Showing 237001 words to 240000 words out of 303099 words
tayi still ta kallesa, ganin yanda yake kallonta tayi wani kara ta sauke rigar kasa ta durkushe tace "Wayyo Yayaaa bana son haka" Yana murmushi ya durkusa shi ma yace "Baki son me??" Bata yarda ta kallesa ba ya mike ya tafi gefen gado ya xauna yace "Toh ki shiga kiyi Ina jiran ki a nan" mikewa tayi ta shige bathroom din ta rufe kofa har da sa makulli. Fita dakin yyi ya ya dawo parlor, ya bude kofa ya fita ya kulle ta waje sannan ya bar gidan, few shoppings yyi ya siyo har da breakfast ya dawo gidan, ya ajiye ledojin hannunsa a parlor ya wuce sama ya bude dakin, tsaye ya ganta jikin window wayarsa kare a kunnenta idonta sha6e sha6e da Hawaye, jin an bude kofa ta juya tana kallonsa ta katse wayar tana shessheka, ya tsaya nan bakin kofar ya dinga mata wani kallo, a hankali ta dinga share hawayen idonta, ya karasa cikin dakin ya fixge wayar yana duba screen din ya ga number Daddy, barin wajen take so tayi ya fixgo hannunta fuska daure yace "What did you tell him??" Ta fashe da kuka tace "Ni dai Yaya don Allah kayi hakuri ka mayar da ni gida, ni bana son ka baxan xauna da kai ba..." Call duration din kiran ya duba yaga kusan 7 mins, ya hade rai sosai yace "I asked what did you tell him??" Ta make masa kafada cikin rawar murya tace "Ni nace masa ya xo ya daukeni baxan xauna a nan da kai ba, nace masa ni bana sonka" Kiran Daddy na ya shigo wayar, ta goge idonta da sauri xata amshi wayar ya mata wani irin kallo ya juya ya fita ta bi sa da ido hawaye na sauka idonta, Yana fita dakin ya ji ya ma kasa daukan kiran, ganin ya kusa katsewa ya daga a hankali ya kai kunne amma ya kasa cewa komai, Daddy yace "Are you there Imaan?" Mujaheed yyi kasa da kai yace "Ina kwana Abba" Daddy yace "Lafiya lau Muhd, ya ku ke" Mujaheed yace "Alhmdllh" Daddy yace "But why did you take her with you without informing anybody Muhd?" Mujaheed ya d'an yi shiru sannan a hankali yace "Ku yi hakuri Abba, amma nobody will let me go with her..." Daddy yace "Ita kuma dayar matar taka fa? Kar ku shiga hakkinta, you know what is right from wrong..." Mujaheed na sauka stairs murya can kasa yace "In sha Allah xata dawo yau Abba" Daddy yace "Toh maa sha Allah, ba sai kun dawo anytime soon ba, Allah ya ba ku xaman lafiya..." Mujaheed yyi murmushi yace "Toh Ameen nagode Abba...." Daddy yace "Tace kuna Zaria koh?" Mujaheed yace "Ehh" Daddy yace "To maa sha Allah, hope there is no problem?" yace "Sure Abba" Daddy yace "And what about ur work?" yace "Xan dinga tahowa daga nan din, I took two weeks leave..." Shiru Daddy yyi kafin yace "But I don't like that, wajen yyi nisa" Mujaheed yace "Sati uku kawai xa mu yi nan Zaria" Daddy yace "Ohk that's better Allah ya kai mu, if you have any problem you let me know" Mujaheed yace "In sha Allah" daga haka Daddy yyi masa sallama ya katse wayar. Mujaheed ya xauna saman kujera ya lumshe ido hoping everybody will accept the marriage that way, footsteps da ya ji sama ya sa ya daga kai ya kalleta, ya bude daya daga ledojin da ya shigo dasu yace "Breakfast" Ko kallonsa bata yi ba fuska daure, ya mike ya wuce sama yana rike da wayarsa ya bar ta tsaye a parlon. Abba ne xaune parlon Inna sae Daddy da Mama Hadiza, Inna na xaune saman tabarma tayi tagumi ido duk ya kumbura ta fashe da wani sabon kuka tace "Ni dai tunda uwata ta haifeni ban taba ganin tantiri irin Mujaheed ba, me nayi masa a rayuwa banda kyautatawa da bautar da nayi da shi da xai saka min da sharri?? Me na masa xai sa in kasa bacci jiya na je tolet ya fi sau hamsin, sannan na kwana kan darduma sbda tashin hankali, wai ashe shi ya shigo ba tsoron Allah ya dauke min jika ya gudu, to wai ma a kan me xai dauketa yarinya nace bata isa aure ba, me xai je yyi da yar mutane? a gaskiya duk inda ya tafi da ita a je a dawo min da jika ba ruwana, ko kuma ni a min kwatancen