Showing 333001 words to 336000 words out of 432432 words

Chapter 112 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete

zauna,tana ci gaba da sauraronta,

"abunda nakeso dake,kada ki ji tsoron komai,ki natsu ki kwantar da hankalinki,ki rubuta mashi duk wani abu da kika sani wanda baki so yana yi maki,wannan dama ce kika samu,"_
   Ajiyar zuciya ta sauke tare da gyaɗa kai tace"shikenan,Zan rubuta mashi yanzu,"
  "Yawwa my daughter,take care of ur self for me,Sai kinji daga gare ni,"
  Daga nan sukayi sallama tayi rejecting kiran,
   Juyawa tayi gefen hagunta tare da kallon jahad tace"Juliet,inason magana dake,idan kin kammala wayar,"
  Juyowa jahad tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Ae mun kammala yin wayar ma tun ɗazu,wayarce kawai ban cire a kunne na ba,saboda ban gajiya da jin Voice ɗinshi,Expecially idan yanayi Mun shagawa6ar nan tashi,kamar in janyoshi ta cikin wayar,in manna mashi kiss,"
  Fashewa Sehrish tayi da dariya,gami da girgiza kai,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Gaskiya ne,Juliet Matar Romeo,abun naku azimunne,"ta ƙarasa maganar a yayin da take komawa gefen gadon ta zauna,kafin ta kuma cewa"Am looking for ur advise,My lovely sis,"jin haka yasa jahad ta miƙe zaune daga kwancen da take,ta jingina bayanta jikin head board ɗin gadon,tana facing sehrish sannan tace"Shawarar me kike so in baki ne"?
  Calmly sehrish tace"yau naje bama babban yaya haƙuri,Kinsan meya faru"?
Hankali aɗan tashe jahad tace"Sae kin faɗa,"
  Murmushi sehrish ta ɗan saki kafin ta cigaba da cewa"bai yi mun komai ba,ko yatsa bai ɗaga mun ba,Yanzu haka ma zancen da nake maki,Yace na rubuta mashi text message na duk abunda banso yana yi mun,"_
  Wani irin ihun farin ciki jahad ta saki tare da furta"Yess!yess!"da alama abun ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,
   "Wlh naji daɗi sosai!dama nifa koda nace kada kije ki bashi haƙuri saboda tsoran karya Bugeki ne,Amma yanzu Alhamdulillah,komai ya wuce,gashi har an samu ci gaba,"
"Yanzu me kike ganin ya dace na rubuta mashi?Mommy azeema tace kada naji tsoran komai na rubuta duk abunda nake so ya daina yi mun,"
Murmushi jahad tayi,tare da cewa"ta kwana gidan sauƙi,Ae yanzun nan zamu tsara mashi text message,Amma inaga kamar mu rubuta mashi ta whatsapp ko?zaifi tsayi rubutun ba kamar na text message ba,
  Sehrish tace"Ni damuwata ma,kada musha wahalar rubutawa yaƙi karantawa,Saboda na ta6a tura mashi message,bai rubutomin reply ba,"
  Jahad tace"kinsan shi mutunne mai jama'a,mutun mai farin jini irinshi bazai rasa dubban saƙonnin Masoyanshi ba,Shawarar da zan baki shine,Idan kin rubuta mashi message ɗin saiki jaraba kiran layinshi,idan ya ɗaga saiki sanar dashi cewa kin tura mashi,"
  Jinjina kai Sehrish tayi,"kin kawo shawara mai kyau,"
  "Yanzu dame dame Yake yi maki wanda bakya so"?Jahad tayi tambayar tana kallon fuskar Sehrish dake kallonta,
  "Abu na farko,nidai bana son wannan tsawar da yake yi mun,na biyu bana son tsallan kwaɗin da yake sanya ni don ba ƙaramar wahala nake sha ba duk in nayi shi,Na uku kuma,banason yana hana ni zuwa part ɗinshi da make-up a fuskata....,"haka Sehrish ta shiga lissafa mata abubuwan da bataso,Bakomai yafi bama jahad dariya ba,fa ce Make-up da sehrish tace bata so yana hanata,cike da zolaya tace"in banda abunki,bashi kike yiwa kwalliyar ba?kuma yace bayaso,sae ki daina kawai,Kinsan ba ko wani namiji bane keson wannan ƙyaleƙyalen namu na mata,wani namijin ma baison ƙamshin turare,kowa fa da irin nashi ra'ayin,"
