Showing 264001 words to 267000 words out of 303099 words
kai tace "Saude ban san wani tuggun Hajiya marafa da tsinannun ya yanta xa su hada min ba nan ba da jimawa ba don nasan baxa su kyale xancen nan haka ba, ga uwar yaron nan da muka je har gida muka sameta ban san tsarin da ta xo tayi ma Inna da Hadiza ba, gashi har yanxu shiru Ahmadu bai ce min komai ba ko gaya masa ne basu yi ba oho, ya xan yi Saude? Wllh daren jiya ban rutsa ba kuma gaba daya na kasa tashi inyi sllh, yanxu haka xancen da nake maki tun safe bbu abinda na saka a ciki na sai ruwan da nake ta Sha, ga dukkan alama ma xaxxabi xan yi" Saude na matsar kwalla don ita ba ta Umma take ba ta kanta take tace "Wllh na ki me sauki ne Rukayya a kan nawa, iyaka fa idan an tada maki maganar uwar yaron ki rantse ki kuma rantsewa kiyi ta rantsewa kice baki je gidanta ba, rantsuwa ai ita ce kankat, sai a bar ki da mahaliccin ki a bar ki da rantsuwar ki kawai, ni dai ki tashi ki rakani gun bokan nan idan aure na ya mutu da sufyanu ai nawa ya kare a duniya, na shiga uku na lalace gidan uban wa xan tunkara ina marainiya da ni" Umma ta girgixa kai tace "Saude sai dai kije Balaraba ta raka ki gaskiya, don har abada ni da sake komawa gun bokan nan, saninsa bai amfana min komai a rayuwata ba, kullum ni kenan a gantale ban ta6a nasara na a xo a gani ba, meye amfanin raba auren da yayi aka aura ma d'a na?? Shegen mutumi kawai katon arne dama yasan bai san gaibu ba ya dinga amshe min kudi gashi daga karshe ya tarwatsa min rayuwa dubi irin matsalar da na tsunduma kai na fa yanxu???" Hajiya Saude ta mike tana kallonta tace "Lallai kin kasance butulu Rukayya, duk yanda na tsaya maki bamu gun wannan bokan ba mu gun wancan Malamin da walakancin da xa ki saka min kenan??" Umma ta mike tace "Don Allah Saude ki fita kiyi tafiyar ki nima a yanxu da kika gan ni wllh ta kaina nake matsalata ta fi naki wllh wllh..." Hajiya Saude tayi wani murmushi tace "Toh nagode kwarai Rukayya xan tafi, amma ki sani wllh kema sai kin girbe abinda kika shuka, duk ta'asa da barnar da kika dinga aikatawa xaki gansu a kwaryar ki kwanan nan, wannan da ya sameki shi ake ce ma wasa farin girki" daga haka Hajiya Saude ta fice daga dakin kamar xata tashi sama tana goge hawayenta. Daren ranan Imaan na parlon Inna xaune idonta a kan tv dake aiki sai dai bata san abinda ake yi ba gaba daya hankalinta baya tare da ita, Inna kuma tana can bakin tap tana aikin gurje gurjenta har ta gama ta shigo ta fara kakkabe kujerunta tana kallon Imaan tace "Ae yarinya jibi akwai fasa mugayen bama bamai xa ayi a gidan nan, iyaka dai bam din ya tarwatsa wa enda xai tarwatsa mu kuma muyi ta kanmu mu kara rike Allah, ke kuma Alhmdllh yanda wannan mutumi Mujaheed ya dauke ki haka ya maido min ke sbda tsayuwar dare da na dinga yi, abinda na nasani a nan gaskiya shine in har Mujaheed bai fita hakkin ki na aure ba wllh wllh babu inda xa ki bi sa, in su Ahmadu sun mutu to ni suma nayi, ba da ni xa ayi wannan ta6arar da abun kunyar ba, ko ya ta6a shigar maki daki ya kwana ne??" Imaan dai sai kallon tv take, Inna ta yi mata tsawa