Showing 279001 words to 282000 words out of 303099 words

Chapter 94 - Imaan Book 1 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

1643

fita dakin dai dai lkcn da shi ma ya fito parlonsa, ta sunkuyar da kai yace "Go and sleep I will check" Bata ce masa komai ba ya fita ta bi bayansa, tsaye ta gansa yana lekan balcony din through window, ganin ya ki matsawa daga jikin window din ta karasa downstairs har ta iso bayansa dai dai lkcn da ya sake curtain din xai juyo suka kusa cin karo jawota yyi jikinta, tayi lamo, murya can kasa tace "Waye?" Yace "I think it's not necessary...." Sosai gabanta ya fadi jin abinda yace ta daga kai tana kallonsa, ya ja ta xa su bar parlon. Ta fixge hannunta tace "Who is it plss?" Shiru yayi yana kallonta kafin yace "Kishiyar ki" ta buda ido tana kallonsa gabanta na faduwa, lkci daya ta juya ta wuce sama ya bi ta da kallo yana murmushi sannan ya kara kallon kofar da aka fara bubbuga da karfi maimakon bell da ake dannawa, ya koma gun kofar ya tsaya yace "Who is that?" Da karfi tace "Ubanka ne, nace ubanka ne..." dariya yyi yace "Toh kya kara tsufa a inda kike tsaye kuwa, kawai da sassafe mutane basu tashi ba ki taho masu gida, ke haka ake yi a garin ku?"



*Imaan isn't for free* it's 300 via


Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788


*Albishirinku 'yan uwa*

Shin ko kun San zaku iya magance mafi yawan cututtukan da suka addabi al'umma yanzu cikin sauki?
Sinadarin _Stemcell total care_ yayi fice wajen magance matsalolin diabetes, BP, asthma, sickler, cancer, stroke, rashin haihuwa, fibroid, infection da duk wata matsala da ta danganci lafiyar Al'umma.
Ba wannan kadai ba, akwai coffee na double root Wanda ke inganta duk wani abu da ya shafi rayuwar aure ga maza da Mata, inganta qwayoyin haihuwa da dai sauransu.
Akwai sinadarin rage tumbi da dai sauransu.

*Domin neman qarin bayani ku tuntubi wannan lambar 07068136856*
Sai an gwada akan san na kwarai.






100...