  Harara sehrish ta ɗan wurga mata tare da cewa"Amma lokacin baya before wedding ɗinmu,ina yin make-up in shiga part ɗinsa bai ta6a hanani ba,sae bayan da aka ɗaura auren,"
Jahad tace"saboda yanzu ne yake da cikakken iko akan ki,Shiyasa ya hana ki,'
  Ta6e baki sehrish tayi kafin ta mayar da idanuwanta kan wayar,Ta shiga whatsapp ɗinta,Contact ɗinsa ta nemo wanda tayi mashi saving da *My Boss man*,ta shiga Cikin Chat ɗinsa,sau ɗaya ta ta6a yi mashi sallama,bai duba ba,"
  A hankali ta soma rubuta mashi saƙon,
   "Sehrish,me zai hanaki ki ɗan rubuta mashi cewa,ya dinga sakar maki fuska,koda bazaiyi murmushi ba"?
  Wani bazawarin kallo sehrish ta jefa ma Jahad,a ƙule tace"idan ya tashi cin ubana,ae baki a kusa balle ki kawo min agaji,Ni na isa in sanya wannan fuskar tashi,ta dinga yi mun murmushi,?kina ganin ko su Abba in yana tare dasu baya murmushi,shifa naturally haka face ɗinshi take,a tamke,"
Dariya jahad tayi tare da kai hannu ta dafa shoulder ɗin Sehrish "Kada ki damu My own sister,Very soon fuskar yaya rafayet,zata koma kullum a washe,amma fa sai ranar da kika haifa mashi baby,"
  Fashewa tayi da dariya,jin abunda jahad tace mata,
  Can kuma tace"Anya,Babban yaya yana son ƴa'ƴa kuwa?irinsu fa kamar basu damu da haihuwa ba,yawanci ma basu son matansu su haihu,Akwai wani American film dana ta6a kallo,Bature ne mutumin har yakai shekara 80 bai ta6a haihuwa ba,Saboda yana da wani ɗan karensa,shiya ruƙa a matsayin ɗansa,yawanci kuma zaki ga basu son haihuwa da yawa,ɗaya zuwa biyu,sae kiga sun kwallafa rai akan ƴa'ƴan nan,"
  Jahad tace"Amma shi Half cast ne!(ruwa biyu)ba dole bane komai ace irin nasu ya ɗauko,Duk da yafi ƙarfi ta 6angaren Mommynsu,kuma acan ya taso duk ɗabi'unsa da halayansa,in kika lura irin nasu ne,Amma daga gani kamar zaiso ƴan babies,ke in ma baiso,to akan ki zai fara son ƴa'ƴa,"ta ƙarasa maganar tana dariya
Murmushi sehrish tayi a yayin da idanuwanta ke akan screen ɗin wayarta,har tayi nisa cikin rubuta mashi saƙon,
  "Jahad,bansan meyasa kikeso in samu ciki ba,kullum baki da zance sai na in samu ciki,in haifa ma babban yaya baby,bayan kinsan cewa nan da wani ɗan lokaci auren zai mutu,"tayi maganar muryarta a sanyaye,
  Jahad tace"saboda na ta6a yin mafarki ne,kuma acikin mafarkin na ganki da ƙaton ciki,sai gashi kuma kin haihu,Kinsan me?tayi tambayar batare da tajira amsar sehrish ɗin ba taci gaba da cewa"babyn da kika haifa Triplets ne kuma dukkansu maza ne,Ƙwayar idonsu blue ce kalar ta babban yayanmu,gashin kansu ma kwantacce ne irin nashi,hasken fatarsu da komi irin nashi ne.....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda jin saukar pillow da tayi asaman fuskarta,wanda Sehrish ta jefa mata shi,
  "Maƙaryaciya kawai,daga jin wannan ƙirƙirarran labari ne,babu wani mafarkin da kika yi,"_
  Dariya sosai sukayi,ba ƙaramin nishaɗi suka samu ba
Bayan ta kammala rubuta mashi saƙon,Miƙa ma jahad wayar tayi don ta duba ta gani in akwai abunda ya dace su ƙara,Kar6ar wayar jahad tayi tana karanta message ɗin har yazo karshe,Sannan tace"komai yayi yadda akeso,tura mashi sakon sai ki kirashi,"