tace "Keee..." Da sauri Imaan ta juya ta kalleta, Inna tace "Toh wllh Bukar kika share ba ni ba, kwana biyu da baki gidan nan bakina tsit bbu shegen da ya sa ni magana, to dama wake sani maganan banda ke da Mujaheed din...." A fusace Imaan tace "Toh wai ni nasan da ni kike ne" Sai kuma ta rufe fuskarta da kujera ta fara kuka ta mike ta shige daki da sauri, Inna ta tabe baki tace "Toh ni ina ruwana idan ya kai ki ya baro ki, duk da baxan ma yadda hakan ya faru ba tunda ba ubansa ya halitto min ke ba, haka kawai ya same ki a banxa, to shi ne banxa ba ke ba" Imaan ta kwanta saman gado tana turo baki a hankali tace "Ko Ina ruwanta ma..." Bayan few minutes ta jawo wayar Inna dake saman gadon ta dinga kallon wayar sannan tayi dialing number din Mujaheed, sai da ya kusa katsewa ya daga kamar xata yi kuka tace "Yaya Ina ka tafi yau?" A hankali yace "Anjima xan dawo, where are you?" Tace "Ina part din Inna" d'an murmushi yayi yace "Are you missing me?" Da sauri tace "A'a fa, kawai naga ban ganka bane, kuma ban san ko ka ci abinci ba..." Yana murmushi yace "Toh xan shigo yanxu, me xan kawo maki?" Rufe fuska tayi a hankali tace "Kaza mana" Muryar inna taji tace "Yau naga jarababbiyar mata, shi Mujaheed din kika kira da katin wayata?? Toh gaskiya sai dai in bar ki da Allah don ba Mujaheed ya saka min katin ba, ba kuma uban Mujaheed ya saka min ba Bukar ne ya sa min kafin ya wuce, wannan wani irin jaraba ce ni patuu? Uwar me kika hada da Mujaheed din xa ki kira sa a wayata, ni dai na shiga uku da wahalar ki" imaan ta katse wayar ta jefar kan gado ta juya mata baya fuska daure, Inna ta dauke wayarta tace "Waye kuma Mujaheed da xaki kirasa da wayata muguwa kawai..." Daga haka ta fice daga dakin. Imaan na ta kwance daki taji an bude kofar parlon Inna, mikewa xaune tayi tana kallon kofar dakin.
*Imaan isn't for free* it's 300 via
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788
94.....
Mujaheed ya xauna parlon yana kallon Inna da ke juya furan gabanta tana kallon ledan hannunsa, yace "Ina yini" tana murmushi tace "Lafiya lau Mai gida, sannu da xuwa" Bai tanka ta ba, ta dau cup ta kusa cika masa da fura da nono ta mike ta basa tace "Dama saboda kai na dama furan nan" amsa yyi ya ajiye xata dau ledan da ya ajiye ya dauke da sauri yace "Ce maki aka yi ledan ki ne?" Tace "to sai nace maka ci xan yi Mujaheed? Haba sai kace gantalalliya kuma, duba abinda ke ciki kawai nayi" daga haka ta koma ta xauna fuska daure, Imaan ta tsaya bakin kofar daki tana kallonsu, Mujaheed ya kalleta bai dai ce komai ba ta fito ta dau ledan tana kallon Inna tace "Toh ni ina nawa furan?" Bata rufe baki ba Inna tace "Baxan bada ba" Dariya Mujaheed yyi ya dau nasa ya mika mata, ta kalli Inna tana murmushi ta amsa, mikewa inna tayi ta nufi kofa ta bude tace "Tashi ka fita ka ban waje Mujaheed..." Mikewa yyi yana kallo Imaan yace "I will call you with her phone...." Ta turo baki tace "She won't let that ai" Mujaheed yace "Hide the phone" shirun da suka ji inna tayi bata ci gaba da masifa ba yasa suka kalleta matsar kwalla suka ga tana yi, Mujaheed ya