xo lalle baiwar Allah, ba fa ta ci komai ba" Mama Hadiza dake parlon ta kalli mai lallin tace "D'an yi hakuri ta ci abinci yanxu ta gama Aunty..." Mai lallin tace "Toh xan jirata a waje" daga haka ta fita, Inna ta harari Mama Hadiza ta gefen ido ta dau abinci ta tafi daki kai ma Imaan tana cewa "Abu dai munafurci munafurci ba a son fadin gaskiya, na ma mata maganar gaskiya kin kwantar da murya kina mata magana salon ta min kallon fitinanna" Imaan ta gama saka kaya kenan Inna ta shigo tace "Ki ci abincin ki a nutse kafin ki fito wani shegen lalli, ba ruwana da gantalewa, ko lallaba maki lallen bana yi da kaina ba cikin dare" daga haka Inna ta juya ta fita. Maryam na kallon Imaan dake tsakuran abincin da Inna ta ajiye mata tace "Ki bani number Sadeeq in kirasa ai shi ya kamata ya baki kudin lalle da kitso ba su Abba ba" Imaan ta kalleta, sai kuma tayi murmushi tace "A'a just leave him... There is no need ai Abba riga ya bada" Maryam tace "Like seriously tun xuwan mu kasar nan ban ga ya kiraki ba Imaan, there is something wrong somewhere bai kamata kiyi shiru ba gashi jibi daurin aure ki cuci kanki" Imaan ta tabe baki tace "Am not saying anything Maryam, kika san uxurinsa" Maryam tayi shiru tana kallonta da mamaki, Imaan ta mike ta rufe abincin don gaba daya ta kasa ci, tun last week tayi loosing appetite dinta gaba daya, a hankali Maryam tace "Baki ci komai ba a abincin Imaan" Imaan tace "Mai lallen tana ta jirana, anjima xan ci" daga haka ta fita dakin, Maryam ta bi ta da kallo, bayan few minutes ta dau wayarta ta shiga duba number Sadeeq, tana gani tayi dialing, har ya gama ring bai dauka ba, ta sake kira nan ma bai daga ba, kwashe lambar tayi a nata wayar ta ajiye ta mike ta shiga gyara ma Inna daki, tana gamawa ta dawo ta xauna ta dau nata wayar tayi dialing number din Sadeeq, ba a dau lkci yana ring ba ya daga, shiru tayi da farko sai kuma tayi masa sallama, ya amsa, tace "Sadeeq?" Yace "Yes..." tace "Why the sudden change of attitude toward ur financee Sadeeq?" Ya d'an yi shiru kafin yace "Wait! Who is this?" Tace "You answer my question first..." Yace "I don't think you are in the rightful place to..." A d'an fusace tace "Kar ka gaya min magana malama, wato kai a silly thought dinka ka riga da ka sameta xaka fara walakantata tun bata shiga gidanka ba ko?? to wllh karya kake Imaan ta fi karfin haka, you are mistaken malam, domin ka kawo sadaki kuma jibi daurin aure ba yana nufin har ta xama taka ba...." Ya katse ta shi ma yace "Toh ki ce mata tayi xuciya ta gaya ma iyayenta ta fasa auren kawai, sai su maido min da sadakina.... I think this will be better than you calling and saying nonsense on phone to me madam" daga haka ya katse wayar, Maryam ta dinga kallon wayar da mugun mamaki nan ko xuciyarta cike yake da tantamar anya Sadeeq din da ta sani ne wannan, Anya Sadeeq din da ya siya mata latest phone da take mafarkin mallaka kwanaki da suka xo Nigeria kawai don tayi masa addu'ar Allah ya bar sa da Imaan ne wannan, mikewa tayi very shock ta fita dakin,