Showing 273001 words to 276000 words out of 303099 words
ya ci gaba da driving dinsa, bayan kusan minti goma ta xame hannunta a hankali daga fuskarta tana kallon titin gabanta, da sauri ta kallesa tana goge idonta tace "Ina kuma xa mu je yaya?" Ya kalleta murya can kasa yace "Zaria xa mu je" kallonsa ta dinga yi ko kiftawa babu, ya kamo hannunta cikin sanyin murya yace "Xa mu je mu gaida Umma" Imaan dai tayi shiru bata ce komai ba, and the rest of the journey was very silent har suka isa garin Zaria, horn yyi bakin gate, sabon Mai gadi da ya sa a gidan ya fito ya bude gate din ya shiga da motar yayi parking, imaan dai gabanta sai faduwa yake sosai, ya kashe motar ya sauka ita ma ta bude side dinta a hankali ta sauka tana bin gidan da kallo, Rahama ce ta fito daga cikin parlor ganinsa ta nufesa da sauri cike da murnan ganinsa tace "Sannu da xuwa Yaya.... Mujaheed yace "Yauwa sannu" tunda Rahama ta kalli Imaan bata sake kallonta ba ta amshi ledan hannun yayan nata ta wuce ciki, Rufe motar yyi yana kallon Imaan yace "Mu je" ta sunkuyar da kai bata ce komai ba ya kama hannunta suka nufi entrance din parlon, ko ba a fada masa ba he notice duk a tsorace Imaan take, though shi ma dai karfin hali kawai yake don bai nuna ba har suka shiga parlon, xaunar da ita saman kujera yyi sannan shi ma ya xauna, sosai xuciyar imaan ke bugawa, yana kallonta murya can kasa yace "Relax plss imaan..." Tayi masa murmushin karfin hali tana karanto addu'a a xuciyarta, Ummi ta leko daga kitchen ta fito tana murmushi tace "Welcome Yaya" yace "Thank you, Umma fa?" Ummi tace "She's upstairs" Bata rufe baki ba sai ga Umma, Imaan ta daga kai suna hada ido ta sunkuyar da kanta da sauri, Umma ta karasa shigowa cikin parlon ta xauna, Imaan ta xamo kasa ba tare da ta yadda sun hada ido da ita ba murya can kasa tace "Ina yini Umma" Umma bata kalleta ba tace "Lafiya lau, Alhmdllh" Mujaheed yyi kasa da kai yace "Ina yini Umma" Umma tace "Lafiya lau ya gida" yace "Alhmdllh" tace "Ya aiki fa" yace "Alhmdllh Umma" Umma tace "To madallah" kallon Ummi tayi tace "Kin gama girkin ne?" Ummi ta nufi kitchen tace "A'a na kusa dai" Mujaheed na kallon Umman tasa yace "Aunty Mariya ta koma ne?" Umma tace "Aa taje kasuwa xata dawo" Mujaheed yace "Ohk..." Ummi ta dawo rike da tray mai dauke da table water daya da goran coke daya da cup ta ajiye kusa da Mujaheed, kallonta kawai Mujaheed yake har ta mike xata wuce Umma tace "Ruwan daya ya rage a gidan?" Ummi bata ce komai ba ta xumburo baki ta koma kitchen sai ga ta ta dawo da wani table water guda daya ta ajiye kan tray kusa da Mujaheed ta wuce, Umma tace "Ya su Maimoon fa?" Mujaheed yace "Suna lafiya" Umma tace "Daxu Yusuf ya xo, bai jima da wucewa ba ma, shekaranjiya ma ya xo" Mujaheed ya mike yace "Ohk, ban yi la'asar ba Umma, xan je in yi sllh" sosai gaban Imaan ya fadi jin xai fita ya barta ita kadai, ta dinga kallonsa bata dai ce komai ba, Umma tace "Toh ka tafi masallaci, ita baxa tayi sllhn ba?" Mujaheed ya kalli Imaan yace "Kin yi sllh ai?" Girgixa kai tayi da sauri duk da tayi a gida, Umma tace "Toh ta tafi sama" mikewa Imaan tayi ta nufi stairs xuciyarta na