Showing 234001 words to 237000 words out of 303099 words
bangaren Inna tun ran Friday, Aunty na kallonsu Maimoon tace "Ku tafi can apartment dinsu ku duba ko tana can" fita suka yi parlon gaba daya, Abba na kallon Inna ganin yanda ta rikice yace "Bari a dubota can bangaren su, amma ina xata je dama Inna" Inna ta bi bayansu Maimoon da sauri, tana tsaye bakin kofa sai xaxxare ido take tana jiran fitowarsu, Maimoon ce ta fara fitowa tace "Bata nan fa Inna" Wani salati Inna ta rafka da karfi sai kuma ta fashe da matsanancin kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, bata ciki fa ku ka ce???" Su Abba da Aunty duk suka fito tsakar gida Mama Hadiza ma ta fito bayan Maryam ta je sama ta gaya mata abinda ke faruwa, Daddy dai na tsaye balcony dinsa yana kallon mahaifiyar tasa, Inna ta tsaya dai dai tsakar compound din ta daura hannu a kai ta dinga rusa kuka tana cewa "Na shiga uku Allah ka dubeni kada Bukar ya kullace ni har gobe kiyama, Ina imaan xata shiga da tsakar daren nan jama'ah, wllh wanke bandaki nake na fito naga babu ita sai kwanon farfesunta, na shiga uku jama'a ku taimakeni kada a dinga cewa a parlona Imaan ta 6ata...." Mama Hadiza ta nufe ta da sauri tace "Haba Inna meye haka kuma, ce maki aka yi Imaan din 6ata tayi? Haba don Allah" Cikin kuka Inna tace "Idan ba 6ata tayi ba to Ina take Hadiza?? Kafff gidan nan an duba bbu ita babu alamarta fa, Wllh da ba a bangarena take ba bbu abinda xai dameni sai dai a daure Ahmadu tunda shi yyi mata auren dole, yanxu kuwa ai ni xa a daure tunda kowa yasan a bangarena take, da wani bakin xan ma 'yan sandan bayani idan an tafi dani?? Kuma duk aka tashi magana dama cewa xa ayi parlon Inna ta 6ata, to ina dalili a sa ni a bakin duniya Hadiza???? Don Allah ku min rai a nemo ta kada in shiga uku, wannan ba karamin magana bane wllh" Ta kuma rushewa da kuka har da durkusawa kasa tana salati, Abba dai ya kasa cewa komai haka ma Daddy da ya makale a Balcony dinsa, Inna ta kara mikewa tana kuka sosai ta nufi gate tana cewa "Duk Ahmadu ne ya jaza mana fitinar nan gaskiya idan wani abu ya sami jikata xan rufe ido in mance ni na haifeka Ahmadu" Umma da shigowarta gidan kenan daga gidan Hajiya Saude ta makale parking space tana wurwurga ido jin wai ba a ga Imaan ba, Inna na kallon mai gadi a waje ta fixgosa tace "Ilu kaga fitar Imaan?" yace "A'a ban gani ba Baaba..." Inna ta wani xaro ido ta turasa kawai ta fice gate din ta saka kai gaba sai babban titi tana salati tana rusa kuka, Mama Hadiza ce ta bi ta tana kiranta amma Inaaa... Karfe goma saura Mujaheed ya mike daga xaunen da yyi gefen gado tun shigowarsu yana kallon football a tv na bango dake manne a dakin hotel din, Imaan dai har lkcn tana durkushe inda take tun daxu, banda axaban ciwo babu abinda kanta da duk joints dinta suke mata amma ko xama ta ki yi, ga kuma bacci dake fixgarta, ta dai gaji da kuka da rokonsa da take tayi tsit ta xuba ma saurautar Allah ido, satan kallonta Mujaheed yyi ganin idonta a lumshe bacci ya dauketa a yanda take, ya dau remote ya kashe tvn ya mike a hankali ya nufeta, dukawa yyi ya dagota ta farka a rikice xata fasa masa ihu ya rufe bakinta a jikinsa, jikinta ya dau rawa tana kokarin kwace kanta bai ajiyeta ba sai saman gado, xata mike ya hade rai, calmly yace "Lie still..." Kai kawai take gyada masa a tsorace, ya dinga kallonta ko kiftawa babu, kamo hannunsa tayi tana girgixa masa kai pleadingly tace "Don Allah Yaya ka maida ni gida kila ana ta nemana wllh" Ya xame hannunsa still looking at her yace "Kila don kina ganin ki a kadunan yasa kike tunanin xan maida ki gida, Allah ya kai mu gobe da safe, I will eraze that thought off ur mind" Ta dinga kallonsa xuciyarta na bugawa, mikewa yyi ya nufi switch din dakin ya kashe wutan, ta mike xaune da sauri gabanta na faduwa tana kallonsa cikin duhu, a hankali tace "Yaya..." D'an Murmushi yyi ya nufi kan gadon, tuni ta sauka ta tsaya tana kallonsa cikin duhun xuciyarta na bugawa....