  Tura saƙon sehrish tayi bayan ta kunna WI-FI ɗinta,nan take saƙon ya isar mashi,phone call ta shiga tare da danna mashi kira,
   Kusan sau biyar tana kira ba'ayi picking ba,
Jahad tace"mu haƙura zuwa anjima yanzu haka suna aikine,"

*Boss Bature*

Wuraren ƙarfe 6 na marece,wata danƙareriyar mota tayi parking a cikin wani katafaren hotel,a parking space motar ta tsaya,jim kaɗan wata matashiyar budurwa ta fito daga cikin motar,jikinta na sanye da riga bubu ta material,ƙafarta kuwa na sanye cikin high hills,ta coge ɗaurin kallabin nan na rashin ɗa'a,Sae faman taunar cingam takeyi abakinta,
   Hannunta na ruƙe da ƴar purse ɗinta,ta sagala mayafin asaman kafadarta,
....fitowa wani matashi yayi daga gaban motar,daga ganinsa zakasan cewa ba ƙaramin shege bane,kuma tantirin ɗan iska,
  Zagayawa yayi tare da buɗe boot ɗin motar ya ɗauko mata trolley ɗin kayanta,sannan ya kalleta tare da cewa"Babe,Mu shiga ciki ko?in ɗan taka maki"
Murmushi Abrah,ta saki tare da nuna mashi hanya tace"bismillah,"gaba tayi yabi bayanta,suna tafiya yana yi mata sambatu,"Gaskiya zanyi kewarki sosai baby,bansan ya rayuwata zaka kasance ba,idan babu ke,zan zama tamkar maraya,"_
  Abra tace"hmm,dama ka daina yi mun wannan daɗin bakin naka wlh,Don na sanka,mayen mata ne,Allah kaɗai yasan yawan matan da kake mu'amala dasu,Ni bansan ma tanawa bace,"_
   "Subhanallah,Zargina kikeyi ma kenan?babu kyaufa,"
  "Ba zarginka nake yi ba,zahiran na gani ae,"suna magana suna tafiya har suka shiga cikin reception,mutane ne ke ta safa da marwa a wurin,Batare da sun sha wahala ba,ta hango Aunty babba tana tunkarosu,Fuskar nan aɗaure babu annuri,Amma tana hango saurayin da Abra tazo dashi,nan take ta ɗan saki fuskarta,ƙarasowa tayi wurinsu,
  "Sannunku da zuwa ya gajiyar tafiya,"
   Saurayin ya amsa mata"Alhamdulillah,Mun same ku lafiya,"
  "Lafiya lou,"kafin ta mayar da idonta kan abra tace"Wanene wannan kuma?yakamata a gabatar mun dashi,ko da yake bari mu shiga daga ciki,'tayi maganar tana yi masu nuni da hannunta,
  Saurayin yace"kash,bazan samu shiga ciki ba,ina sauri ne zan wuce wurin wani uncle ɗina dake anan,Urgently yake nemana,"
   Aunty babba tace"Amma banji dadi ba,duk irin wannan ɗawainiyar da kayi mana,bazaka shigo daga ciki ba ka huta,ko lemu ne ka ɗan sha,'
  "Kada ki damu Aunty,Idan kuka dawo daga tafiyar zanzo ne sai mu gaisa dakyau,"
   "Aunty wannan shine Bobby ɗin da nake baki labarinshi,Yana da kirki sosai,Saboda yana kyautatamun,"ta ƙarasa maganar,fuskarta dauke da murmushi,
  Aunty babba tace"Ma sha Allah,naji daɗin ganinka sosai,Allah dae ya nuna mana ranar aurenku,Musha biki,'
  Murmushi ya saki yana faman shafa keyarshi da hannunshi,
    "Bari mu shiga daga ciki,Sae munyi waya,"acewar Abra,
   "Okey babe,ki kulamun da kanki,Sae kinga saƙona,"
   Ya ƙarasa maganar tare da juyawa yabar reception din,Aunty babba tayi gaba Abra tabi bayanta,Har izuwa cikin ɗakin da ta kama,
    Suna shiga cikin ɗakin abra ta saki trolley din kayan,ta faɗa saman gadon ta kwanta tana faman sauke ajiyar zuciya,
    Daga gefen gadon Aunty babba ta zauna,tare da kallonta tace"kun sha tafiya,toh ya ku ka baro su mammyn'?