bugawa, Mujaheed ya bi ta da ido sannan ya kalli Umma dake kallonsa yace "Sai na dawo Umma" Umma tace "Toh sai ka dawo" daga haka ya fita parlon. Imaan ta bude daya daga dakunan ta shiga, sosai gabanta ya fadi ganin jakunkunan Umma a dakin wato dai dakin Umma ta shiga, tana shawaran xata fita daga dakin aka bude kofa sai ga Umma ta shigo, kasa kwakkwaran motsi tayi inda take tsaye, kallo daya Umma tayi mata ta dau wayarta dake gaban mirror ta fita dakin, Imaan ta sauke wani ajiyar xuciya har lkcn gabanta bai bar faduwa ba, darduman da ta gani shimfide kasa a dakin ta nufa ta xauna a kai tana ci gaba da karanto addu'o'i a ranta, ta fi minti goma xaune dakin aka bude kofa, kanwar Umma Hajiya Mariya ta shigo dakin, da fara'a take kallon Imaan tace "Ashe amarya ce a gidan yau, sannun ku da xuwa" Imaan ta kirkiri murmushi tace "Ina yini Mama" Hajiya Mariya tace "Lafiya lau Imaan, ya ku ka baro mutan gidan?" Imaan tace "Alhmdllh" Hajiya Mariya tace "Toh madallah, Allah ubangiji ya sanya albarka a auren nan, ya bada xuri'a dayyaba" Imaan ta sunkuyar da kai bata ce komai ba, Hajiya Mariya ta ajiye handbag din hannunta ta fita dakin. Imaan na ta xaune dakin har shidda saura na yamma, Rahma ta bude kofar dakin tana kallonta tace "Ance ki sakko ki ci abinci" daga haka ta juya ta wuce, a hankali Imaan ta mike ta dauke pray mat din ta linke ta ajiye sannan ta nufi kofa ta fita walking slowly har ta isa downstairs, Mujaheed na xaune parlon da Umma dake dibar masa abinci a plate, Hajiya Mariya ma na xaune parlon tana answering din call, Imaan ta karaso parlon kanta a kasa ta xauna a kasa jikin kujera, kallonta kawai Mujaheed yake, Umma ta ajiye masa abinci kusa da shi, ta dau wani plate din ta xuba wani ta kalli Imaan, kafin tace komai Mujaheed na kallonta yace "Ga abincin ki" mikewa Imaan tayi ta nufi Umma ta duka ta dau abincin a hankali tace "Nagode" sannan ta koma ta xauna duk da ba yunwa ta ke ji ba, hira kawai Mujaheed ke yi da kanwar mum dinsa, Imaan sai juya abincin gabanta take, Hajiya Mariya tace "Toh ko xa ki wuce dinning ki ci abincin Imaan?" Imaan tayi murmushi tana kallon direction din dinning din, Hajiya Mariya tace "Tashi ki je can ki xauna kin ji" mikewa Imaan tayi ta dau abincin da ke cike da nama ta wuce dinning ta xauna, tana ta xaune can bayan ta d'an ci abincin da xata ci, Hira kawai Mujaheed yake da Hajiya Mariya amma gaba daya hankalinsa na kan Ummar sa da tayi shiru bata cewa komai, can kuma ta mike ta wuce sama ya bi ta da kallo, jin ana kiran Magrib ya mike yace "Xan je masallaci in dawo mum" Hajiya Mariya tace "Toh sai ka dawo" ya kalli imaan sannan ya nufi kofa ya fita, Hajiya Mariya ta mike ta dau plates dake parlon ta kai kitchen ta fito tana kallon Imaan daga inda take xaune tace "Tashi kema kiyi sllh Imaan" Imaan tace "Toh" daga haka ta mike, sbda dadewan da tayi xaune a dinning din sai taji kafarta ya d'an rike mata, haka dai ta daure ta wuce sama, wani dakin daban ta bude ta shiga bandaki tayi alwala, ta fito ta xauna bakin gado, ta kusa minti biyar a xaune aka bude kofar dakin Ummi na tsaye bakin kofa tace "Ance ga darduma can kije kiyi