wajen in tafi da kai na in daukota, ita Imaan din har nawa take xai gudu da ita sbda ya lalace, kaiii Ahmadu baka yi sa'a ba gaskiya, ban ta6a ganin tantiri irin Mujaheed ba, shiryawa xan yi yanxu a kai ni gidansa ya ga barbadin bala'i sannan in juyo tare da Imaan tunda ba uban wani ya haifa ma Bukar ita ba" tana fadin haka ta mike xata shige daki ta dauko mayafi, Mama Hadiza ta bi ta da kallo tace "Toh ai basa gidansa inna" Inna ta juyo da sauri tana kallonta tace "Basa gidansa? To ina ya kai ta?" Mama Hadiza tace "Sun dai yi waya amma bai fadi inda suke ba" Inna ta xauna kan kujera baki bude tace "Ya xa ayi ya ki fadin inda suke, ni kuma da suka bari nan fa???" Mama Hadiza ta saci kallon Daddy da ke ta kallon uwar tasu, da mamaki Inna da ta kasa rufe baki tace "Shi Mujaheed din mance wahalan da nayi masa yyi xai tafi da Imaan banda ni?" Bbu wanda dai ya tanka su cikinsu. Mujaheed ya gama gyara gidan gaba daya ya goge duk kuran ko ina ya dawo fess, ya kalli agogo dake nuna karfe sha daya saura ya wuce sama ya bude bedroom dinsa ya ga Imaan kwance tana bacci tun bayan da ta sha drugs da ya siyo mata bayan ya tilastata tayi breakfast take baccin, bathroom ya shiga ya sake yin wanka ya fito ya shirya cikin kananun kaya ya dau makullin motarsa ya juya yana kallonta, karasawa yyi gun gadon ya xauna gefenta ya dukar da fuskarsa dai dai nata, a hankali ta bude ido jin saukan numfashi a fuskarta, ya ja hancinta murya can kasa yace "I am going out now but I will be back soon lil sis" Ganin bacci ne sosai idonta yyi pecking goshinta ta lumshe ido bata ce masa komai ba, mikewa yyi ya fita dakin ya kulle mata kofa sannan ya fita ya kulle gidan ta waje ya hau motarsa ya bar gidan, hanyar kaduna ya dauka.... Direct Marafa ya nufa bayan ya shiga garin kaduna, yana isa gidansu Safeenah yyi parking a kofar gida ya fito daga cikin motar ya shiga cikin gidan, bbu kowa parlon sai Sajidah, daga sama har kasa ta kallesa ta ci gaba da danna wayarta, ya xauna saman kujera ba tare da ya sake kallonta ba ya ciro wayarsa ya kunna, sannan yyi dialing number Safeenah, tana dagawa yace "Ina parlor ki fito" Safeenah dake shiryawa ta fito wanka ta xaro ido tana kallon Uwarta dake waya, Safeenah ta dade bata ji farin cikin da take ji ba a lkcn, ta xauna gefen gado bayan ta sa kayan tana kallon Hajiyarsu dake waya tana cewa "Ehh dama shine abu na farko da nake son ayi mata, Ehh sunanta Rukayya, xa mu yi waya anjima" daga haka ta katse wayar, Safeenah ta xaro ido tace "Hajiya Mujaheed ne fa a parlor" Hajiyan Marafa tace "Mujaheed Kuma? To me ya xo yi??" Safeenah ta bata rai ta mike ta nufi gaban madubi ta feshe duk jikinta da turare sannan ta dau karamin gyale ta fita, tana shigowa parlor ganinsa a xaune ta nufesa da sauri ta fada jikinsa ta rungumesa gam, sai kuma ta fashe da kuka tace "I've missed you a lot Mujaheed, don Allah ka xo ne mu koma gidanmu mu ci gaba da xamanmu mu kadai??" Yace "Tafi ki hada kayan ki" ta xaro ido tace "Da gaske??" Yace "I am waiting" gaba daya su Hajiya Baturiya dama sun kwaso kayanta daga gidan Mujaheed bayan abinda ya faru, ta mike da sauri ta tafi daki tana kallon Uwarta tace "Mummy yace in hado kayana wllh" Hajiyan Marafa tace "Babu inda xa ki je sai an gama aikin da ake yi..." Safeenah ta fashe da kuka tace "Ni dai wlh Mummy ki Bari in bisa gida fa xa mu wuce ya ma saki yarinyar Ina ji, don Allah ki bar ni mu je" Hajiya Marafa tace "Cewa nayi ki bari sai an gama aikin da ake yi tukun, ke ana kokarin kwatar maki yan ci kin kasa ganewa sbda son miji" Safeenah tayi kamar xata yi kuka tace "Ni dai Hajiya tafiya xan yi daga karshe sai in dawo idan an gama aikin, amma ni kam da baku bata kudin ku ba ni kadai na isa Hajiya Rukayya a duniyar nan, wllh sai na rabata da d'anta, Auren ma da aka masa Ina jin babu shi yanxu" daga haka ta fita xuwa dakinta ta hau hada