Showing 186001 words to 189000 words out of 303099 words
yi ba ya wuce parlon sa, Umma ta wuce sama da sauri don dauko hijab, Mikewa Mujaheed yyi ya fita parlon ya bi bayan Aunty, tare ya gansu suna tahowa da Ammi dake sanye da hijab ita ma, yana tsaye har suka iso, ya gaida Ammi ta amsa tana tambayarsa ya aiki, yace "Alhmdllh, ya mai jiki" Ammi tace "Toh da sauki" a hankali yace "Toh mu je in ajiye ku" Aunty tace "Toh ka kyauta" dai dai nan Umma ya fito parlon sanye da hijab ita ma, tana kallon Aunty tace "Toh Amina xuciyata bata kai inda kike tunani ba lalacewa, rashin lafiya Kuma da ke kan kowa kike boye min fisabilillahi??" Aunty ko kallonta bata yi ba ta nufi gate, Ammi dai bata ce komai ba ita ma tafiyar take, Umma tace "Munafurci dai bashi da amfani a rayuwa, kuma tare kika shigo gidan nan kika ganmu da Aisha" daga haka ta kalli Mujaheed tace "Kai xaka kai mu ne" ba tare da ya kalleta ba yace "Ehh" har suka shiga motar tasa babu wanda yace komai, Aunty ta gaya masa asibitin bayan sun hau saman titi. Maimoon ce ta fito ta kai su har ward din da imaan take, Mummy na xaune saman kujera kusa da gadon da imaan take kwance tana bacci, sai kannin Sadeeq biyu da kanwarta da Mariya, Su Aunty na shiga ward din Mummy ta fara welcoming din su, a ka shiga gaisawa fara'a, Umma dai sai kallon Mummy take, Mummy tace "Jikin ma da sauki sosai, kawai drip din ne da bai kare ba, don sunce biyu ne" Aunty tace "Toh Alhmdllh, Allah ya sauwake, ku kuma Allah ya bada lada" Mummy tayi murmushi tace "Toh Ameen, Allah ya bata lafiya" Mujaheed dai na tsaye daga bakin kofa yana kallon Imaan dake bacci tana sauke numfashi a hankali, da sallama Sadeeq ya shigo ward din....
*Imaan isn't for free* it's 300 via
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788
67....
Sadeeq ya gaida su Aunty da ladabi, sannan ya gaida Umma ma dake ta kallonsa, Umma tace "Lafiya lau, ya hidima?" Yace "Alhmdllh" Umma tace "Toh Allah ya bata lafiya, ku kuma Allah ya sassaka da dawainiya, a haka nan dai ake kullum yau ciwo gobe lafiya, an rasa gane kan abun dai, Allah dai ya rabata da wannan cuta da ya ki ci ya ki cinyewa ni Rukayya" Mujaheed dake ta kallon mahaifiyar tasa ya karasa cikin ward din xuwa gadon da imaan take tana bacci ya tsaya yana kallonta, ya kai hannu goshinta ya ji babu xafi bacci dai take mai nauyi, Umma dai sai wani kallo take masa ta gefen ido, Aunty na kallon Mummy tace "Toh Hajiya tunda kuna nan mu xa mu koma, Allah ya saka da alkhairi, mun gode kwarai" Mummy na murmushi tace "Ah haba dai ba komai ai yi ma kai ne, Allah dai ya bata lafiya, ya ba mu alkhairi" Ammi ma tayi mata godiya hade da sallama, Umma da ke xaune ta ki tashi ta bi su da kallo baki sake tace "Sai kace ana koranmu ko tashi yarinya bata yi ba balle mu ga lafiyarta ku ce xa mu wuce?" Can ta tabe baki tana gyara xama tace "Atoh ku je ni sai na xo" Ita dai Ammi bata ce komai ba har ta fita Maimoon ma ta fita, Mujaheed dai sai kallon uwar tasa yake daga inda yake tsaye, Aunty dake ta kallonta ta dai nufi kofa tana danna wayarta, suna fita ward din ta kai waya kunne bayan wani lkci