danne dariyarsa, Imaan ta ta6e baki ta dauke kai, cikin rawar murya inna tace "Dama banda 6are wa xai xage ka?" Mujaheed ya kalli Imaan yace "Don't forget to hide the phone" Imaan tace "Ohk I will do so" Mujaheed ya nufi kofa yana murmushi yace "Sae da safe inna" daga haka ya fita ta kulle kofarta ta sa makulli, Imaan xata shiga daki a fusace inna tace "Kada ki fara don ba uwarki Aisha bace mai min gyaran daki kije ki xubar min da kasusuwan kaji ki cuce ni" Imaan ta tabe baki ta dawo parlor ta ajiye ledan da cup din furan da Mujaheed ya bata ta tafi kitchen dauko plate kafin ta dawo inna ta dauke cup din furanta da sauri ta juye a bowl ta rufe tana cewa "Baxan bayar ba wllh" Har Sunday Imaan na part din Inna bata tafi bangarensu ba don haka kawai ita dai ta ji tana kunyar Amminta, har Inna ta gaji ta kyaleta kiran da Mujaheed ke mata ta wayarta iyaka tace masu idan katin ta ne to su da Allah. Karfe goma saura Imaan na parlon tana kallo Inna kuma na shan shayi Daddy ya shigo parlon, Mikewa Imaan tayi da sauri daga xaunen da take cike da farin cikin ganinsa sai dai kuma ta samu kanta da kasa xuwa ta rungumesa kamar yanda ta saba, murmushi yyi ganinta yace "Ba ku tafi ba Mamana?" Inna ta cafke tace "Ehh ni nace bbu inda xata, ba sadaka aka ba Mujaheed ba da xai ki yi mata lefe, in dai bbu lefe to baxata bar gidan nan ba Bukar, kai haka aka baka uwarta bbu lefe???" Daddy dai bai ce komai ba ya xauna saman kujera, Imaan ta duka ta gaishesa tana murmushi, yace "How are you doing?" Tace "Alhmdllh Daddy, ya hanya?" Yace "Alhmdllh" kallon inna yayi yace "Ina kwana?" Inna tace "Lafiya lau Bukar, Allah maka albarka" yace "Ameen, ya gida?" Tace "Toh ga gida dai mun gode Allah" yace "Toh ga ni na dawo Inna" Inna tace "Aa ba xance gaka ka dawo ba, ka tashi ka tafi ka huta kafin a neme ka kuma...." Shiru yayi yana kallonta can ya mike yace "Toh sai anjima" tace "Allah ya kai mu" Imaan ma tayi masa sai anjima ya fita parlon. Karfe sha biyu Mama Hadiza ta shigo parlon Inna dake ta xuba kamshin turaren wuta tare da mahaifiyar Sadeeq da Hajiya Salmah aminiyarta, Inna ta fito daki ganinsu ta washe baki tace "Toh Alhmdllh, sannun ku da xuwa" Hajiya Khadija ta xauna da kawarta sannan suka gaida Inna, inna ta amsa ta dauko masu ruwa ta ajiye tana kallon Mama Hadiza tace "Toh duk ki kirasu ta waya ai koh?" Mikewa Mama Hadiza tayi ta shiga daki, ba a dau lkci ba ta fito, Inna ta shimfida tabarma ta xauna Mama Hadiza ma ta nemi waje ta xauna, Aunty ce ta fara shigowa parlon sannan Ammi, duk suka dinga kallon mahaifiyar Sadeeq sannan aka gaisa, tun da Abba ya kira Umma yace ta tafi parlon Inna taji xuciyarta ya tsinke, wato sai yau xa ayi mata maganar da take tunanin babu shi jin shiru shiru, dakewa tayi ta sa Hijab ta fito xuwa part din Inna shawarar da Saude ta bata na mata ringing a kai, har dai ta iso parlon Inna fuskarta a daure, bata ta6a jin faduwar gaba irin yanda ta ji a moment din ba lkci daya jikinta ya mace ta kasa karasowa cikin parlon tana kallon Hajiya Khadija ko kiftawa babu, Inna na kallonta tace "Sannu da xuwa Rukayya