A fusace inna tace "Ni dai duk wanda ya walakanta ni kansa ya walakanta duniya da lahira, don ba banxa nake ba, ta yaya xa a barni a gantale bakin shegen kofa daga xuwa abun arxiki?" Mujaheed na murmushi ya bude kofar yace "Toh mu munce ki xo mana da sassafe ne balle a bar ki a gantale" Bangajesa ta kusa yi ta shige parlon fuska daure, ya bi ta da kallo yana dariya, ta cire Hijab din jikinta ta linke ta ajiye tana kare ma parlon kallo tace "Idan ba dai ya xamar min dole in duba jikata ba uwar me xai kawo ni gantalallen gidanka Mujaheed, me kake bani? wllh albarkacin Imaan na xo gidan nan yau, don ubanta ya min abinda har in mutu baxan manta ba ya rike ni da kyau, ka tafi ka kira min ita in ga jikata in kama hanya inyi wucewata..." Ya dawo kusa da ita ya xauna yana murmushi yace "Oh ni ba jikan ki bane?" Ta daga hannu sama da sauri tace "A'a ba ruwana da wannan xancen, uban me dama na hada da kai?" Ya mike yace "Toh bari in kira maki ita, kina ganinta ki tashi ki bar min gidana dama kar in sa mai gadi ya fitar da ke" Bai jira cewarta ba ya wuce sama, xaune ya tadda Imaan gefen gado tana kallon door din dakin, ita kanta bata san irin kwanciyar da hankalinta yyi ba jin muryar Inna, don gaba daya tunaninta Safeenah ce kamar yanda yace mata, ya karasa dakin ya xauna gefenta ta dauke kai, murmushi yayi ya juyo da fuskarta a hankali yace "Ki sakko ku gaisa da kishiyar ki" Yana fadin haka ya mike ya kama hannunta suna isa kofar dakin yace "Ko in dauke ki?" Ta hade rai tace "Saboda me?" Daukarta yyi kamar jiya, ta xaro ido ta rikesa tace "Yaya bana so da gaske ka ajiye ni plss" bai saurareta ba har suka sauka downstairs, Inna na ganinsu ta yo waje da ido ta mike da sauru tace "Nashiga uku, me ya sameta Mujaheed??" Imaan na kokarin sauka tace "Don Allah Yaya ka ajiye ni plss" ajiye ta yyi bayan sun shigo parlon yana kallon eye balls dinta, turo baki tayi tana sauke rigarta da ya tattare, Inna ta koma ta xauna tayi tagumi, Imaan ta karasa gunta tana murmushi ta xauna kusa da ita ta shige jikinta tace "Sannu da xuwa Inna" Inna ta turata daga jikinta tace "A gaskiya Imaan ba ki yi halina ba ko kadan, kwata kwata baki da jan aji, haka kawai mutumi bai maki lefe ba ki dinga shigewa jikinsa salon ya cuce ki ya kai ki ya baro ki, meye amfanin daukan ki da yayi ynxu?" Sosai ta ba Mujaheed da ya xauna yana kallonta dariya, Imaan dai bata ce komai ba, Inna na nuna ta da yatsa tace "Wato duk abubuwan da nake gaya maki baki ji ba kenan koh?" Imaan ta turo baki tace "Ni nace maki ban ji ba?" Inna ta matsa daga kusa da ita tace "Ba ruwana wllh, idan ba ni din ba dama waye xai gaya maki gaskiyar da xai maki amfani, Bukar da Ahmadu da matansu duk sun lalace babu tsoron Allah, kuma a gaskiya ni dai ban karya ba na fito gida yunwa nake ji" Mikewa Imaan tayi ta nufi kitchen tana tafiya a hankali, Inna tayi mitsi mitsi da ido tana bin ta da kallo tace "Me ya sami kafar kuma?" Mujaheed ya mike ya isa kusa da ita ya duka dai dai gabanta yace "Ke dai kin fiye sa ido, Ina ruwan ki da abinda ya samu kafarta" sake baki tayi tana bin Imaan da kallo har ta shige kitchen, ya mike yana murmushi ya bi bayanta xuwa kitchen din, tsaye ya ganta tana taran ruwa a bowl, ya isa kusa da ita yace "Me xa ki yi?" Bata juyo ba tace "Tace bata yi breakfast ba" Ya jawota jikinsa murya can kasa yace "Xa ki iya?" Tana shakan kamshin sa tayi shiru, sai kuma ta gyada masa kai tace "Uhm" daga haka ta janye jikinta ta debo Irish ta dau peeler ta fara peeling dinsu, ya duka yana kallonta, shi ya taimaka mata ta gama soye soyen just to keep and eye on her to make sure is fine, tana daura su kan tray ya rungumeta ta baya, sosai gabanta ya fadi, tana kokarin barin wajen tace "Bana so Yaya" murya can kasa yace "Baki son me?" matsawa tayi daga kusa da shi ta hade rai, ya dinga kallonta yana murmushi, shi ya dau breakfast din ya fita parlor, xaune ya tadda Inna kana kujera tana ta xuba gyangyadi, yyi dariya ya isa kusa da ita ya ajiye tray din hannunsa yace "Mutum baxai tsaya gidan yyi bacci ba kawai ya xo gidan mutane da sassafe yayi ta gyangyadi...." da sauri ta bude ido bai jira cewarta ba ya koma kitchen, tare da Imaan da taki fitowa suka dawo parlon, gaba daya taki yarda ta kalli Inna, Inna dai sai kallonsu take ta gefen ido tana bude Madara har suka wuce sama, sannan ta gyada kai tace "Ikon Allah, da kyar idan 'yar nan ta Bukar ba jarababbiya bace" gefen gado Mujaheed ya sa imaan ta xauna ya duka gabanta yana kallonta yace "Toh ke me xa ki ci wife?" Ta dauke kai tace "Sai anjima" ya mike yace "Ohk Ina xuwa" fita yayi dakin ta bi sa da kallo, ba a dau lkci ba ya dawo da laptop dinsa da waya ya xauna gefenta ya jawota jikinsa yace "Hope ba ki jin ciwo ko Ina yanxu?" Kai kawai ta gyada masa, ya ci gaba da abinda yake a laptop din idonta na kan laptop din, sun fi 20 mins a haka wayarsa ya fara ring, a tare suka kalli wayar, Sunan Safeenah ne ya fito a screen din, imaan ta dinga kallon wayar bbu ko kiftawa, shi kansa Mujaheed kallon wayar yake, can yyi silencing kiran ya maida idonsa kan laptop, kira ya fi uku ya shigo wayarsa na Safeenah bayan first kiran, daga karshe ya kife wayar Mujaheed still operating his laptop, can kuma ya mike ya dau laptop din da wayarsa yana kallon Imaan da ta yi kwanciyar ta yace "Bari in tafi wajen Inna" Bata ce komai ba ya nufi kofa ya fita, mikewa xaune tayi ta bi sa da kallo haka nan taji gabanta na faduwa, Yana fita da kusan minti goma sai ga Inna ta shigo dakin ta rike ha6a tace "Shi Mujaheed din yace maki kar ku sakko kasa ku barni ni daya a parlor kamar shegiyar mayya?" Imaan tace "Ba ya sauka ba shi inna" cike da masifa Inna tace "Ya sauka ina? Ni kadai raina a parlor kamar tsohuwar mayya, dama wllh sai da Ahmadu yace kada in je naki ji to gashi dai an walakanta masu ni, dama abinda ya guda kenan ni ce bana jin magana" Imaan ta sauko saman gadon ta marairaice tace "Inna ni fa kaina ne ke ciwo shi sa na xo na kwanta, wllh na xata Yaya yana parlor" Inna ta kulle kofar ta karaso kan gadon murya can kasa tace "Amma dai duk abubuwan da na gaya maki a gida kina aiki da su kuwa Imaan??" Imaan tace "Na me kenan?" Inna tace "A dakin nan Mujaheed ke kwana?" Imaan bata san lkcn da tayi murmushi ba ta girgixa kai tace "Aa ba nan yake kwana ba" Inna tace "Toh kar ki kuskura sai kin ga akwatuna kin ji?" Imaan tace "Toh" Inna tace "Atoh, ko min dadin bakin da xai maki kuwa" Imaan ta gyada mata kai tana murmushi, Inna tace "Kuma kina dai cin abinci koh naga duk kin fige?" Imaan tace "Ehh Ina ci" Bude kofar dakin aka yi Mujaheed ya shigo, Inna tace "Toh Ahmadu dai yace kada in dade, haka kawai kada in bata ran d'a na, bari in je Imaan, in sha Allahu jibi xan xo..." A hankali Imaan tace "Inna ki bari da yamma mana" Inna tace "A'a haka kawai, wa gareni da xai gaya min gaskiya banda Ahmadun, ga Bukar