tace "Toh ga Matar ka can gaban surukai tana maganganu da bai dace ba a kan ciwon 'yar ka, mun fito yanxu xa mu tafi tace babu inda xata kawai dai don ta samu sararin ci gaba da rashin kirkinta a wajen, idan ma xaka kirata to ka kirata ta fito ward din nan, Banda ma kinibibi da can duk ciwon da Imaan take ta ta6a bin mu asibiti...." Bata jira cewarsa ba ta kashe wayarta fuska daure, Ammi dai sai murmushi take suna tafiya, ko minti daya ba ayi ba Abba ya kira Umma dake kallon Mummy tana cewa "Mun gode fa, Allah ya saka da alkhairi ya bada lada, abun kam sai addu'a yau ciwo gobe lafiya ana dai ta tafiya a haka..." Ring din wayarta yasa tayi shiru tana kallon screen din, can ta daga ta kai kunne kafin tace komai Abba yace "Rukayya ku dawo gida yanxun nan gaba daya" a hankali tace "Ko saboda me?" Strictly yace "Nace ki dawo yanxu Madam" tace "Toh" daga haka ta katse wayar tayi tagumi tana kallon Imaan bayan kusan minti uku ta mike tana murmushi tace "Toh, Hajiya tunda sun ce mu tafi bari mu wuce don a mota daya muke, ma dawo da safe, Allah ya saka da alkhairi" Mummy tace "Toh Ameen, Allah ya tashe mu lafiya, sai da safen" Da ido Mummy ta bi ta har ta fita kafin ta dauke kai, Mujaheed dai na tsaye kusa da gadon har sannan idonsa na kan imaan, Sadeeq dake tsaye ya ja kujera ya xauna, Mummy na kallon Mujaheed da murmushi tace "Kanwarka ce koh?" Murmushin yyi shi ma yace "Ehh kanwata ce" Mummy tace "To madallah, ga kujeru ka xauna" Yana kallon drip din da aka sa mata yace "Am comfortable ma" tace "Toh yyi kyau" Mariya ce ta shigo dakin rike da warmer din abinci ta ajiye tace "Bata tashi ba har yanxu?" Mummy tace "Eh bata tashi ba" Mariya na kallon Mujaheed tayi murmushi tace "Ina yini Dr?" Mujaheed ya mayar mata murmushin yace "Lafiya lau Mariya" Mummy na kallonsa tace "Kai ma likitan ne kenan" shafa kai kawai yyi yana murmushi, Mariya tace "Ehh Dr ne, a Chasel hospital yake aiki" Mummy tace "Maa sha Allah, that's good" Shi dai Mujaheed bai ce komai ba, Sadeeq dai sai danna wayarsa yake babu yabo bbu fallasa, Mujaheed ya kalli agogo yace "Xan je in yi isha, xuwa anjima xan dawo in sha Allah" Mummy tace "Toh sai ka dawo" daga haka ya nufi kofa ya fita, Mummy na kallon Sadeeq tace "Are they of the same mother?" Girgixa kai Sadeeq yyi har sannan yana danna waya, Mummy tace "Stepmother dinta ce warce ta fita yanxu?" Sadeeq ya kalleta yayi d'an murmushi yace "Not at all, mum din shi wanda ya fita ynxu ne" Mummy bata kuma cewa komai ba. Karfe takwas da rabi Imaan ta farka daga baccin da take, har sannan Mummy na xaune kusa da ita tare da Suhaila sai sadeeq dake xaune idonsa a kan wayarsa, Aunty kuma na can gun Aisha Kanwar sadeeq dake kwance daya ward din, Mummy na kallonta tace "Sannu, ya jikin?" Ta d'an yi murmushi tace "Na ji sauki" Mummy tace "Toh Allah ya sauwake" Shi dai Sadeeq kallonta kawai yake, ta mike xaune a hankali tace "I want to use the restroom" Mikewa Sadeeq yyi ya cire tube din ruwan ta sakko daga saman gadon tana dafa gado sbda jirin da ta ke ji, Mummy dai sai sannu take mata, Suhaila xata kama hannunta tayi murmushi tace "Xan iya" daga haka ta wuce bathroom dake ward din tana dingishi, Mummy dai ta bi ta da kallo, Da alwala ta fito bathroom din ta karasa kan gado ta dau Hijab dinta dake linke, Mummy tace "Sllh xa ki yi?" Imaan ta gyada mata kai, Mummy ta kalli Suhaila tace "Ki tafi can ward din ki dauko darduma" Mikewa Suhaila tayi ta fita, shi dai Sadeeq sai kallon Imaan yake, ita kuwa bata yarda ta kallesa ba, Mummy ta nuna mata kujera tace "Toh xauna kafin ta dawo" ba musu ta xauna saman kujeran, ba a dau lkci ba Suhaila ta dawo da pray mat ta shimfida mata. Imaan na xaune pray mat din bayan ta idar da sllh, Mummy ta bude warmer ta debi hadadden jollof rice da Mariya ta kawo daga gida ta sa mata da enough meat, Mummy tana kallonta tace "Toh tashi ki hau saman gado ki ci abincin" Mikewa Imaan tayi ta hau saman gadon ta mika mata abincin ta amsa a hankali tace "Nagode" Suhaila tace "A hada maki shayi?" Girgixa kai Imaan tayi tace "Wannan ya isheni" Bude kofar ward din aka yi Abba ya shigo da sallama tare da Maimoon, Sadeeq ya mike har ya iso cikin dakin Abba yayi ma Mummy sannu ta amsa tace "Sannu da xuwa" gaishesa Sadeeq yyi Abba ya amsa da fara'a yana tambayarsa mai jiki, sannan ya kalli Imaan dake kallonsa yace "Sannu Mamana, how are you feeling now" tana murmushi tace "Na ji sauki Abba, Ina yini" yace "Lafiya lau, Allah ya kara lafiya daughter" Mummy tace "Ina yini Alhaji" Abba yace "lafiya lau, ya masu jiki" tace "Alhmdllh da sauki sosai" yace "To madallah, Allah ya basu lafiya, Allah kuma ya bada lada" Mummy tace "Ameen" Maimoon ta ajiye ledan fruits dake hannunta tana kallon Imaan tace "Sannu" Murmushi imaan tayi mata, Abba yyi ma Mummy sallama yace xai shiga ya duba sis din Sadeeq, Mummy tace "Tou mun gode Alhaji" yana kallon Imaan yace "Sai da safe Mamana, Allah ya kara lafiya" ta amsa da "Ameen, thanks Abba" tare suka fita da Sadeeq da xai kai sa gun sis dinsa. Basu kai minti biyar da fita ba Mujaheed ya shigo dakin hannunsa rike da leda, Tun da suka hada ido Imaan ta sunkuyar da kanta, ya karaso ciki yana ma Mummy sannu, Mummy tace "Har ka dawo" yace "Ehh na dawo" Yana kallon Imaan da taki yarda ta kallesa yace "How are feeling now" still bata kallesa ba tace "Na ji sauki" ya ajiye ledan hannunsa a table, yana silencing wayarsa dake ringing, Mummy ta nuna masa kujera tace "Toh ka xauna koh" ya d'an yi murmushi ya xauna saman kujeran, Imaan dai sai juya abincin gabanta take, Mummy tace "Ba fa cin abincin kike ba" diba tayi ta kai baki ta dago kai tana kallon Mujaheed dake kallonta, a hankali ta dauke kanta tana cin abincin. Sai kusan karfe goma Sadeeq ya dawo dakin, Tun da ya kalli Mujaheed sau daya ya dauke kai yana kallon Mummy yace "Xa a mayar da ke gida ne tunda Suhaila da sis dinta na nan?" Mummy tace "Don't worry nan da anjima sai in tafi" Yace "Ohk" karasawa yyi kusa da Imaan murya can kasa yace "Ba inda ke maki ciwo ko?" Ta gyada masa kai kawai, yace "Ohk, xan je gida in dawo yanxu, I want to freshen up" ta kallesa tace "Ohk" murmushi ya sakar mata ta sunkuyar da kanta, ya juya yana kallon Mummy yace "Xan dawo ltr mum" daga