Showing 324001 words to 327000 words out of 432432 words
Chapter 109 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete
ƙwarin guiwar gaya mashi magana?duk irin yadda take jin shakkarshi?yarinyar da ko cikin idonshi tsoran kallo takeyi,balle har ta ɗaga mashi yatsa,
Gyara kwanciyarshi yayi,ya koma yana fuskantar right hand ɗinshi,sannu a hankali bacci ya dauke shi batare da ya shirya yin shi ba,
Wuraren ƙarfe Takwas na safe,jahad na cikin bacci,taji shessheƙar kuka acikin kunnuwanta,buɗe idanuwanta tayi tare da wurgasu wurin da take jin sautin kukan,Sehrish ta gani zaune ta jingina bayanta a head board ɗin gadon,sae kuka takeyi kamar wadda ta rasa wani mai mahimmanci arayuwarta,
Da sauri jahad ta miƙe zaune,tana kallonta tace"Sehrish!lafiya kike kuka?ko haryanzu ciwon cikin ne"?
Girgiza kanta tayi alamar a'a,
"To ki faɗamun meke damunki ne"?da damuwa a fuskarta tayi maganar,
Cikin shesshekar kuka Sehrish ta soma magana,
"Jahad!na shiga uku!najama kaina bala'e,Jiya nayi ma babban yayanmu rashin kunya,batare da sanina ba,wlh sai yau da safe na tuna duk abunda ya faru,nasan cewa bazai ƙyaleni ba,Dole ya hukunta ni"ta karasa maganar tare da sa hannu tana matsar hancinta,
Hankali atashe jahad tace"Sehrish!kodai mafarki kikayi ne?ae babban yayanmu bai dawo ba,kin manta sun tafi damaturu ne"?tayi maganar tana ƙoƙarin fahimtar da ita,
"Wlh jahad ba mafarki nayi ba,jiya ya dawo acikin gidan nan,yana nan a part dinsa,"
Hannu jahad tasa tare da dafe saitin zuciyarta adan tsorace tace"Munshiga Uku!garin yaya har kikayi mashi rashin kunya?kuma kina acikin hayyacinki babu magagin bacci atare dake"?
"Bana acikin hayyacina jahad,zafin ciwone yasa na balbaleshi da masifa,har ina nuna shi da yatsa..."kaf ta kwashe duk abunda ya faru a tsakaninsu ta sanar ma jahad,
Hannu jahad tashiga tafawa tana faɗin"wlh babu ruwana!sehrish kin shiga uku,mai kwatarki a hannunshi yau sai Allah,hukuncinki yafi ƙarfin ayi maki shi acikin gidan nan sai dai yakai ki can headquater dinsu,"
Jin wannan maganar,ya ƙara ɗaga hankalinta,fashewa ta kuma yi da kuka,
Lallashinta jahad ta shiga yi"Am sorry,zolayarki nakeyi,amma gaskiya sehrish Anya baki sha Codine ba?Yo ni ko giyar wake nasha,ae bazan iya tunkarar babban yayanmu ba,balle har in gaya mashi irin zafafa kalaman da kika yada mashi,"
Cikin shesshekar kuka tace"dan Allah jahad ki bani shawara,kodai in gudu in bar gidanne?kinga su daddy basu nan,zai iya kashe ni,"
Shiru jahad tayi tana saƙa wani abu aranta,sehrish kuwa ta zuba mata ido tana jiran jin shawarar da zata bata,
"Kinsan me!kada ki kuskura kije bashi haƙuri,Dama kin faɗa mashi cewa kada yayi tunanin zaki gudu kibar gidan ne,ko kuma zaki zo bashi hakuri,Sannan kuma kince mashi ba zaki ƙara zuwa part dinshi ba koda ace kin kammala ƙazantar ne,Inaso ya tabbatar da cewar dagaske kike mashi bada wasa ba,hakan zaisa abun ya tsaya mashi acikin ranshi kuma zaiji shakkar ƙara faɗa maki irin waɗannan kalaman saboda gudun kar girmanshi ya faɗi,sannan idan yaga kwana biyu baki je yi mashi aiki ba,ina da tabbacin cewar zai nemeki ne,Amma muddin kika je bashi hakuri,wlh sai kinyi danasani ne,"
"Amma jahad,rashin kunya fa nayi mashi,yakamata na bashi hakuri in ba haka ba Zai gane cewa ina acikin hayyacina na gaya mashi magana,kuma zai dinga yi mun kallon mara kunya ƙarshe ma ya tsane ni gaba daya,"
Murmushi jahad tayi tare da cewa"indai bazai ta6a lafiyar jikinka ba toh da sauki,ƙwara yayi maki kallon mara kunyar,akan dai kije bashi haƙuri,nasan bazaki fahimce ni ba,A yanzu amma nan gaba zaki ga amfanin yin hakan da kikayi,"_
Zugudum sehrish tayi tana doubting akan abunda jahad ta faɗa mata,Anya kuwa jahad ba hanyar banza takeson ɗaurata ba?in ba haka ba saboda me zata hana ta zuwa bashi haƙuri,bayan itace mai laifi,A matsayin shi na mijinta kuma yayanta,bai kamata tayi mashi hakan ba,sannan kuma taƙi zuwa bashi hakuri,
Shigowar azmee ne ya katse mata zancen zucin nata,atare suka juya suna kallonta,
"An kammala breakfast,yana a dining yana jiranku,"
Ta karasa maganar tare da kai idanunta kan sehrish tace"Ya jikin naki"?