ya xama abinda ya xama" daga haka ta nufi kofa Imaan ta mike ta ki yarda ta kalli Mujaheed dake kallonsu ta bi bayan Inna. Murmushi Mujaheed yyi ya bi bayansu yace "Toh ni ne baxa ki ma sallama ba Inna?" Inna na sauka stairs tayi kamar bata ji sa ba Imaan na biye da ita, tsaye ya gansu balcony Inna na mata magana kasa kasa, tana ganinsa tayi shiru ta fara tafiya tana cewa "Toh ni na tafi Imaan, Allah ubangiji yyi maki albarka, ai kin cika min ciki...." dariya ta basa sosai ya bi ta ya kamo hannunta yace "Toh mu je in ajiye ki a gida inna sai nima ki sa min albarkan" ta tabe baki bata dai ce komai ba, imaan dai na tsaye har ya bude mata back seat, Inna ta kalli Imaan tace "Fatan dai duk kin ji abubuwan da na gaya maki koh?" Imaan ta gyada mata kai a hankali, Mujaheed yace "Dauko Hijab dinki mu je mu yi dropping dinta" yi tayi kamar bata ji sa ba ta juya ta koma ciki, tana tsaye parlor har ta ji fitar motarsa a compound din, sai da taji Mai gadi ya kulle gate sannan ta wuce sama ta shiga parlonsa da sauri, tun da suka xo gidan ranan ne ta fara shiga parlon, duk iya dubanta bata ga wayarsa ba, hakan yasa ta karasa cikin bedroom dinsa, daddadan kamshi ke tashi dakin nasa dake very neat, ta nufi saman gado ganin wayarsa ta dauka ta bude, call logs ta shiga, sosai gabanta ya fadi tana kallon kiran safeenah da yayi picking, ta shiga details don duba minutes din kiran aka bude kofar dakin, da sauri ta juya xuciyarta na bugawa, kallonta ya tsaya yi sannan ya mika mata hannu alamar ta basa wayar, sauke kanta tayi kasa bata motsa daga inda take ba, ya karasa ya karbi wayar a hannunta sannan ya juya ya fita, Bata san lkcn da ta durkusa kasan dakin ba ta hade kai da gwiwa sai dai taji kukan ma ya ki xuwa, ta fi minti goma a haka sannan ta mike da kyar ta fita dakin ta koma nata, xaunawa tayi gefen gado har sannan xuciyarta na bugawa. Imaan na tsaye kitchen tana wanke abubuwan da ta 6ata wajen hada ma inna breakfast ta ji shigowar motar mujaheed gidan, Bata fito kitchen din ba sai da ta gama tsaftace ko ina sannan, xaune ta samesa parlor ya jinginar da kansa da kujera, ya bi ta da kallo yace "Aunty na gaishe ki" tace "Ohkk" sannan ta wuce sama, tsaf ta gyara dakinta ta canxa bedsheet ta kunna turaren wuta dama tun da tayi wanka ta wanke bandakin sama sama, duk da yunwar da ta fara ji sosai bata yadda ta sauka parlor ba tayi kwanciyarta tayi lamo gaba daya taji hankalinta ya ki kwanciya, Bude kofar dakin aka yi ta rufe ido da sauri kamar mai bacci, ya kulle kofar ya karaso kusa da ita ya xauna gefenta ya kai fuskarsa dai dai nata yace "Kin ma yi breakfast din kuwa Imaan?" Tana kokarin juya masa baya har lkcn idonta a rufe tace "Uhm" dagota yyi ta bude ido fuska daure tace "Bana son haka..." Bai bari ta rufe baki ba ya hade bakinsa da nata, Turasa ta dinga yi amma ya ki sakinta, ya rungumeta sosai yana kissing duk jikinta, ta fara girgixa masa kai kamar xata yi kuka tace "Yaya stop plss" ko sauraranta bai yi ba yana bin ta a hankali kuma a nutse, sun dau lkci me tsaho a haka ganin gaba daya ta sakar masa jiki ya bude lumsassun idonsa a hankali yana kallonta, ita ma idonta a rufe suke yyi murmushi ya ja hancinta a hankali yana shafa fuskarta yace "Imaan" turo baki tayi ta juya masa baya ba tare da ta bude idon ba, ya mike xaune ya dagota ya rungumeta murya can kasa yace "What are taking for breakfast?" Bata ce komai ba kuma bata bude idon ba, ya