*Naji kuma xan iya, though it's short... Thanks for the prayers*
*Imaan isn't for free* it's 300 via
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788
83......
Mujaheed bai yarda ya kalleta ba ya ciro wayarsa a aljihu ya xauna saman gadon ya kunna wayar, ita dai tana tsaye tana kallonsa gabanta na faduwa, number yyi dialing ya jingina da gadon, Safeenah dake kwance saman gadon hajiyarsu an cire mata drip kenan har ta fara bacci ta mike xaune da kyar tana kallon wayarta dake gaban mirror yana ring, Hajiya Baturiya tace "In ma xa ki rabu da wayar nan kiyi baccinki ki rabu da shi..." A hankali tace "Toh idan shine fa Anty?" Hararanta Hajiyan Marafa ta dinga yi daga inda take xaune, yayarta Sajida tace "Wlh idan kika ja ma kanki wani ciwon Safeenah iyaka namu muyi ta maki fatan samun lafiya, me aka yi aka yi Mujaheed da xa ki nemi hallaka kan ki a kansa? Mutumi da har yau bai kira ki ba balle ki san abinda ake ciki, wa ya sani ma ko da saninsa aka yi auren ma tunda uwarsa ce kan komai" Safeenah ta kalleta da sauri tace "A'a wllh bai san da auren ba, nasan shima hankalinsa ne ya tashi shi yasa muka ji sa shiru" Hajiyan Marafa tace "Na rasa wannan bala'in ni dai, haka kawai ki dauki namiji ki sa a rai kina neman ja ma kanki wani ciwon??" Safeenah ta sauka saman gadon da kyar ganin basu da alamar dauko mata wayar, tana isa gaban mirror din ta xaro ido tana kallon wayarta tace "Wllh shi ne Mummy..." Da sauri ta daga wayar kafin ya katse ta kai kunne, kawai sai ta fashe da kuka sosai, Mujaheed yyi shiru yana sauraronta na few seconds, can yace "Let me assume baki son kiran nawa kenan..." Da sauri tace "Me yasa ka kashe wayar ka all this while Mujaheed, me yasa baka yi tunanin halin da xan shiga ba a wannan lokacin, don Allah ka ce min karya ne baka min kishiya ba, kace min karya ne ni kadai ce matar ka Mujaheed, I can't imagine my self sharing you with any lady wllh baxan yarda ba, ni ce kadai matarka a duniya" Ya daura kansa saman pillow dake kusa da shi yyi kasa da murya yace "Yanda kika samu labarin auren nan haka nima na samesa Safeenah, I know nothing about it, ban san komai a kan auren nan ba..." Kuka take sosai tace "Wllh Mujaheed na isheka duniya da lahira me xa kayi da wata matar kuma, kayi min rai kada ka min kishiya, ka barni ni kadai a gidan ka, na isheka duniya da lahira, don Allah kace min babu xancen auren nan kuma plsss..." Bai san lkcn da yyi murmushi ba a hankali yace "Marriage or no marriage Safeenah you still remain my first, ke ce matata ta farko, then why worry?" Imaan dake tsaye tana kallonsa tunda ta fahimci da warce yake waya ta wani daure fuska ta juya masa baya tana jin wani irin haushi a xuciyarta, kuka kawai Safeenah take kamar ranta xai fita tace "Kana nufin da gaske kenan auren na nan Mujaheed, Kuma wai da cousin dinka da ta raina ni?? Nooo plss wllh baxan iya sharing mijina da ita ba, I can never, you are meant for me alone, tell ur parent u don't need a second wife plss, ban rage ka da komai ba..." Murmushi yyi sosai yace "Thank God you know I don't need a second wife, then why disturb ur self?? I just have to obey my parent that's all" Juyowa Imaan tayi a hankali tana kallonsa, yace "I will call you tomorrow, get set before 9:00am xan xo" daga haka ya katse W
wayar yana satan kallon Imaan, missed calls din Mama Hadixa ya gani kusan shidda, tun yana waya yake jin shigowar kiran nata, murmushi yyi ya shiga gun text message ya tura mata text kamar haka, "Am sorry I did what is wrong Mama, but I think this the only way out don baxan iya sakin Imaan ba" yana tura mata ya kashe wayar gaba daya yana kallon imaan dake tsaye har lkcn tana kallonsa, kwanciya yyi saman gadon ya lumshe ido, ta goge hawayen dake sauka idonta har lkcn tana kallonsa, da ta tuna abinda yace ma Safeenah sai taji wasu hawayen sun taho mata, tana ta tsaye har bayan kusan minti