  "Tana can,rai hannun Allah,ae na faɗa maki cewa bata da lafiya,Amma da sauƙi dae,tunda tana ɗan mikewa har ma ta zauna,Matsalar dae babu mai kula da ita,Shima Abie ya tattara yana shi yana shi yabar gidan,yanzu ita kaɗai ce acikin gidan,bansan ya zata ƙare ba,"hankalinta kwance take yin maganar,
  Shiru Aunty babba ta ɗan yi,batare da ta janye idanuwanta daga kan fuskar abra ba,
  "Aunty kinyi shiru,ba kice komai ba?wai nikam Ina Aunty hayaam ne'?nayi tunanin zan ganku atare ne,kuma nayi mamakin ganinki a hotel"
   Harara ta ɗan watsa mata tare da cewa"in ba a hotel ba,a ina kikeson ki ganni ne?Ko bakisan cewa aure na ya mutu ba"?
...ƙumshe dariya Abra tayi,
    "Kiyi mai isarki lokacinki ne ƴar rainin hankali,Muna nan cikin tashin hankali,ke kina can kina holewarki,wato kin samu duniya ko"?
  Turo baki abra tayi tana fadin"matsalar kenan fa,yanzu nasha wahalar tafiya,ko ruwa ban sha ba,Amma zaki fara yi mun faɗa,Allah in naji ban iyawa,sae dai ki neme ni ki rasa,"
   Sakin baki Aunty babba tayi tana kallonta,kafin tace"lallaine wuyanki ya isa yanka,fiye da haka ma zaki iya faɗamun,"
    murguɗa baki abra tayi tare da cewa"na tambaye ki Aunty hayaam amma baki ce komai ba,tana ina,"?
   Ta6e baki Aunty babba tayi kafin tace"Ae hayaam ni kaina bansan inda take ba,kinsanta bata gajiya da yawo,yau kusan kwana uku banganta ba,sae dai ta kirani mu gaisa,Amma ni kona kirata a kashe nake samun wayarta,"
  Saboda rashin tsoran Allah,Aunty babba ta zauna tana shirgawa Abra ƙarya,don tasan cewa muddin Abra taji cewa,hayaam na kwance gadon asibiti ba lafia,baza ta ta6a yarda suyi tafiyar nan da ita ba,Sai ta tsaya tayi jinyarta,kuma in taji cewar ta bar ƴar uwarta a asibiti babu mai kula da ita,to tabbas ranta zai 6aci sosai,"
   "Kai Aunty hayaam,ita ma dae kamar wadda taci ƙafar kare,bata nan bata can,"
  Aunty babba tace"Ni duk ba wannan ba,Kinsan dai dalilin dayasa nace kizo ko"?