"da sauƙi alhamdullah,nagode ssai da irin kulawar da kuka bani,"
"Kada ki damu ae duk yiwa kaine,Amma naga kamar hawaye akan fuskarki,Ko haryanzu akwai ciwon ne"?
"A'a,naji sauƙi sosai,"
Murmushi azmee ta saki,kafin ta juya ta fuce daga ɗakin,
"Jahad kije kawai kuyi breakfast ɗin,Ni zan zauna a ɗakine,kada mu haɗu da babban yaya,Don nasan bazaiyi mun da kyau ba,"
"kada kisa damuwa aranki mana,duk kin bi kin tashi hankalin ki,Da yunwa zakiyi ta zama ne?bazaki ci komai ba"?
Shiru tayi ba tare da tace komai ba,
"Okey,zan kawo maki breakfast ɗin aɗaki sai kici hakan yayi maki"?
Ɗaga mata kai sehrish tayi"Eh,ki kawomin anan,zan fi samun kwanciyar hankali,akan in fita wajen,"
Saukowa jahad tayi daga saman gadon,ta buɗe kopa ta fuce daga dakin,
Ajiyar zuciya sehrish ta sauke,tunani ta shiga yi ko a wani hali babban yaya yake ciki,Yayi bacci jiya ko baiyi ba,Allah yasa dai kalamanta basu ta6a mashi zuciyarshi ba,
shigowa jahad ta kumayi hannunta ɗauke da madaidaicin tray,kayan tea ne sai chips da sauran abunda baza a rasa ba,Asaman drawer ta ajiye mata shi,sannan ta juya ta fuce daga ɗakin,
Matsawa tayi kusa da trayn,sannan takai hannu ta ɗauki cup of tea ɗin tana ɗan kur6arshi,
Cikin ƙankanin lokaci ta kammala yin breakfast ɗin nata,
Zama tayi cike da fargabar abunda zai biyo baya,
Ranta ne ya bata cewar,ta jaraba kiran aunty azeema ta sanar da ita abunda ya faru atsakaninta da sgr,may be ta samu shawara mai kyau a wurinta,
Da sauri ta ɗauki wayarta dake ajiye saman gadon,contact ta shiga ta lalubo numbarta,ta danna mata kira,tana fara ringing,Azeema ta ɗaga kiran nata,
Tunkafin tafara magana hajiya azeema tace"2 days ba hello ba hi ko?har kin fara mantawa dani ko,"
Murmushi sehrish tayi tare da cewa"ba haka bane,Aunty azeema kusan kullum ne saina nemi layinki,amma baya shiga,"
Azeema tace"Hakane fa,nifa wayata indai bani na kira mutun ba,da wuya ne a same shi,kullum busy nake,"
Shiru sehrish tayi tana tunanin ta ina zata fara kora mata jawabi,
"Ina sauraronki,Har yanzu ba wani cigaba a zamanki dashi"?_
Nan fa sehrish ta samu ƙwarin guiwar sanar da ita duk abunda ya faru atsakaninsu daren jiya,
Tayi tunanin aunty azeema zatayi mata faɗa ne,amma da buɗar bakinta sai cewa tayi"Very Good!hakan da kikayi mashi yayi mun dai dai wlh,"
Sakin baki sehrish tayi tamkar tana agabanta,kusan bakinsu ɗaya da jahad,
"Kada ki kuskura kije bashi haƙuri!nafi so ya gasgata kalamanki"
Cike da mamaki sehrish tace"Aunty azeema dagaske kike?kada na bashi haƙuri"?