sllh" Mikewa Imaan tayi ta fita dakin tana tafiya a hankali saboda kafarta, dakin Umma ta bude ta shiga da sallama murya can kasa, taga darduman a shimfide ba kowa dakin, ta hau saman darduman ta tada sllhn, tana ta azkar bayan ta idar da sllh Hajiya Mariya ta shigo dakin tace "Imaan ke Mujaheed ke jira xa ku wuce" A hankali Imaan tace "Toh" sannan ta mike ta dauke darduman ta linke ta ajiye, Hajiya Mariya tace "Sai ayi ta hakuri, Allah ya ba ku xaman lafiya" imaan bata iya tace mata komai ganin yanda take tafiya Hajiya Mariya tace "Me ya samu kafar kuma" kamar xata yi kuka tace "Ciwo yake son ya min" Hajiya Mariya tace "Ayya sannu, kun xo da drugs din ki ne?" Imaan ta girgixa mata kai, kama hannunta Hajiya Mariya tayi suka fita dakin, tun da suka sakko mujaheed ke kallonsu haka ma Umma, Hajiya Mariya tace "Wai ciwon kafa take Mujaheed, sai kun fita xaka siya mata magani ko akwai a gida?" Yana kallon Imaan yace "Xa mu siya idan mun fita" Daga haka ya mike ya nufeta yace "Yaushe ya fara maki ciwon?" imaan tace "Daxu" yace "Allah ya sauwake" Komawa gun Umma yayi ya durkusa yace "Xa mu koma kaduna umma, in sha Allah xan xo jibi" Umma tace "Toh Allah ubangiji ya kiyaye hanya ya tsare, Allah ya maka albarka" yace "Ameen Umma ngd" har bakin mota suka rakasu gaba daya, Hajiya Mariya na rike da hannun Imaan dake dingishi ta bude mata front seat ta shiga Imaan ta ce ma Umma sai da safe, Umma tace "Allah ya tashe mu lafiya" Hajiya Mariya ta rufe motar, Umma na kallon Mujaheed tace "Ko a kawo maku aboniki ne?" Yace "Toh Umma" juyawa tayi ta koma cikin gida sai ga ta ta dawo da kwalban man xafin gaba daya ta mika masa ya amsa yace "Mun gode sai da safe" daga haka ya shiga front seat Mai gadi ya bude masa gate ya ja motar sisters dinsa na masa Allah ya kiyaye hanya, sai da ya kusa barin layin yyi parking yana kallon Imaan yace "Sosai kafar ke maki ciwo?" Ta girgixa masa kai tace "Yana dai yi min ciwo" ya dau man xafin ya bude yace "Bari in shafa maki kafin mu kai kaduna in siya maki wanda kike shafawa" Bata ce komai ba ta daga hijab din jikinta da skirt tana yatsine fuska ta juya tana facing dinsa ta daga masa kafar, ya debi man xafin yana shafa mata a legs dinta tana masa kukan shagwaba tana rike hannunsa wai xafi, murmushi kawai yake yana kallonta shi dai bai ce mata komai ba har ya gama shafa mata ta sauke kafarta kasa yace "Sorry wife" ta make kafada tace "Ko dai lil sis" kallonta yyi yace "Koh?" Tace "Ehh" ya gyada mata kai yana murmushi yace "Gaskiya ne, come closer in shafa maki sauran na hannuna a jikin ki" Bai jira cewarta ba ya jawota ya saka hannunsa a hijab dinta ya daga rigar jikinta ya shiga shafa mata both hands dinsa a warm tummy dinta gently in a circular motion, ta xaro ido tana son komawa baya ya ki barin tayi hakan yana kallon fuskarta to see her reaction, da farko kasa cewa komai tayi, can kuma ta rike duk hannunsa kamar xata yi kuka tace "Wllh bana son irin haka yaya, don Allah stop it" Bai saurareta ba har sai da ya kyaleta don kansa yana murmushi, ta turo baki xuciyarta na bugawa har lkcn tana jin kamar hannunsa na jikinta, driving din ya ci gaba da yi yana