talatin, jin kafafuwanta sun gaji ga bacci da ta fara ji ta durkusa a hankali tana ta6a tiles din dakin taji sanyi, ta dauke hannunta ta mike tsaye tana kallonsa, bayan kusan minti biyu ta xauna gefen gadon a hankali tana satan kallonsa, jin bai motsa ba duk da ba ganin fuskarsa take ba ta gane kilan yyi bacci, kamar me tsoron gadon ta kwanta a edge ta juya masa baya ta rufe ido, a hankali ya juya yana kallonta bayan few minutes, mirginawa yyi side dinta, cikin bacci kawai taji sa kusa da ita, Bude ido tayi a tsorace xata mike ya riketa, cikin rawar murya tace "Wayyo Yaya plss ka bari, meye haka" yace "Waye yayanki?" Jikinta ya dau rawa tana girgixa kai tace "Ba kowa wllh" yyi kasa da murya drawing her closer to himself yace "Who am I to you now?" Hawaye ne ya shiga sakko mata ta ki cewa komai, ya daura forehead dinsa kan nata ta rufe ido da sauri, yace "Talk to me now" a hankali tace "Yaya kai na fa ciwo yake min da bayana tun daxu...." ya kwantar da kanta a hankali kan chest dinsa cikin sanyin murya yace "Tell me... Me yasa kike son in sake ki bayan destiny da ya hada mu Imaan? Baki tunanin kilan dama we where meant for each other, isn't this great? everything just happened all of a sudden, so fast, baki tunanin wannan wani al'amari ne babba, why kike so na sake ki?" wasu hawaye masu xafi suka dinga xubo mata ta lumshe idonta ta ki cewa komai, a hankali yace "Talk to me pls" ta bude idonta tace "Saboda kai na dauke ka a matsayin yayana ne..." ya d'an yi shiru sannan yace "Kenan ba aure tsakanin mu?" Ta girgixa kai cikin rawar murya tace "Akwai...." Yace "Toh me yasa kika bar sa a matsayin babu a xuciyar ki?" Tace "Saboda Ina maka kallon yayan da muka fito ciki daya, I grew up looking at u as my blood brother, I've neva tot of living together with you as..." Sai kuma tayi shiru, ya d'an yi murmushi yace "Ni kuma ban taba maki wannan kallon ba, Ina maki kallon cousin dita ce da xan iya aure ta haifa min kyawawan yara masu shagwaba da son jiki irin nata, masu dogon hanci da karamin baki irin nata, masu asthma da ....." Dukansa ta yi a kirji kamar xata yi kuka tace "Ni bana sooo...." Yana murmushi ya rungumeta sosai cikin sanyayyan muryarsa yace "In sha Allah our kids will be more than healthy..." ta dago da sauri ta kallesa tace "Ni fa baxan xauna da kai ba as my husband, I just can't... Bayan ga matarka da ka gama ce ma kai baka son auren" Kallonta kawai yake ko kiftawa babu, xuciyarsa ya dinga raya masa yyi mata abinda yyi parlon Inna jiya amma kuma kawai sai ya ji nauyin yin hakan, saketa yayi, yyi kwanciyarsa yana murmushi yana tunanin ranan da xai nuna mata shi ba yayanta bane, soon but not in a hotel room, xamowa kasa tayi, tana turo baki tana kallonsa, daga karshe dai ta duka nan kasa ta kwantar da kanta saman gado a haka bacci ya dauketa, mikewa yyi jin alamar tayi bacci ya xaga ya dagata sama ya kwantar da ita saman gadon ta riko hannunsa cikin muryar bacci tace "Yaya I am feeling cold..." kwanciya yyi kusa da ita ta shige jikinsa, yyi murmushi yana kallonta ya cire mata hijab din jikinta keeping her more closer to himself, gaba daya scent dinta ya cikasa, ya lumshe ido trying to force him self to sleep, but the thought of imaan by his side, sooo close... as his sunnatic wife couldn't let him, gashi da yyi yunkurin gyara kwanciyarsa just to maintain sai ta kara shige sa, and he wish everyone was happy with this surprise marriage, da ya fi kowa murna da farin ciki a duniya, duk ya tuna Ummarsa sai ya ji gabansa ya fadi, don tun da aka daura auren bai yrda ko na second daya sun hadu ba. Sai kusan karfe biyu da wani abu na dare bacci ya daukesa, duk da sanyin da yyi yawa a dakin bbu me jin hakan a cikinsu.... Da asuba kiran sllh ya farkar da Mujaheed, ya kalli Imaan ya gyara mata kwanciya xai mike ta rikosa, kunna kananun wutan dakin yyi yana kallon fuskarta yaga bacci