"Ƙwarai kuwa,ina goyon bayan hakan ɗari bisa ɗari,kuma kada ki kuskura kije part dinshi da sunan aiki,Ki rabu dashi,dama ae yace kada ki koma mashi har saikin kammala kazantar kibarshi a hakan,kada ki wani ji tsoro,"
Lumshe ido sehrish tayi tare da ware su fuskarta da dan murmushi tace"Shikenan aunty azeema bazanje ba in sha Allah,"
"Namanta ban sanar dake ba,nafa dawo nigeria,tun jiya amma na wuce damaturu,bazan samu zuwa nan ba yanzu saboda abunda ya faru na rasuwar modibbo,amma kada ki damu zan bada saƙo ta wurin junaid,naji yace zai biyo Abusufyan idan ya tashi dawowa,zan bashi ya kawo maki har gida,Sannan zanyi maki bayanin yadda zakiyi amfani dasu,koda ta wayane,"
"Nagode sosai Aunty azeema,Allah yasaka da alkhairi,Amma yaushe zaki dawo nan?don nayi kewarki sosai,"
Dariya hajiya azeema tayi tare da cewa"Very soon zan dawo,"
Sehrish tace"to shikenan,Allah ya kaimu lokacin,"
"Ameen my daughter,"
Sun jima suna waya kafin daga bisani ta ajiye wayar,har hankalinta ya kwanta,duk da akwai sauran fargaba atare da ita,
saukowa tayi daga saman gadon,Wardrobe ta nufa,hannu tasa ta buɗe,Arab gown ce ta ɗauko pink colour,tare da mayafinta shima pink ne amma bai ciza ba,kamar na rigar,zura kayan tayi ajikinta,sannan ta koma gaban mirror ta zauna,zuba ma mirror din ido tayi tana kallon fuskarta,ta cikin madubin,yayin da zuciyarta ke tariyo mata abunda ya faru adaren jiya,
A 6angaren Sgr kuwa,wata irin matsiyaciyar yunwa ce ta farkar dashi daga bacci,saukowa yayi daga saman gadon,Jallabiya ce ajikinshi,wuce wa yayi wurin closet ɗinshi,withins mins ya shirya kanshi cikin jeans da t shirt Maroon colour,rigar ta fito da surar jikinshi saboda ta ɗanyi tighting ɗinshi,Ƙafarshi na sanye cikin Canvas sneakers,
fitowa yayi daga part ɗinsa,Ya nufi downatairs,a natse yake taka staircase din har ya sauko down,Su jahad na zaune ita da hosana saman Sofa mai mazaunin mutun uku,suka jiyo takun takalmanshi,
ɗagowa sukayi atare suna kallonshi,lokacin da ya ƙaraso wurinsu,da sauri suka haɗa baki wurin gaisar dashi,
Batare daya kallesu ba,Ya amsa masu gaisuwarta su,fuce wa yayi daga cikin main palour ɗin,Kaitsaye Motarshi ya nufa,Amstrong na ganin shi da sauri ya ƙarasa tare da buɗe mashi motar ya shiga daga ciki,sannan shima ya bude driver seat ya zauna,
Kafin ya tashi motar,ya ɗan dago tare da kallonshi ta cikon mirror yace"Sir,Where are we going"?
"Restaurant,"ya bashi amsa atakaice,
Shiru amstrong yayi batare daya tashi motar ba,Hakan yasa shi cewa"what are u waiting for"?
