Showing 228001 words to 231000 words out of 303099 words
magana ya fara fitowa koh, wllh ni dama nasan da kyar Sadeeq yyi ma jikata haka, yaro ne fa mai hankali da natsuwa, ubansa ma ga dattako da sanin ya kamata sannan ga kudinsa na halak, duk satan da ake a kasar nan ko biyar bai taba sata ba wllh inda ya burgeni kenan, komai nasa na halas ne babu Haram, gaskiya a duba lamarin nan a tausaya ma yaron nan, yanxu dai jiran dawowar ta Rasulu nake inji bayani a nan kuma xa a san ni tababbiya ce a gidan nan, kaff sai na tada gidan nan wllh idan abinda muke xargi gaskiya ne, kuma don Allah da Mujaheed na son auren nan xai gudu? Ni nasan yana can abun duniya ya ishesa baya son auren, ya kwantar da hankalinsa kawai da rai na babu me cutar sa yyi masa auren dole wllh, me xai ci da Imaan Allah na tuba" Mama Hadiza dai bata ce komai ba amma gaba daya kanta ya gama kullewa, bata ma san surutun da Inna take ba don tausayin Sadeeq ya dameta. Misalin karfe sha daya da rabi na dare Inna na kwance parlor sai sharar bacci take ga darduman ta da Hijab da carbi a gefenta tayi shirin tashi tayi sllhn dare anjima, kukan da Imaan ke yi tun bayan wucewar Sadeeq yasa taki kwanciya a dakin bayan tace mata aniyarta ta bi ta, shine tayi kwanciyar ta a parlor, murda kofar parlon aka yi a hankali ya shigo ya ya kulle kofar ya tsaya nan bakin kofa yana kallonta, bayan few seconds ya nufi bedroom dinta walking gently ya bude kofar yana kallon ciki, Imaan na kwance ta rufe har kanta da duvet sai dai ba bacci take ba, duk a xaton ta Inna ce ta bude kofar dakin hakan yasa ko motsi bata yi ba, murmushi yyi ya rungume hannunsa ya jingina da kofa yana kallonta ko kiftawa babu, a hankali ya rufe kofar dakin ya nufi kan gadon, Imaan ta bude ido sosai daga cikin Duvet din da take jin kamshin turaren da take ji....
*Imaan isn't for free* it's 300 via
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788
81.....
A hankali ya sa hannu ya sauke bargon daga saman kanta bayan ya xauna kusa da ita, ido hudu suka yi, ta mike xaune a mugun firgice ta xaro ido tana komawa baya da karfi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, innaaa" sai kuma ta fara kokarin sauka daga kan gadon ko ina na jikinta na 6ari, yyi hanxarin rikota ya maido da ita kusa da shi ganin xata kurma masa ihu ya hade ta da jikinsa ya sa hannu ya rufe bakinta, da karfinta ta dinga struggling din kwatar kanta hawaye na sakko mata amma ta kasa, gaba daya kuma ta ki yarda ta kallesa, shi kam sai kallonta yake daga karshe ya xame hannunsa bakinta ya rungumeta hade da lumshe ido murya can kasa yace "Imaaan..." Ta fashe da kuka sosai tana tura sa tace "Bana son haka yaya ni ka sake ni plsss, meye haka kke yi, ka sakeni bana soo....." Unexpectedly taji warm lips dinsa a kan neck dinta, ta wani xaro ido ta fasa ihu cike da shock tace "Wayyo Innaa....." Muryar Inna suka ji daga parlor cikin rikicewa take cewa "Kai amma gaskiya ban taba ganin shaidaniyar yarinya irin wannan 'ya dai ta Bukar ba, me na maki xaki gigitani haka fisabilillahi ina bacci Imaan? Me na maki?? To fito don ubanki