  "Eh nasani,"ta bata amsa,
"Yawwa,Jibi nakeso mu shirya mu tafi,lokacin kin huta sosai,"
  Yatsina fuska Abra tayi,tana ɗan gatsina hanci tace"Oh ni,yanzu haka zamu kwasa mu tafi wurin boka har enugu,cikin dajin Allah,Kamar waɗanda basu da mafaɗi,Kuma dae babu tsoran Allah..... "
  Tunkan ta ƙarasa maganar Aunty babba tace"Rufe mun baki,Uwar surutu sai kace aku,Duk ba don ku akeyi ba?don rayuwarku tayi kyau," fuskarta aɗaure tayi maganar,
  Zumbura baki abra tayi,tare da yin ƙasa ƙasa da muryarta tace"mutun yayi sallar dare mana,ya roƙa wurin wanda ya halicce shi sai wani boka can"
  "Me kikace"Aunty babba tayi tambayar tana kallonta,Don tajiyo ƙusƙus ɗin da take yi,
 Abra tace"Ni Bance komai ba,idan ma nayi magana to akan abinci ne,yunwa nake ji,"ta ƙarasa maganar tana shafa stomach ɗinta,
   "Okey,bari nayi mana order,sae muci atare,don nima banci komai ba,"
  
Wuraren ƙarfe 7,Motoci guda biyu suka shigo cikin gidan a jere,a lokacin Jahad da Sehrish suna a kitchen tare da Aunty azmee suna tayata aiki,Azmee na agaban gas cooker,Sehrish da jahad,suna yanke yanken kayan lambu,
  Jin dirar motacin nan yasa Sehrish saurin cewa"Ga babban yaya nan ya ƙaraso gida,"
  Jahad tace"Anya kuwa shi ne?Junaid fa ya sanar dani cewa yau ko gobe zasu dawo,Allah yasa su ne,kada abunda na haɗa mashi ya lalace,"
  Murmushi sehrish ta saki,tana cewa"Mrs romeo,Ae koda bai dawo ba,mu zamu cinye kayan daɗin da kika haɗa mashi,".
  Muryar azmee suka jiyo daga bayansu tana cewa"Nima hadani za'aci daɗin,"
  Dariya su kayi gaba dayansu,
Jahad tace"idan zaki ci Aunty azmee babu damuwa,Amma Allah koda bai dawo yau ba,ƙwara na zuba shi a dustbin da dai inba su rishi suci"
  Harara sehrish ta ɗan watsa mata da yake suna facing ɗin juna na,tace"saboda baƙin hali irin na ɗan adam,'
   "Aunty azmee ina da tambaya dan Allah,"acewar jahad,
  Azmee tace"Allah yasa na sani,"
Murmushi jahad ta yi tare da cewa"Tsakanin babban yaya da Junaid waya fi wani kyau,"
  Har sai da gaban azmee ya faɗi rass,Saboda girman tambayar da tayi mata,jinjina kai tayi na wani lokaci kafin tace"tashin hankali,Kuma ni kike so in amsa maki tambayar,"
  Jahad tace"Eh,saboda nasan kinsan menene kyau,zaki iya fadin wanda yafi kyau acikinsu,"
  Sehrish tuni ta dakata da yankar lettuce ɗin da takeyi,hannunta ruke da wuqa,duk ta qagara taji amsar da azmee zata basu,
  "Ni ko a school,ban ta6a haɗuwa da question mai wuyar Amsawa ba irin wannan,To ae dukkansu kyawawane na bugawa a jarida,Junaid kyau rafayet kyau,"
  Dariya sukayi jin yadda azmee keta nanata maganar,da alama sun caza mata kai,
   "Amma ni a ganina,kamar junaid yafi kyau,saboda shi fuskarshi kullum asake take,Kuma wannan murmushin nashi ba ƙaramin kyau yake ƙara mashi ba,"acewar Sehrish,
Jahad tace"Amma ae bai kai yaya rafayet tsayi ba,duk da shi ma dogone,kuma baida irin surar jikin babban yayan mu,"