haka ya nufi kofa Mummy tace "Toh ai ba ku yi sallama da Dr ba" Juyowa sadeeq yyi ya kalli Mujaheed yace "Ohh I didn't notice him, see ya ltr..." Mujaheed ya d'an yi murmushi yace "Alright" Daga haka ya fice daga ward din. Imaan ta daga kai ta kalli Mujaheed taga kallonta yake ta turo baki ta dauke kai, Mujaheed bai bar hospital din ba duk da kiran da Safeenah da Umma suka dinga lafta masa, ya kuma ki dagawa, har sai da Umma ta kira Maimoon tace ta kai masa waya, Maimoon na kallonsa ta mika masa wayar tace "Ya M.A...." amsan wayar yyi ya kai kunne, cike da bala'i da masifa Umma tace "Mujaheed wai Kanwar Uwarka ko ta ubanka ce kwance gadon asibiti???" Shi dai bai ce mata komai ba, rai bace tace "Tun raina bai gama baci gaba daya ba ka kama hanyar gidan ka yanxun nan, ka bar yar mutane can ita kadai tsakar dare kamar ni ce kwance ba lafiya a gadon asibiti, ko meye hadin ka da sauran ciwon?" Mujaheed bai ce komai ba ya katse wayar ya mika ma Maimoon ta amsa, Mujaheed bai bar asibitin ba duk da fadan Umma sai kusan Sha daya da wani abu, shi ma Mummy ce tace masa amma ba shi da family, Bai bata amsa ba sai murmushi da yyi ya mike yace "Toh sai da safe, Allah ya bada lada" tace "Ameen" Imaan dake kwance ta rufe ido kamar mai bacci, ta bude idon ta bi sa da kallo har ya isa kofa, sai kuma ya juya ya kalleta, da sauri ta rufe idon, har xai fita sai kuma a hankali tace "Sai da safe" Yana kallonta yace "Allah ya tashe mu lafiya" daga haka ya fita ya rufe kofar. Washegari aka sallami Imaan karfe sha daya na safe, Stepmum din Sadeeq da su Suhaila ne suka kai ta har gida, Ammi tayi masu godiya tare da Aunty, basu wani jima a gidan ba suka wuce tunda tare suke da driver. Bayan sati daya da yayi dai dai da saura sati guda a kawo lefen Imaan.... Umma ce xaune makeken parlon gidan Bulasawa tare da Hajiya Balaraba sai Safeenah da ta ke ta taunan cingam ta ci kwalliya iya kwalliya tayi kyau, ba don Suhaila da ta gansu bakin gate a tsaye ta dawo boko a motarta ba da babu yanda xa ayi a barsu su shigo gidan don masu gadi sun ce ba a sanar da su xa ayi bak'i ba, ynxun ma sun fi minti sha biyar xaune parlon suna jiran fitowar uwar gidan Bulasawa, duk sun yi shiru kamar masu xaman makoki, can dai Hajiya Saude na kallon Umma murya can kasa tace "Anya shawarar nan tayi kuwa Hajiya Rukayya??" Umma na kallon Safeenah tace "Ni ban kawo hakan a kai ba fa, sai da Safeenah ta kawo shawarar, kuma jikina ya bani da nasara...." Safeenah ta tabe baki tace "Ku dai ba ni nace ayi haka ba?? ku kwantar da hankalin ku kawai, na fa san abinda nake, haka kawai ga hanya mafi sauki kuyi ta kai ma katti kudin ku suna cinyewa, har yanxu ban ga alamar abun da ake ta ce maku ba gashi saura sati a kai lefe a sa rana, ga dai hanya straight...." Umma tace "A'a wllh babu me cinye min kudi, ana biya min bukatata yanda ya kamata... So nawa kuma??" Shigowar Mummy parlon sanye da hijab har kasa yasa duk suka yi tsit, kallonsu ta dinga yi har ta karaso ta xauna saman kujera, Umma na murmushi tace "Sannu da fitowa Hajiya" Mummy tace "Yauwa daga Ina?" Umma tayi yar dariya tace "Lahh, baki