ki tafi bangaren ku baxa ki kwanar min a nan ba wllh tllh, maxa fito min dakina, kuma ke da Allah tsorata ni da kika yi, gaskiya ke da Allah" Mujaheed ya saketa da sauri ya koma baya ganin tana jan numfashi da kyar, jinginar da ita yyi da gado yana kallonta yace "Hey relax now...." Kin yarda su hada ido tayi tana kokarin daidaita numfashinta, tashi yyi ya kunna fan din dakin ya dawo ya xauna ya dago kanta yace "I said relax..." Murda kofar dakin Inna tayi jin sa a rufe cike da masifa tace "Bude min dakina ki fito ki kama gaban ki ba ruwana, Allah ya saka min, daga yau kada ki sake yo min nan dama don koran kare xan maki muguwar yarinya kawai" Imaan dai sai sauke numfashi take hankali, lkci daya ta mike tsaye hawaye na sakko mata xata tafi gun kofar ta bude duk don ta samu ta gudu Mujaheed ya kamota ya mayar da ita kan gadon ta fashe da kuka jikinta na rawa tace "Inna kice masa ya bar ni in bude kofar" Inna dake tsaye har sannan ta wani xaro ido tace "Auzubillahi waye ya shiga dakin?? Waye ya shiga??" cikin rawar murya Imaan tace "Yayaa..." Inna ta d'an yi shiru kafin tace "Yaya? Waye kuma Yaya?" Imaan dai bata ce komai ba sai goge idonta take xuciyarta na bugawa tana komawa baya, Mujaheed ya kafeta da ido ko kiftawa baya yi yana kallonta, Inna tace "Shi Mujaheed din d'an iska ya xama xai tsallakeni a parlor ya shigar maki daki kina kwance? Ko wiwi ya sha daga inda ya taho??" Mujaheed ya mike yana murmushi ya shafa kansa ya nufi gun kofar ya bude, Imaan taji 6ata taba son k'in ganinsa irin na moment din nan ba, ko kallonsa bata son yi balle ta ji muryarsa, gaba daya ta ji ta tsane sa, Yana bude kofar Inna ta kallesa daga sama har kasa sannan ta kalli Imaan da ta takure waje daya tana hawaye tace "Ya kai minti nawa da shigo maki" Imaan taki cewa komai sai hawaye da shessheka, Inna ta kara kallon Mujaheed tace "Iskancin naka ya kai ka dinga biyo dare kana shigewa dakin mutane Mujaheed?? Toh dama neman ka ake ruwa a jallo, tunda dai ka gama guje gujen ka mara tushe sai mu tafi gun su Ahmadu ka rubuta ma jikata takarda ka mika ma ubanka da ya daura maku aure ya bata, don gaskiya Imaan bata isa aure ba, idan ma ta isa to a gaskiya ka fi karfinta, Ina xata kai lafcece irin ka? Ko baka ga yanda take bane, sannan wannan yaro Sadeeq dai ya dawo daxu ashe ba yin kansa bane.... Don haka mu je dama kai kadai ake jira" Mujaheed yyi wani murmushi yace "Ke ma xa ki iya rubuta takardan ki bata ai...." Inna tayi misti mitsi da ido ta tsaya kallonsa ko kiftawa babu, can kawai ta fice daga dakin, ya bi ta da ido har ta fita parlor gaba daya bayan ta cire makullin jikin kofar parlon, yana jinta ta sa makulli ta waje ya juya yana kallon Imaan, ganin ta mike xata shige toilet da gudu, yyi hanxarin cafkota ta kwala wani ihun jikinta na rawa tace "Na shiga uku don Allah Yaya ka bariii...." Ya ajiyeta saman gado ta ja duvet tana rufe jikinta tana kuka, yana kallon idanuwanta duk da ta ki yarda ta kallesa yace "Listen to me now..." Kin tsayawa waje daya tayi tana komawa baya tana kuka, ya wani hade rai yana kallonta yace "I said stay