Cikin harshen turanci amstrong yace"Sir,kayi haƙuri da abunda zance,Amma zuwa restaurant ba naka bane,da matsayinka aganka a restaurant ka je cin abinci?kaida ya kamata ace a gida ake girka maka,idan ba damuwa zanje nakawo maka,ka koma ciki pls"
Tunda ya soma magana sgr yayi shiru yana sauraronshi,saboda amstrong yana ɗaya daga cikin waɗanda suke Control dinshi,"
Amsa mashi yayi da okey,sannan ya buɗe motar ya fuce,
Duk wannan abun dake faruwa sehrish na tsaye a wurin window tana leƙen motarshi,taga lokacin daya shiga cikin motar,kuma sai taga ya fito daga ciki,
Aranta tashiga tunanin ko lafiya,
Dawowa cikin gidan yayi,Part ɗinshi ya koma ya zauna saman sofa yana jiran dawowar Amstrong,dan bala'e ga abinci acikin gidan amma yafi ƙarfin yayi ma wani magana ya kawo mashi abincin,tunda ya ƙori mai aikin tashi,
Cikin minti goma sha biyar,Amstrong ya shigo cikin gidan hannunshi dauke da ledojin,Su jahad na ganinshi suka shiga gaisar dashi,fuskarshi ɗauke da murmushi ya amsa mashi,sannan ya wuce upstairs sashen sgr,
Yana barin wurin da gudu jahad ta nufi ɗakinsu,tura kopar tayi ta shiga ciki tana faman ƙwala ma sehrish kira,
tsaye ta same ta hannunta ruke da wayarta,ganin jahad ta faɗo ɗakin babu sallama yasa tace"Lafiya"?
Jahad tace"Yanzu naga wannan sojan wanda yake yin driving ɗin babban yayanmu,Hannunshi dauke da ledojin kuma na restaurant ne don naga sunan ajiki,"
Cike da mamaki sehrish tace"to fa!ko meyasa ya aika akawo mashi abinci bayan ga wanda aka girka agida"?
Jahad tace"Yanzu haka saboda abunda ya faru atsakaninku ne jiya,shiyasa yaƙi cin abincin gidan,"
Jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,
"Yanzu haka,saboda yana ƙyamar girkina ne saboda ina yin period,shiyasa bazaici abincin gidan ba,"acewar sehrish,
Jahad tace"Amma ae bake kikayi girkin ba,Aunty azmee ce ta girka,Gaskiya nafi tunanin cewa wani abunne daban yasa bazaici abincin gidan nan ba,"
Murmushi sehrish ta ɗanyi tare da cewa"kinsan Allah babban yaya bazai iya cin abincin nan ba,Ina nan dake ƙarshe sai dai azubar da shi abanza"
Jahad tace"Mu zuba ido mu gani,zaici ko bazaici ba,"
***
Excuse sir!muryar amstrong ce ta dawo dashi daga zurfin tunanin da ya faɗa,
Muryarshi a kasalance yace mashi"Come in,"
Shiga ciki yayi tare da ajiye mashi asaman table dinshi,Sannan ya sara mashi,kafin ya fuce daga ɗakin,
Kusan minti 5 bai motsa ba,kamar ba yunwa yake ji ba,Hannu yasa tare da curo bugger daga ciki,yana ƙokarin kaita a bakinshi ,Ya tuna da jinin daya gani ajikin wandon sehrish,aikuwa nan take Ya sake ta ta faɗi saman table din,Wani irin yunƙurin amai ne ya taso mashi,da sauri ya miƙe ya nufi cikin toilet,ya shiga kwara amai agaban basin,Ba ƙaramin galabaita yayi ba,ƙyanƘyami ya hana yaci abincin ga yunwa na cinshi,har zazza6i ya fara kamashi,
Tap ya kunna ruwa ya shiga kwararowa,tarba hannayenshi yayi ya shiga kuskure bakinsa,kafin ya wanke face ɗinshi,
Fitowa yayi daga cikin toilet,yana faman sauke ajiyar zuciya,komawa yayi saman gadonshi ya kwanta,wasa wasa Zazza6i ya rufe shi,temperature ɗin jikinshi yayi zafi sosai,
Kasa samun natsuwa sehrish tayi,tunda taga an kira sallar magrib da isha'e,sgr bai fito daga part ɗinsa ba,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankalinta yayi ba,jiki na rawa ta fito daga ɗakinsu ta wuce kitchen,Anan ta samu azmee tana ƙarasa gyara kitchen din ita da hosana,
Ganinta yasa azmee tace"Ya jikin naki"?