take, xai tashi ta kara rikesa, murmushi yyi ya ja dogon hancinta hakan yasa ta bude ido a hankali, ya kai hannu goshinta ta wani hade rai tana kallonsa ta mirgina da sauri daga wajen, sauka yyi saman gadon ya shiga bathroom, tashi tayi ta jawo hijab dinta ta saka ta kashe Ac din dakin ta koma can karshen gadon ta kwanta tana tunanin lkcn da ta hau saman gado ta kwanta, yana fitowa ya kalleta yace "Baxa ki yi sllh ba" shiru tayi bata ce komai ba fuska daure, ya fita dakin, sai a sannan ta mike ta wuce bathroom din, har ya dawo masallaci tana xaune saman darduman da ta gani a dakin tana azkar, ya xauna gefen gadon yana kallonta, ita dai bata yarda ta kallesa ba, ya dawo kusa da ita a hankali yace "Good morning wife" Bata fuska tayi tace "Ni ba wife din ka bace" Ya wara ido yace "Ohh don ban nuna maki ke wife dita bace jiya da daddare koh?" Dauke kai tayi ta ki cewa komai, ya gyada kai Yana murmushi yace "Xan yi maganin ki, abinda dare da yawa" Yana fadin haka ya mike ya hau saman gadon ya kwanta hade da lumshe ido. Karfe bakwai da wani abu suka bar hotel din, Imaan dai sai kallon hanya take tana jiran ta ga inda xai kai ta, ganin sun dau hanyar kano ta xaro ido a tsorace tana kallonsa kamar xata yi kuka tace "Yaya don Allah ka bari, where are you taking me to plss, wllh nasan ana ta nemana gida ka mayar da ni don Allah" Yana kallon titi a hankali yace "Kaf gidan nan yanxu bbu mai iko da ke, so they are all supposed to know that kina wajen mijin ki su xuba mana ido kawai, su da xa mu dawo masu da cute kids in sha Allah, sai mu ba Umma daya mu ba Ammi biyu mu ba Aunty daya sai mu tausaya ma Inna ita ma mu bata guda daya duk da lalata mana ita xata yi yanda ta lalata ki...." hawaye Imaan ta fara yi tana kallonsa tace "Don girman Allah ka mayar da ni gida Yaya, stop this joke" gently yace "You think I am joking ko? Xa ki sha mamaki kam" Ta dakatar da kukan da take tana kallonsa ganin he is so serious, Bai kalleta ba driving kawai yake da d'an gudu, tayi kasa da murya tace "Don Allah kar ki min haka Yaya, kar ka raba ni da Ammina..." sae kuma ta fashe da kuka, yace "Idan ban raba ki da ita ba ynxu ae ita xata raba ni da ke, ni kuma baxan yarda a raba ni da ke ba coz I want to live with my lil sis in one roof" Tafiyar kusan minti hamsin yyi ya shiga garin Zaria, Imaan dai gaba daya she is shock ganin da gaske fa Mujaheed yake, wani babban gida yyi Parking ya fito yana rike da mukullin gidan ya bude gate din ya dawo motarsa, ya shiga gidan yyi parking a space na mota hudu dake babban compound din ya kashe motar ya fito yana kallonta, bin gidan kawai take da kallo kusan a tsorace, ya rufe side dinsa ya xaga ya bude inda take yace "Come down" ta hade hannunta tana girgixa masa kai tace "Am begging you ka mayarda ni gida don Allah Yaya, Kar ka min haka" sakko da ita yyi daga motar ya rufe yana rike da hannunta ya nufi entrance din shiga gidan ya sa makulli ya bude, parlor ne babba, kuma bbu abinda bbu a ciki amma duk komai ya d'an yi kura, ya kulle kofar parlon ya sa makulli sannan ya wuce stairs, Imaan ta durkushe wajen jikinta a sanyaye ta ma kasa kukan, lkci daya ta mike tana xaro ido da karfi tace "Yayaaa" sai kuma ta nufi stairs da gudu tana ci gaba da kwala masa kira, Mujaheed ya fito daki da sauri yana saukowa stairs suka kusa cin karo, rungumesa tayi jikinta na rawa tace "Kamar na ga wani abu yana tafiya wllh Yaya, I saw an insect" Jan ta yyi xuwa sama ya bude bedroom yace "Tafi ki yi wanka na hada maki ruwa" a tsorace tace "Ni dai Yaya wllh kamar cockroach na gani fa" yyi murmushi ya kama hannunta xuwa bathroom yace "Toh muje in raka ki kiyi wankan" bin bayansa ta dinga yi tana kallon kasa ko xata kara ganin wani, yace "Toh cire kayan" Hijab dinta ta cire ta ajiye gefen gado, ta fara kokarin cire dogon rigar baccin jikinta, shi dai kallonta kawai yake har ta fara dage rigan, sai kuma