still now" da kyar ta xauna waje daya ganin ba da wasa yyi maganan ba amma ko da mistake taki kallonsa sai hawaye take xuciyarta na bugawa, ya dinga kallon lips dinta sannan a hankali cikin sanyin murya yace "isn't this our Destiny Imaan?" Sai a sannan ta kallesa da sauri, ta xaro ido cikin rudewa tana girgixa masa kai tace "Noo it's not plss, Yaya this not destiny, we are meant to be only brother and sister not husband and wife, this is not destiny plsss, kai yayana ne wllh, ni kuma kanwarka ce ko ka manta, bayan wannan babu wani alakar da ya dace da mu Yaya, wllh Yaya wannan abun kunya...." Bai jira ta kai karshen abinda xata fada ba ya bata shock of her life at that moment ta hanyar hade bakin sa da nata...... Iyakar rikicewa Imaan ta rikice a wnn lkcn don har daukewa numfashinta sai da ya kusa yi, don kansa ya kyaleta, amma fa shi ma ya kasa kallonta, murya can kasa yace "Am I still ur Yaya?" Shock bai bar ta ta iya basa amsa ba banda rawa babu abinda jikinta yake tana ja baya, dai dai nan kuma aka bude kofa a can parlor.... Inna ta shigo masu dakin tana kallonsu tace "Yana nan har yanxu Ahmadu" mikewa Mujaheed yyi ya saci kallon Imaan da har sannan ta kasa kwakkwaran motsi kuma taki cewa komai ya fita dakin ya ga Abba tsaye bakin kofa, Yyi kasa da kai kafin yace komai Abba yace "Where were you all this while??" A hankali Mujaheed yace "Ina nan Abba...." Abba yace "mu je to" Inna ta dau Hijab ta nufi kofar xata fita Abba yace "Ina kuma xa ki Inna" da mamaki tace "A'a ba magana xa ayi ba ya sakar min jika, Ahmadu na fa ce maka yaron ya xo mana da Hadia jiya yana ta kuka kamar xai mutu, nasan Hadiza ta gaya maka komai, wllh ba yin kansa bane kuma ko waye yyi masa haka xa mu binciko in sha Allahu kashin ko ma waye ya bushe...." Abba yace "A'a kiyi hakuri kiyi kwanciyar ki yanxu dare yyi, gobe da safe sai a xauna kowa da kowa ayi magana a nutse" Inna tace "A'a da yanxu da goben ai duk daya ne Ahmadu, ni dai gaskiya mu je ayi magana ayi ta ta kare yanxu, kada wani abu ya sami Imaan kaga auren nan ba sonsa take ba" Da kyar Abba ya lallaba Inna a bari gobe da safe ayi magana, shi dai Mujaheed na tsaye kansa a kasa amma gaba daya hankalinsa na kan abinda yyi Imaan, shi kansa bai yi xaton xai iya hakan ba, Bai san lkcn da yyi wani murmushi ba yana shafa kansa, muryar Inna ya ji tace "Kaga mahaukaciya ma ya mayar da ni, dariya yake min ko Ahmadu, to wllh sai ya sakar min jika tunda ba sonsa take ba baxa a mata dole ba" Abba yace "Allah ya kai mu goben" daga haka ya kalli Mujaheed yace "Mu je" Mujaheed ya kalli kofar dakinta sannan ya bi bayan Abba, slowly suke tafiyar yana gefen Abba, Abba yyi breaking silence din yace "You are not happy with what I did koh Muhd?" Mujaheed ya kallesa murya can kasa yace "Not at all Abba" Abba yace "Toh ina ka shiga kwana biyun nan" Mujaheed ya sunkuyar da kansa yana murmushi yace "Ina gidan a bachelor frnd of mine, bana son tashin hankalin gidan ne" Abba na gyada kai yace "Gaskiya ne, jiya Hadiza ta sameni ta min bayanin yanda suka yi da yaron nan Sadeeq, kasan Hadiza ba komai take