kayanta a jaka, cikin few minutes ta gama ta jawo jakar downstairs, Mujaheed ya dinga kallonta har ta iso parlon, Sajida ta dinga mata wani kallo tana girgixa kafa, Mujaheed yace "Hajiya fa?" Safeenah ta koma sama da sauri ta shiga dakin uwarta tana murmushi tace "Hajiya wai ki fito ku gaisa" Hajiya Marafa tace "Bai kai wannan matsayin ba, banda ma kin nace ina mu Ina hada xuri'a da Rukayya? Waye bae san Rukayya da abinda take yi ba, in sha Allahu ta ja ma kanta abinda ba shikenan ba tunda har ni tayi ma haka, xan kuma nuna mata mu bama xama da kishiya, Ana gama aikin da ake dama xan tako gidan da kai na" juyawa Safeenah tayi ta fita dakin tana cewa "Bayan nace maki babu auren yanxu wace kishiya kuma, ai sai dai mu gwada mata hankali kawai..." Tana dawowa parlor ta kalli Mujaheed tace "She's in the bathroom mu je kawai dear" mikewa yyi ya nufi kofar fita ta bi bayansa tana kallon Sajida tace "Sai mun yi waya Aunty Sajida" ko kallonta Sajida bata yi ba har ta fita, sai da suka shiga mota Mujaheed yace "Zaria xa mu je" Safeenah ta xaro ido cike da farin ciki tace "Ae ya fi dear nah, gwara mu yi nisa da gida kawai, after some months sai mu dawo kaga bbu wanda xai kara tada wani maganar, wllh hakan ya fi, har naji hankali na ya kwanta sweetheart" shi dai bai ce mata komai ba ya tada motarsa don duk hankalinsa yyi kan Imaan da ya bari tana bacci....
*Imaan isn't for free* it's 300 via
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788
84....
_And I dedicate this particular page to the entire members of_ *Murmushin Novels* group....
I Khaleesat Haiydar is wholeheartedly saying a big fat *Thank you* to the entire members of the above👆🏻 named group... nagode nagode, Allah ya bar kaunar, I really appreciate it sisters, Allah ubangiji ya kara maku budi da daukaka, ya bar xumuncin mu, ya sa ku gama da duniya da iyaye lafiya, Allah ya saka da alkhairi, Billah Ina yin ku har raina, sannan.... _Inna na gaisuwa tace sai kun xo mata kwalema da share share a fitar da duk dattin da suka makale mata kada su cuceta, sannan tace in maku tuni da tsoron Allah a duk inda xa ku kasance duba da yanda duniyar ta lalace yanxu mutane ba tsoron Allah, domin kuwa lkcnsu tsoron Allah ake kaca kaca ba wasa, don haka ku ji tsoron Allah a duk inda xa ku kasance, sannan ku xamo masu tsafta domin sace xuciyoyin masu house_... Lol, gaskiya I am happy da abinda ku ka min jiya, I love u all... 😍🥰❤️
And my lovely fans that partronized my book happily without thinking twice, ku ma ina yin ku har raina wllh, Ina son ku, _Inna tace kuma tana gaishe ku, kuma ku rike Allah, to wa gare ku da xa ku rike dama banda Allahn? Sannan ayi ta ma iyaye biyayya domin a rabu lafiya da su kamar yanda Ahmadu da Bukar ke mata biyayya..._ lol
Mujaheed na gama parking a compound ya kashe motar ya bude ya fito, gate ya tafi ya kulle ya dawo, Safeenah da ta fito motar tana mika ta sauke ajiyar xuciya tace "Har hankalina ya kwanta dear, i prefer here than kaduna unlike kwanaki da muka xo naji duk ban son garin, yanxu kam I like it here..." Shi dai bai ce mata komai ba ya nufi entrance din gidan rike da takeaways din da yyi a hanya, tace "But wait, foodstuffs din fa Dear, ka bar su a booth, my bag is there also..." ba tare da ya juyo ba yace "we will take them in later..." Bin bayansa tayi suka shiga gidan, ya xauna saman kujera bayan ya ajiye ledojin abincin hannunsa ya jinginar da kansa da kujeran don duk ya gaji sosai, ko kadan shi dama bai son driving me nisa, Safeenah na murmushi ta tsaya bayan kujeran tana massaging shoulders dinsa a hankali tace "Bari in je sama in hada maka ruwan wanka baby, nasan ka gaji, shi sa nace ka bani driving din inyi ka ki...." Shi dai bai ce komai ba yana sauraronta, tana gama fadin haka ta cire mayafinta ta ajiye saman kujera xata wuce sama ya bi ta da kallo yace "A'a kar ki damu