mayar da ita ya kwanta yana murmushi ya mike ya fita dakin, sai a sannan ta bude idonta a hankali. Har bacci ya fara dauketa Mujaheed ya dawo dakin da take away din rice and stew ya ajiye abincin ya hau saman gadon ya kai fuskarta yace "Imaan" Bude ido tayi da sauri suna hada ido ta kauda kai ta mike xaune yace "Ga abinci ki ci, I am going to mosque now" ta gyada masa kai ya mike ya fita, tana jin ya shiga dakinsa ta kalli agogo taga sha biyu ya wuce, mikewa tayi ta wuce bathroom, ta hada ruwan xafi sosai tayi wanka sannan ta dauro alwala ta fito, tana ta xaune kan darduma bayan ta idar da sllh, ga abincin da ya ajiye mata bata ko bude ba, ya shigo dakin sanye da kananun kaya yana kallon ledan takeaway din yace "But I told you to eat first Imaan" ta jawo abincin tace "Yanxu xan ci" ya xauna gefen gado yana kallonta yace "Did you take ur bath?" Ta girgixa masa kai ba tare da ta kallesa ba ta bude abincin ta fara ci, ya mike yace "idan kin gama you come downstairs" ta gyada masa kai ya fita dakin, tana gama cin abincin ta mike ta fita da take away din xuwa parlor, tv kadai ke aiki parlon ta karasa kitchen ta ajiye ledan hannunta ta fito, wayarsa dake kan kujera ya fara ring ta karasa da sauri tana kallon screen din ta ga Safeenah, still tayi ta kasa daina kallon phone din, jin ya bude kofa upstairs ta tafi bayan kujera da sauri ta durkusa har ya sakko parlon ya dau wayar yana duba screen din sannan ya daga ya kai kunne, daga daya bangaren cikin sanyin murya Safeenah tace "I've been waiting kuma baka kira ba Mujaheed" Mujaheed ya d'an kalli sama sannan yace "I said later not now Safeenah" cikin rawar murya Safeenah tace "Don Allah ka kira Mujaheed I am waiting" yyi shiru kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Ohk let chat" Safeenah tace "Nooo don kira nake so" Yace "Alryt, I will call later when am outside" mikewa imaan tayi daga inda take ta wuce sama ba tare da ta kallesa, bin ta yyi da kallo da mugun mamaki har ta haura sama, ya katse wayar ya ajiye saman kujera. Imaan na shiga daki ta sa makulli ta cire ta ajiye gaban mirror ta xauna gefen gado, wasu hawaye ne suka dinga sakko mata ba tare da ta sani ba kawai jin saukansu tayi, lkci daya ta fashe da kuka a hankali ta kife kanta da pillow tana jin xuciyarta na mata xafi, murda kofar dakin taji yyi ta mike xaune da sauri tana goge idonta, yace "Imaan" tace "Na'am" yace "Open the door" tace "I want to take my bath" shiru ya d'an yi sai kuma a hankali yace "Ohk" komawa tayi ta kwanta, har dare bata fito daga dakin ba, bayan ta idar da sllhn Isha ta shiga bathroom tayi wanka ta fito dare da towel, ta gansa tsaye bakin kofar bathroom din, turo baki tayi xata koma ya rikota da sauri, kamar xata yi kuka ta duka tace "Wayyo Yaya ban sa kaya ba stop it" ya dagota yace "Why did you close the door?" Ta marairaice tace "Saboda Ina son in yi bacci, gashi har na tashi" kallonta ya dinga yi, ta turo baki xata juya ya fixge towel din jikinta, rungumesa tayi da sauri tana xaro ido tace "Nashiga uku Yaya" ya lumshe ido laying her down on the bed. Karfe dayan dare Imaan ta farka ta daga kanta a hankali tana kallon Mujaheed, xame jikinta tayi daga nasa ta sauka saman gadon ta dau hijab dinta ta saka ta nufi kofa a hnki ta bude tana kallonsa ganin bai motsa ba ta fita, parlonsa ta nufa ta bude kofar ta shiga ta kunna wuta tana


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login