ba ma listening ear ba, but tunda har ta sauraresa... sure da wani abu a kasa, Ur mum isn't still okay with this Union, grandma din ka har yanxu ba mu gane inda ta dosa ba gaskiya dama she has always been a confusionist, Hajiya Aisha bata gidan nan yanxu haka all because ita ma bata son auren, I caused all this Muhd, kai ma ban yi shawara da kai ba naji ra'ayin ka, so I think raba auren nan shi xai fi komai sauki a gidan nan" sauraronsa kawai Mujaheed yake kansa a kasa, Abba na gyada kai yace "Gobe da safe duk xa mu hadu, ita ma Aishar xa a kirata ta xo don a gabansu xa a yi komai...." Shi dai Mujaheed bai ce komai ba har suka isa apartment dinsu, Abba yace "You spend the night here sbda gobe da safe xa a kira meeting din" murya can kasa Mujaheed yace "In sha Allah" daga haka Abba ya wuce parlonsa, Mujaheed ya wuce sama walking gently. Daren ranan gaba daya bai yi baccin kirki ba, haka ma Imaan da kiss din da ya mata ne ya tsaya mata cak a rai, da ta tuna sai gabanta yyi mugun faduwa kuma sai ta mike xaune to calm her self down, ta goge bakinta ya fi a kirga amma har lkcn ji take kamar it's happening fresh, ko Sadeeq da yyi mata wanda ya fi wnn ma bata ji abinda take ji ba yanxu, da ta tuna Yaya ne yyi mata sai hankalinta ya kara tashi ta fara hawaye, anya yayan da ta sani ne wannan kuwa, har xuciyarta taji gaba daya tsoronsa ma take... Washegari misalin karfe tara na safe Ammi ta shigo gidan ta dalilin kiran Gwaggwo da Abba yyi tun sassafe, Aunty na xaune parlon sai Umma da duk ta fige damuwa yyi mugun mata yawa, amma da ta tuna Mujaheed ya dawo kuma tana da yakinin yau xai yi saki sai ta samu relieve, Aunty suka gaisa da Ammi, Ammi ta nemi waje ta xauna, Umma dai bata yarda ta kalleta ba, bayan nan Yusuf ya shigo yana rike da makullin motarsa ya xauna ya gaida parent din nasa, Abba ya shigo parlon tare da Daddy duk suka xauna, Daddy ya amsa gaisuwar Yusuf yana tambayarsa matarsa, Kawu Bala ne next din shigowa nan kuma aka yi ta jiran Inna da Imaan sai Mujaheed, Inna ta wangale kofa ta shigo, Imaan na biye da ita sanye da hijab har kasa, kanta a kasa ta xauna kasa kusa da inda Inna ta xauna, Abba ya gaida Inna Daddy ma ya gaisheta sannan kawu Bala sauran ma duk suka gaisheta, sama sama ta dinga amsa gaisuwar tana kalle kallen inda xata ga Mujaheed, Imaan ta gaida su Abba sannan ta gaida su Aunty, Umma dai ta ki yarda ta kalleta sai kallon kofa take tana jiran shigowar Mujaheed dinta, Inna tace "Naga Ikon Allah, toh shi ina mutumin yake, ni fa ban gama tsaftace bandaki na ba na yo nan gaskiya Ahmadu...." Bude kofar parlon aka yi Mujaheed ya shigo suka hada ido da Imaan da ke kallon direction din, da sauri ta sunkuyar da kai gabanta na faduwa ta matsa kusa da Inna kamar irin xuwa yyi ya dauketa, sanye yake cikin kananun kaya ya sauke kansa kasa bai yarda ya kalli kowa parlon ba ya karasa kusa da Yusuf ya xauna sannan ya gaida occupant din parlon kansa a kasa, Shiru ne ya biyo baya a parlon, Umma dai sai kallonsa take ganin wani fresh da yyi abun sa, hakan yasa ta kara jin hankalin ta ya tashi, wato bai damu ba