baxan yi wanka ba yanxu" ta juyo tana kallonsa tace "Oh really, amma idan kayi ai xaka fi samun relieve ae dear, anyway mu je sama in maka tausa toh" cike da shagwaba ta fadi hakan, bai ko kalleta ba ya mike ya dau ledan abinci daya yace "Ni fa I am okay, I just need rest...." Ta langwabar da kai tace "To mu je ka kwanta my dear...." Bai ce komai ba ya nufi stairs, jin tana biye da shi ya tsaya a staircase din sannan ya juya yana kallonta yace "Tot you said you are hungry ga abinci can kuma kin bari downstairs" ta tabe baki tace "No apple din da na ci daxu a hanya ya isheni, nima hutawa xan yi, all my body is just aching" Bai ce komai ba ya ci gaba da tafiya tana biye da shi har suka isa corridor din dakuna hudun dake jere, tsayawa yyi dai dai kofar dakin da yake amfani da, ya d'an saci kallonta ganin dakin ta nufo yace "You use the other room Safeenah" Da mamaki take kallonsa, sai kuma tace "Why? Beside tunda muke xuwa gidan nan na taba amfani da wani dakin banda wannan da muke using tare? Baka taba ce min inyi amfani da wani daki ba ai" Ya juya yana kallonta da kyau yace "Ohk we are not sharing it this time around, you choose from any of the other rooms, this is a master bedroom" wani kallo Safeenah ta dinga yi masa daga sama har kasa, can tace "What's wrong with you Mujaheed, why are u behaving this way?? dama mun ta6a raba daki tunda muka yi aure da kai? Ko kuma wani sabon walakancin ka tsiro?" Ya shafa kansa murya can kasa yace "Plss Safeenah I am tired bana son magana, I told u I need rest, idan baxa ki shiga any of the rooms ba ki koma parlor" yana fadin haka ya shige dakin ya sa makulli, Safeenah ta wani xaro ido tana kallon kofar da mugun mamaki, ta fi minti daya tsaye tana tunanin wannan kuma wani sabon walakancin Mujaheed ya kirkiro mata? Tabdi ai ko wahala kawai xai daukar ma kansa don maganin sa xata yi ba na wasa ba, da wannan tunanin ta sauka downstairs a fusace xuciyarta na tafarfasa, don sosai ranta ya baci... Mujaheed ya ajiye ledan hannunsa yana kallon Imaan dake bacci har lkcn, takawa yyi ya isa kusa da ita ya xauna gefenta, a hankali ya kai hannu forehead dinta ya ji temperature dinta normal, Bude lumsassun idonta tayi tana kallonsa, sai kuma ta dauke kai a hankali ta matsa daga kusa da shi ta juya masa baya, yace "Kinyi sllh?" Kin basa amsa tayi ta turo baki, idonsa ya sauka kan darduman da ke shimfide dakin alamar tayi sllhn, yace "Tashi ki ci abinci" ta hade rai tace "Ni baxan ci ba" yace "Koh??" K'in cewa komai tayi, ya sa hannu ya daga ta, ko ba a fada masa ba yasan next reaction dinta hakan ya sa ya maxa ya juyo ta ya rufe bakinta ya hade rai sosai yana kallonta, ta 6ata fuska kamar xata yi kuka cikin sanyin murya tace "Ni dai ka maida ni gun Ammina" Mikewa yyi ya dagota ya dawo da ita kasa kan darduman da ta bari a shimfide fuska daure yace "Ga abinci nan ki dauka ki ci" ganin kallon da yake mata ta jawo ledan a hankali hawaye na taruwa idonta ta bude ta ciro take away din shinkafa da kazar da ya siyo mata sai table water da five alive drink, spoon ta dauka ta debi shinkafar ta fara ci a hankali, shi dai kallonta kawai yake ko kiftawa babu, can yyi murmushi ya tafi kan gado ya kwanta hade da lumshe idanuwansa, bayan kusan minti biyar ya bude ido to see if she is eating the food, kazan abincin ya ga ta dauka tana ci as if her happiness depend on it don ba cin wasa take ma kazan ba, suna hada ido ta juya da sauri bayan ta cire naman a baki, murmushi Mujaheed yyi ya mike xaune ganin ta ajiye kazan yace "Wa kika ajiye ma?" Ta turo baki tace "Ni baxan ci ba" kallon bakin da take turo masa kawai yake.... Inna ce xaune kan kujera a parlonta tana saka gogaggun kayanta a sabon Ghana must go din da ta sa Mai gadi ya siyo mata aka bude kofa hade da sallama, Daga kai tayi tana amsa sallaman ta ajiye set din riga da xanin hannunta tace "Sannu da