"Da sauƙi aunty azmee,sai dai...."shiru ta ɗanyi bata ƙarasa maganar ba,
Tunkarota azmee tayi tare da ruƙo hannunta suka ja daga gefe sannan tashiga tambayarta meya faru,
"Aunty azmee,wani abu ya faru jiya tsakanina da babban yaya ban sanar maki ba,"
"Faɗamun meya faru,Allah yasa dae ba wani laifin kika aikata masa ba,"
Nan sehrish ta kwashe duk abunda ya faru ta sanar mata,
"Ya salaam,' azmee ta ambaci hakan hankalinta aɗan tashe tayi maganar,
"Wlh aunty azmee ba laifina bane,bana acikin hayyacina ne,shiyasa nayi mashi rashin kunya,"
Muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,
Cigaba da magana tayi"Ni babban abunda yafi tayar mun da hankali,har aka kammala sallar magrib da isha'e,banga ya fito daga cikin part dinshi ba,kuma inajin tsoran in tunkare shi,saboda nasan dole ya hukunta ni,kuma nayi shawara da aunty azeema tace kada na kuskura naje bashi haƙuri,haka jahad ma tace mun,"
"Sehrish idan kikace zaki ɗauki shawarar Azeema,zata kaiki ta baroki ne,saboda ita wata irin wayayyiyar maca ce,Bazan hana ki ɗauki shawararta ba,amma inaso ki tuna matsayinshi a wurinki,Yayanki ne shi kuma Mijinki,jiya ya kwana da fushinki acikin zuciyarshi haka yauma ya tashi da fushinki,tabbas zaki jefa kanki cikin matsala ne,in har bakiyi hanzarin neman afuwarsa ba,Yakamata kije ki bashi haƙuri,kuma ki sanar dashi cewa ba a hayyacinki kike ba!"
. "yanzu aunty azmee kina nufin inje in bashi haƙuri"?
"Eh,haka nake nufi,"
"Amma fa yace mun kada na kuskura na ƙara zuwa part ɗinshi har saina kammala period ɗina,"
"Kada ki damu da wannan kije kawai,in sha Allah babu abunda zai faru,"
Tashin hankalin da ba'a sama shi date,Shin shawarar wa kuke tunanin zatayi ma sehrish amfani?Shawarar Azeema da Jahad,ko kuwa shawarar Aunty Azmee, 💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*
*Father of soldiers*
*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*
_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana ta whatsapp dan Allah banda kiran wayar,bana ɗagawa 08103884440❤_
Nagode da shawararki Aunty azmee,in sha Allah zanyi amfani da ita"
"Yawwa haka nake son ji" azmee tayi maganar tare da komawa cikin kitchen,Sehrish kuwa bata wuce part ɗinshi ba,bedroom ɗinsu ta wuce,sam takasa samun natsuwa,ta rasa shawarar wa zata ɗauka acikinsu,bakomai yafi sata fargaba ba,fa ce abunda zai biyo baya idan tayi kuskuren zuwa sashen shi,
Har wuraren ƙarfe goma sha biyu na dare bata runtsa ba,tana zaune saman gadon nasu,yayin da wayarta ke ruƙe a hannunta,Hosana na kwance a gefenta tana bacci cikin bargo hankalinta kwance,Jahad kuma na can ɗakin azmee,
Wani tunani ne yazo mata acikin zuciyarta,da sauri ta shiga contacts ta lalubo layin Aunty azeema,ta danna mata kira,cikin sa'a ta ɗaga kiran nata,
Kara wayar tayi a kunnanta,tare da yi mata sallama,
"Assalamu Alaikum,"
Aunty azeema tace"Wa'alaikum salam daughter,me kikeyi har yanzu baki yi bacci ba,"?
"Na kasa yin bacci ne,ina cikin damuwa"acewar Sehrish,
Azeema tace"kodai duk fargabar babban yayan naku ne?
"Ba haka bane,Aunty azeema,na ɗan shiga damuwa ne,yau babban yaya bai fito daga part ɗinshi ba,har akayi sallar La'asar da magrib,bai fito ba,"
Maganar sehrish ta ɗan tashi hankalin hajiya azeema,
"Amma ya ci abinci kuwa"?