satan kallonta yana murmushi. Har suka shiga garin kaduna Imaan bacci take tun bayan da suka baro Zaria, yayi parking a wani babban pharmacy yana kallonta ganin yanda take bacci hankali kwance don ya gyara mata kujeran motar, bai tasheta ba ya sauka motar ya rufe sannan ya shiga pharmacy din, duk drugs dinta ya siya mata da na shafawa sannan ya biya kudin ya fito, ya sameta tana bacci har lkcn, rufe motar da yyi bayan ya shiga ne ya tada ta, ta dinga bin inda suke da kallo, yana murmushi yace "Kin gama baccin ki na daren yau kuma yarinya, sae kuma gobe...." Ta gyara xamanta tace "Where are we now?" Yace "Kaduna" daga haka ya tada motar suka bar haraban pharmacy din... Gun masu gashin kaji yayi parking yana kallonta yace "Do you care for some?" Tace "Meye shi?" Yar dariya yyi yace "Kazan kika manta yau?" ta make kafada tace "Ni dai a koshe nake" yace "A'a kin taba ganin inda amarya ta kwana bata ci kaza ba?" imaan ta wani hade rai tace "Ni ba Amarya bace" yace "Xa ki san ke amarya ce yau" daga haka ya sauka motar ta bi sa da kallo, guda daya ya siya sannan ya hada da chill fresh milk da suke siyarwa a wajen, yana dawowa cikin mota ya mika mata, ta ki amsa ta wani daure fuska, ya ajiye yana murmushi bai ce mata komai ba ya tada motar, har suka isa gida fuskarta a daure yake, Mai gadi ya bude masa gate bayan yyi horn ya shiga gidan yyi parking, ya juya yana kallonta, hawaye ya gani makale idonta, sauka yyi motar ya xaga ta side dinta ya bude motar ya kama hannunta ta fito daga motar hawayen dake idonta ya sauko kasa, jawota yyi jikinsa a hankali yace "Yayah ne fa Imaan"
*Imaan isn't for free* it's 300 via
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788
98......
Imaan dai bata ce masa komai ba ta sauke kanta kasa a hankali, yana murmushi ya ja dogon hancinta ta turo baki ta dauke kai, ledan dake cikin motar ya dauko ya kulle motar sannan ya kama hannunta suka nufi entrance din gidan, da makulli ya bude kofar ya shiga tana biye da shi a baya, banda kamshi na turaren wuta me dadi bbu abinda ke tashi a parlon dake dauke da new furnitures kamar ba a ta6a rayuwa ciki ba, komai na parlon sabo ne, yana rike da hannunta suka isa tsakar parlon ya ajiye ledan hannunsa ganin taki yarda ta daga kanta, ya kai bakinsa kunnenta yace "Baxa ki kalli gidan ki ba kanwata" Ita dai bata ce masa komai ba, yana facing dinta ya dago kanta a hankali yace "Imaan" shiru tayi tana kallonsa, ya sa finger dinsa ya share hawayen idonta yana murmushi ya kama hannunta suka wuce upstairs, bedroom dinta ya bude mata yana kallonta yace "Ur room" kallon dakin ta dinga tana tsaye bakin kofa, ya shigar da ita ciki ta lumshe ido ta bude jin daddadan kamshin dake tashi dakin, I don't want to talk about how expensive foreign furnitures da Daddy ya xuba ma tillon yar tasa, kudi ne ba na wasa ba ya kashe a dakin Imaan, ko yar governor sai haka, lol, ganin ta kasa cewa komai Mujaheed ya juya ya fita dakin, Imaan ta dinga bin babban bedroom din da kallo wasu sabbin hawaye suka kawo idonta amma na farin cikin abinda mahaifinta yayi mata, a sanyaye ta nufi kofar da ta gani cikin dakin ta bude a hankali