gane ni ba Hajiya??" Mummy dai sai kallonta take don sarai ta gane ta, can kuma ta girgixa kai tace "A'a ni ban gane ku ba, daga Ina?" Umma tace "Toh ni dai sunana Hajiya Rukaiya, in dai kina jin Barrister Ahmad Yusuf na nan kaduna to Mai gidana ne..." Mummy bata daina kallonta ba tace "Ohk..." Umma tayi kasa da murya tace "Hajiya a matsayina na yar uwar ki musulma na xo maki taimako albarkacin musulunci..." Da mamaki Mummy tace "Taimako kuma? Wani irin taimako nace maki ina bukata??" Umma ta gyara xama tace "Hajiya don nace na xo maki taimako ba ina nufin kudi ko wani abu gareni da xan baki ba don kin fi karfinsu, amma ki sani wllh wllh taimakon nan sai ya fi maki kudi ko wani abu na kyale kyalen rayuwa... Hajiya kin san shi aure ba abu bane da xa ayi na rana daya a gama ko na wata daya, A'a rayuwa ce da ake fata ya xama na har abada, kin ga wannan yarinyar da d'an ki ke nema??" Ita dai Mummy kallonta kawai take, Umma tace "Toh wllh wllh kin ji rantsuwar musulmi sickler ce, sannan kin ga yanda kika ganta ita kadai, to har gun iyayenta ita kenan takk... uwar ta fi shekara 13 bata haihu ba, kafin daga karshe taje ta san abinda ta yi Allah ya bata yar, wanda da Allah ya tashi kamata ya hadata da sickler, har yau kuma wllh tllh uwar ta hana uban karin aure kiri kiri, sannan babu wanda bai san abinda take ba, daga ita sai yar suke yanda suka ga dama a daulan uban, matar kanin mijina ne uwa daya uba daya, kin ga dai ba kishiyata bace ita balle ace ina ma 'yar ta bakin ciki, ko daya wllh ba haka nake ba, gaskiya ce duk inda take sai na fade ta, yanxu haka maganar da nake maki d'an kishiyata Yusuf ni ce kan gaba gun nema masa aure gidan Alhaji Mukhtar Kiyawa da kika sani dai na nan garin, wllh wlh mahaifiyar yarinyar nan ba mutuniyar kirki bace muguwar bafillatana ce ta karshe, kije anguwar mu malali ki shiga gidajen layinmu kaf kiyi tambaya a kanta xa ki sha labari, tayi kadan in mata hassada wllh balle ace ko hassada nake mata, Bari ki ji Hajiya wllh a ta dalilin ta Mai gidana ya min kishiya, ta cusa masa aminiyarta ina ji Ina gani ta aure min miji, ita kuma taki barin a mata kishiyar har yau gashi ba haihuwa take ba, ita ma kuma ita kenan gun uwarta, sae gashi ta haifi kwaya daya ita ma, kakar yarinyar ma gwaggwo ita kadae iyayen suka haifa aka ce, kamar yanda baxan so Mujaheed da abinda xai cutar da shi a rayuwa ya xame masa wahala ba haka baxan so ma duk wani matashi ko da ba ni na haifesa ba, a wata wllh uban yarinyar na kashe mata kudi ya fi dubu dari biyu, kullum cikin abu daya ake idan ciwon ya matsa mata kuwa ke kya ce baxata yi ba, shi sa nayo tattaki in sanar maki ki ceci d'an ki, barin ma shi da yake d'an ki na fari....."
*Imaan isn't for free* it's 300 via
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788
68......
Umma tayi shiru tana kallon Mummy tana jiran jin abinda xata ce, sai dai fa gabanta faduwa yake, Safeenah da Hajiya Saude ma kallonta suke su ji abinda xata ce, Mummy da tayi shirun kusan minti biyu ta sauke ajiyar xuciya daga karshe tace "Alright, I will look into the matter, nagode da shawara" Umma