Sehrish tace"baici abincin gida ba,ɗazu dai yasa an kawo mashi abincin restaurant,amma bani da masaniya akan yaci ko bai ci ba,"
Shiru hajiya azeema tayi na wani dan lokaci,haka itama sehrish ɗin,Kowa da abunda yake saƙawa aranshi,
"Kina jina"muryar hajiya azeema ce ta katse mata zancen zucin da ta shiga,
"Ina sauraronki Aunty,"
"Gaskiya akwai matsala,saboda ba ƙaramin abu bane zai hana Sgr zuwa masallaci ba,Ina da tabbacin cewa zuciyarshi ta motsa,Allah kaɗae yasan halin da yake ciki,gashi babu kowa agidan idan baku ba,dama ace su Abbanku suna nan ne ko Omar zasu iya shawo kan matsalar,Amma yanzu haɗari ne wani ya tunkare shi,tunda ba'asan halin da yake ciki ba,wani irin zafin zuciyane dashi idan ya fusata kowa tsoran tunkararshi yake yi,Amma idan akaci sa'a,Ya yanke jiki ya faɗi ya suma a lokacin da zuciyar tashi ta motsa,to tabbas koda ya farfaɗo bazai tashi da wannan fushin ba......"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar,tana sauke ajiyar zuciya,
"Yanzu ya zamuyi kenan"?sehrish ta tambaya,fuskarta dauke da damuwa,
"Abunda za'ae yanzu shine,inaso kije part ɗin nashi kiga a wani hali yake ciki,Amma fa kada ki bari ya ganki,a 6oye zaki je,in ba haka ba a tsinto ƙasusuwanki a dakinshi,"ta karasa maganar cike da zolaya,
Dariya sehrish ta dan yi duk da tsoron daya kamata,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Shikenan Aunty azeema,zanje in sha Allah,"
Azeema tace"yawwa daughter,idan kin dawo duk abunda ya faru ki sanar dani pls,"
"Toh Aunty,"
Daga nan sukayi sallama,saukowa daga saman gadon Sehrish tayi,bayan ta ajiye wayar saman side drawer,ta zura slipper ɗinta dake ajiye nan ƙasan,ta gyara mayafin jikinta sannan ta fito daga dakin nasu,
Tunkafin ma ta hau upstairs din gabanta ke faɗuwa rass rasss,tamkar wadda zata tunkari wani zombie,
A hankali take taka staircase ɗin harta samu ta haura sama,tana tafiya tana ambaton"La'ilah ha illa antas subhanaka inni kuntu minazzalimin,"har tazo bakin ƙopar part dinshi,kamar wata 6arauniya haka ta leƙa cikin falon,ganin baya ciki yasa ta sauke ajiyar zuciya,cikin sanɗa ta zura ƙafarta ciki,a hankali take tafiya,gudun kada yaji sautin takalminta yasa ta zuƙunna tare da ciresu ta ruƙesu a hannunta,
A ƙopar bedroom ɗinshi ta tsaya,har lokacin bata daina ambaton La'ila ha illah anta subhanala inni kuntu minazzalimin,acikin zuciyarta ba,saboda tsabar tsoro,zuciyarta tamkar zata fito daga ƙirjinta,saboda bugun da take yi mata,daraam!daraaam,
A hankali ta ɗan zura kanta tare da leƙawa cikin ɗakin nashi,
Kwance yake saman gadon,gangar jikin na asaman gadon,yayin da head ɗinsa zuwa wuyanshi suka zuro daga gefen gadon,Sumar kanshi ta zubo har saman floor,
Gabanta ne ya faɗi rasss!tun daga kan yadda yayi kwanciyar ta gane cewa babu lafiya,gaba ɗaya zufa ta wanke jikinshi tamkar wanda ya watsa ruwa ajikinshi,ta ko'ina zufar ke tsastsafo mashi,gaba ɗaya ga66an jikinshi sun sake,
Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,batasan ko bacci yake yi ba,ko suma yayi,Allah wa'alamu,
Zura ƙafarta tayi yayin da gabanta ke ci gaba da faduwa,Shiga cikin bedroom ɗin tayi,har zuwa wurin gadon nashi,Yanayin kwanciyar tashi ma,Zata iya haifar mashi da matsanancin ciwon wuya,saboda yadda ya yi sadda kai,
Zuba mashi ido tayi tana kallon fuskarshi,daga gani ba ƙaramin jiki yaji ba,
Tunani ta shiga yi,kodai