kenan??? kawu Bala ya bude wajen da addu'a sannan ya kalli Abba, Abba ya sauke boyayyen ajiyar xuciya calmly yace "Abubuwa da dama sun faru tun bayan wannan aure da na hada ba tare da shawara da kowa ba few days ago, domin haka nake mai kara ba ma kowa a parlon nan hakuri bisa bacin rai da aka shiga da dai sauran su, to bayan wannan ina son jin views din ku a parlon nan akan auren nan kafin mu san abun yi, Ni da Sadeeq da Bala ba mu da abin cewa tukun sai mun ji naku ra'ayin in sha Allah, but before then... jiya Hadiza ta xo min da wani batu da yake bukatar a duba sa sosai...." Inna dai sai girgixa kafa take, Abba na kallonta yace "Inna xa mu so mu fara jin ta bakin ki a kan auren Imaan da Mujaheed da na hada...." Inna ta katse sa da sauri tace "Me kuwa xan ce Ahmadu, ka ji ta bakina kamar Yaya? wllh Imaan bata son auren nan don ma ka ji, da a shiga hakkinta fa? Tun xamanin kakannin mu aka daina auren dole, toh tunda ta ce bata so gaskiya ni ban ga amfanin auren ba, kada in je in rasa ta a banxa, yanxun nan ya rubuta mata saki ta san inda dare yyi mata, amma gaskiya ba wai bana son auren bane tunda duk jikokina ne, to da wani abu ya samar min jika fa? Ko bacci fa bata yi bata cin abinci, A'a wllh ba ruwanaa" Mujaheed dai sai kallon Inna yake kasa kasa, Umma taji kamar ta goya Inna don murnan furucin ta, Mama Hadiza dai ko kallon Inna bata yi ba sanin awa daya yyi kadan tace ai bbu auren da ya fi na Imaan da Mujaheed daraja a duniya, Abba ya sauke ajiyar xuciya ya kalli Mama Hadiza yace "What did you think Hadiza?" Mama Hadiza ta d'an yi shiru sannan cikin sanyin murya tace "Barrister in har su yaran basu son auren nan abu mafi sauki da kwanciyar hankali shine a raba, xumunci ba abun wasa bane, kada wnn aure ya 6ata xumunci gaskiya...." Abba ya gyada kai cikin gamsuwa bai dai ce komai ba, can ya kalli Umma yace "Meye ra'ayin ki Rukayya?" Umma ta fara matsar kwalla tace "Ba shi da fa'ida auren nan Alhaji, ita yarinya ba so take ba uwar yarinya ba so take ba, toh wani aure kuma Allah na tuba...." Abba yace "Ke ma kuma ba so kike ba koh?" Umma dai bata ce komai ba sai matsar kwalla take, a hankali tace "Alhaji raba auren nan shine kwanciyar hankalin kowa..." Abba ya kalli Aunty yace "Amina ur view?" Aunty ta sauke ajiyar xuciya tace "Duk yanda Allah ya tsara dai dai ne Alhaji, in barin auren in kuma raba auren..." Abba ya kalli Yusuf yace "Engineer..." Yusuf ya d'an yi murmushi bai ce komai ba, Abba ya kalli Imaan da kanta ke kasa yace "Mamana baki son auren nan ko?" Ta fashe da kuka kamar jira take ta gyada masa kai tana shessheka, Abba ya kalli Ammi yace "Hajiya Aisha??" Ammi ta kallesa tace "Gwara raba auren Barrister...." Abba ya kalli Mujaheed yace "M.A...." Mujaheed ya kallesa, ya d'an yi shirun kusan second biyar sannan yace "Baxan iya sakinta ba Abba...." Duk aka xaro ido a parlon ana kallonsa, Imaan ta fashe da matsanancin kuka ta fada kan Inna da ta hangame baki tana kallon Mujaheed ita ma, Abba na kallonsa kamar yanda Daddy ma ke kallonsa yace "Ko saboda me?" Mujaheed ya sunkuyar da kai a hankali yace