taga bandaki ne babba, ta sauke kanta kasa ta juya ta fito daki, hijab din jikinta ta cire ta linke ta ajiye ta bude press taga gogaggun kayanta me yawa da sleeping dresses har inner wears, rufe gun kayan tayi ta koma bandaki ta dauro alwala ta fito ta dau sabon darduma dake linke kan stool din mirror, babu kalan turaren da babu gaban mirror din, sai lotions dinta da take shafawa da hair cream, ta shimfida darduman hannunta sannan ta tada sllhn Isha, ta jima xaune kan darduma bayan ta idar da sllh tana addu'a daga karshe ta mike har xata cire kayan jikinta sai kuma ta kalli kofar dakin, turo baki tayi ta tafi ta sa makulli ta dawo ta cire kayan ta linke ta ajiye ta shiga bathroom, babu abinda babu na bukata a cikin bathroom din tun daga sponge, soap da take amfani da, shower gel, toothpaste, toothbrush, hatta washing machine sai da Daddy ya siya mata aka sa a bathroom, ta hada ruwan xafi a bucket da ta gani tayi wanka, ta wanke bakinta da Listerine sannan ta dau brand new towel da ta gani a bandakin ta daura alwala ta dauro ta fito. Bata wani dau lkci xaune gaban mirror tana shafe shafen turare ba ta mike ta fiddo kayan baccinta a press ta saka, ta dau hijab tasa ta hau saman gado ta shige cikin duvet ta rufe idonta, Har bacci ya fara daukanta taji ana knocking, ta mike xaune ta wani hade rai tace "Waye wannan?" Mujaheed yace "Waye koh? to bude ki amshi drugs din ki..." Tace "I am not feeling pain anywhere" murmushi yayi yace "I know... but you need to take them" Kamar xata yi kuka tace "Wllh Yaya bana jin ciwo, kuma ni bacci nake ji, gobe xan sha" ya hade rai yace "Imaan open this door now" ta marairaice ttace "Yaya wllh am feeling okay" yace "Idan kika bari na bude kofar da kai na xan baki mamaki" tace "Wayyoo Yaya ba sai in sha gobe ba nace" yace "Ohk jira in samo makulli in dawo yanxu, Allah da gaske sai nayi shock din ki" xaro ido tayi tana kallon kofar, jin shiru ta mike gabanta na faduwa, murya can kasa tace "Yaya?" Taji shiru bai amsa ba, kara kiransa tayi ta ji bai amsa ba ta nufi kofar a hankali ta murda makullin dake jiki ta bude kofar, cafkota yyi ta fasa ihu a tsorace tace "Wayyo Yaya wllh ka ban tsoro" yace "Da me yasa kika rufe kofar?" Ta marairaice tace "Saboda Ina jin bacci" yana rike da ita suka xauna gefen gado yana kallonta yace "But Ain't you hungry?" Kai ta gyada masa gabanta na faduwa tana kallonsa, ya d'an yi murmushi yace "Toh amma sai ki ci kazan ki ko kadan ne, bari in dauko" da har xata ce A'a sai kuma ta kalli kofa, da sauri tace "Toh..." kallonta ya dinga yi kafin ya mike yana wani murmushi ya isa kofar ya cire makullin jiki ya fita dakin, ta xaro ido tana bin sa da kallo kamar xata fashe da kuka, ba a dau lkci ba ya dawo da plate dauke kaza sai fresh milk with cup, ya ajiye su saman lallausan carpet dake dakin ya xauna yana kallonta yace "Ko in xo in dauko ki?" A hankali tace "Yaya wllh na koshi da gaske" yace "Ehh just tsoka daya xa ki ci sai ki sha madaran" shiru tayi tana kallonsa kamar xata yi kuka, duk da dariyar da take basa ya hade rai yace "Baxa ki sakko ba" xamowa kasa tayi a hankali ta xauna tana facing dinsa ya dau tsoka