shigo mana..." Umma ta kalli Inna sannan ta kalli Abba da Daddy dake parlon su ma, ganin Umma ta ki shigowa Inna tace "Haba Rukayya sai kace yarinya kin wani makale jikin kofa, ke fa ake jira tun daxu, don Allah ki rufa mana asiri ki shigo...." Lkci daya Umma ta kara daure fuska ta shiga parlon ta nemi gefe daya ta xauna tana kallon direction din kofa, Inna ta kalli Abba tace "Toh ko dai a kira Mujaheed ne, Ina son ayi komai kan idonsa" Daddy yace "A'a ba sai an kirasa ba" Inna tace "Tohh ai shikenan" Hajiya Khadija na kallon Umma da kyau tace "Kafin in fara magana Ina fatan kin gane ni dai Hajiya?" Umma ta kalleta a takaice tace "Ina fa xan gane ki? Jama'ah ai da yawa" Wani murmushi Hajiya Khadija tayi tace "Ehh dama ba lallai ki gane ni ba, kilan idan na fara magana a kan abinda ya kawo ni xa ki gane ni" Hajiya Khadija ta kalli Inna tace "Kaka wannan matar da kike gani kusan watanni biyu da suka wuce ta ta6a takowa har cikin gidana ta sameni da wani batu da xan fadi kowa ya ji yanxu" kallon Hajiya Khadija gaba daya occupant din parlon suka dinga yi with interest, Inna ma sai gwalo ido take tana sauraron Hajiya Khadija, Hajiya Khadija tace "Wannan mata ta sameni har gida tare da surkarta da kawarta, a kan maganar auren d'a na Sadeeq da 'yar gidan nan Imaan, a bakinta nake jin cewa Imaan sickler ce ba lafiyayya ba, har kudaden da mahaifinta ke kashe mata duk wata a kan ciwonta sai da ta fada min,.... Bana son inyi nisa don maganganun bbu dadin ji, bbu irin bacin da matar nan bata yi ma mahaifiyar yarinyar nan a gabana ba, babu kunya tace min in har na yarda d'a na ya aureta to fa xa su mallake min shi kamar yanda suka mallake mahaifin yarinyar, matar nan da ku ke gani ta fi minti ashirin tana magana na batanci a kan yarinyar nan Imaan da mahaifiyarta a parlona, munafukar kawarta na taya ta, daga karshe nace masu to nagode xan yi shawara a kan batun nasu, muka rabu da su a haka... abu biyu na gano tare da baiwar Allahn nan a lkcn, na farko Hassada... na biyu kuma kiyayya mai tsanani, na kuma ga alamar xata iya yin komai domin ta tarwatsa rayuwar imaan da mahaifiyarta, she can go to any extent doing that, kwata kwata bata tsoron Allah matar nan, muguwa ce, Ni kuma da na fi ta bayan sun bar gidana da few weeks na sa aka kai lefen Imaan, shine ganin bata samu nasara ta wajena ba ta shiga gun bokaye ta yi ma d'a na asirin da yasa yaji bai son auren kwata kwata, ta raba da sa imaan sbda son xuciyarta...." Gaba daya mutanen parlon kallon Umma suke babu ko kiftawa with shock, shi dai Daddy tunda ya kalleta sau daya bai sake kallonta ba ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, Ammi tayi murmushin karfin hali hawaye cike idonta tana girgixa kai, Mahaifiyar Sadeeq na kallon Umma da kyau tace "Ki saurareni da kyau, ke dai kin gan ni ne kawai amma baki san wacece ni ba, you know nothing about me, before going further don Allah Ina so ku tambayar min ita me Sadeeq yayi mata?" Bbu wanda ya iya cewa komai cikin parlon, Mama Hadiza ta dinga girgixa kai tana kallon Umma da ta tamke fuska tana kallon Maman Sadeeq, can Umma ta mike tana kallonta da kyau tace "Hajiya ni kika gani a gidan ki? Ni Rukayyar? Ni kuwa?? A Ina na san ki da har xan je gidan ki? Ni din?? Kinsan abinda kike cewa kuwa? Uban me xai kai ni gidanki da ban ma san hanyar gidan ba, to wllh wllh wllh karya take min Alhaji, na rantse ban san matar nan ba ban ta6a ganinta ba Allah shaida, wllh ban santa ba ban san me nayi mata take son 6ata min suna haka ba, innalillahi wa inna ilaihi raji'un..." Bude baki Hajiya Khadija tayi tana kallon Umma da mugun mamaki, Aunty tayi wani murmushi tana girgixa kai, umma ta fashe da matsanancin kuka tace "Idan na yarda da kazafin nan da sharri da kika biyoni har gida kika min Allah ya tsine min, wllh sai an bi min hakkina ko nawa ne xan kashe, wllh baxan yarda da wannan sharrin da bakin fenti da kika goga min ba" Inna ta hangame baki tana kallon Umma dake kuka sosai tana huci, Umma ta isa gaban maman Sadeeq cikin daga murya tace "Wllh wllh baxan yadda ba, ni Rukayyar ce naje gidan ki na 6ata imaan da uwarta?? To wllh tun a duniya xa a fara mana shari'a dake, ba Bulasawa ba in ma mai kudin duniya kike aure wllh sai an bi min hakkina, me na maki xaki 6ata ni haka gaban mijina, uwarsa da kanninsa?? Me na maki? A ina na ta6a sanin ki?" Wani murmushi kawai Hajiya Khadija take tace "Amma tunda nake ban taba ganin makira, annamimiya, makaryaciya, kuma warce bata tsoron Allah irin ki ba, ke shaidaniya ce a siffar mutum, ke din annoba ce a cikin jama'ah..." Bata rufe baki ba Umma ta nuna mata yatsa a goshi tana huci tace "Uwarki ce shaidaniya annoba ba ni ba" a hankali Hajiya Khadija ta mike tana kallonta tace "Ni ki nuna ma yatsa kika xagi uwata??" Umma na huci tace "An nuna maki din, kiyi abinda xa ki yi idan kin isa, haka kawai mata ki shigo min gida ki min wannan kafurin sharrin haka mai muni" murmushi kawai Hajiya Khadija tayi tace "First na bari ne ki gama rantse rantsen ki kafin inyi reminding din ki gidana akwai Cctv camera, sannan secondly sai kin san kin nuna min yatsa a goshi" Inna ta mike tana salati tace "Rukayya kin ja ma kanki babban bala'i da bamu san iyakarsa ba tunda kika daga rubabben shegen yatsan ki kika dunguri goshin wannan baiwar Allah, wllh kin debo ruwan dafa kan ki, bbu abinda ya sha kan Ahmadu balle ni...." Mikewa Abba yyi ya fita daga parlon, Umma na kallon Inna cike da masifa tace "In sha Allahu baxan ga bala'i ba, a kan me mata xata shigo har gidana ta min irin wannan kazafin inyi shiru? Wllh baxan yarda ba duk inda xa mu tafi sai dai mu tafi" Hajiya Khadija ta mike tace "Ki saurareni, sai na nuna maki ke a makiran ma karama ce, sai na nuna maki karshen ki tun a duniya, kuma sai kin san ba a cutar min da Sadeeq, da acuce sa gwara an cuceni" daga haka Hajiya Khadija ta fice daga parlon kawarta ta mike ta bi bayanta, inna ta saki shewa tana kallon Umma dake xufa tana huci tace "Anyi walkiya mun ganki axxaluma diyar shaidan, dama tun ba yau ba nasan mugun abinda kika aikata ma jikata ya dawo kanki aka aura ma d'an ki, d'an Albarka, Toh Alhmdllh ba a bakina aka ji wnn mummunan labarin ba, in kin cuce wani