  Sehrish tace"Ae da ace shima junaid ɗin zai dinga motsa jiki,in a short time zaki ga ya koma kamar babban yayan mu,ae su maza daga sun fara ɗaga ƙarfe Jikinsu ke buɗewa,"
  Azmee tace"hakane kema kince wani abu anan,Gaskiya dukkansu zan iya cewa babu wanda yafi wani kyau,idan don saboda murmushi zaisa junaid ya ɗare rafayet a kyau,to ae shima rafayet ɗin idan yayi murmushi sai kin kusa zaucewa,kilan bai ta6a yin murmushin bane kun gani,sannan kuma ga surar jiki ta ko'ina dae su duka biyun sai dai ace ma sha Allah..."zugudum sehrish tayi tana sauraron abunda azmee ke cewa,aranta tace"Kutmelesi,Su Aunty azmee har ansan su babban yaya nada kyawun sura,da kyakkyawan murmushi,ba dai kalle mun mijina takeyi ba,"ta ɗan yi maganar hada tamke fuska,can kuma ta fashe da dariya...,

  Suna cikin tattaunawar nan,Suka jiyo Muryar Junaid yana sallama,aikuwa jiki na rawa jahad ta ajiye knife din dake hannunta,da gudun gaske ta fito daga kitchen din,
  Yana a tsaye,jikinshi sanye da shadda brown colour,hannunshi ruke da trolley,fuskar nan ɗauke da ƙayataccen murmushi,duk a tunaninta shi kaɗai ne,hakan yasa ta nufe shi da gudu zata rungume shi,ƙiris ya rage ta ƙarasa,Sae ga Marshal Omar da Uncle abusufyan sun shigo,da sauri taci burki,tana faman sauke ajiyar zuciya,Fashewa junaid yayi da dariya yana kallonta,saboda ya gane abunda taso tayi,Su uncle sunyi mashi buƙulu,
.....hannu tasa ta rufe fuskarta,tana dariya,
Murmushi marshal ya saki,haka shima abusufyan ɗin,Jahad sarkin kunya,
   Fitowa sehrish tayi daga cikin kitchen ɗin,fuskarta ɗauke da murmushi,da sauri ta ƙarasa wurin abusufyan,hugging ɗinshi tayi tare da cewa"sannu da dawowa Daddy,ya gajiyar tafiya,"?ta ƙarasa maganar tare da ɗagowa daga jikinshi,
Hannu yasa tare da shafa fuskarta yace"lafiyalou My Daughter fatan na same ku lafiya,"yayi maganar yana miƙa ma jahad hannu,cike da jin kunya ta ƙarasa wurinshi,ya rungumota ajikinshi,
  Marshal Omar yace"Oh ni,babu mai yin hugging dina,daddynku kawai kuka sani,babu komai nasan da hosana na nan,da gudu zata bani hug" dariya sukayi gaba ɗayansu,haɗa baki sukayi wurin gaishe dashi,Ya amsa masu fuskarshi a sake,
  "Lah ya Omar,"muryar hosana ce ta katse su,ɗagowa su kayi gaba ɗaya suna kallonta,Da alama daga bacci ta taso,sae faman lumshe ido takeyi,
  Kai tsaye ta tunkarosu,kamar yadda yayi tsammani,ko Daddynsu bata runguma ba,wurinshi ta wuce,ta rungumeshi tare da kwantar da kanta saman wide chest ɗinshi,'
  Jinjina kai Abusufyan yayi tare da cewa"Hosana ko kallo ban isheki ba ko?,hankalinki na akan Omar," Yayi maganar yana kallonta,
   Murmushi ta saki tare da ɗagowa daga jikin Omar ta koma wurinshi,zata rungumo shi da sauri yaja da baya yana cewa"bana so,babu ruwana dake,ki koma wurin Omar ɗin,Ae ni baki damu dani ba,burina kawai in dawo gida don saboda ke,Amma shine kika watsa mun ƙasa a ido,"
  Dariya suka shiga yi gaba dayansu,hosana kuwa bubbuga ƙafa ta shiga yi muryarta tamkar zata yi kuka tace"pls daddy,let me hug u,wlh nayi missing ɗinka sosai,kawai dae nayi alƙwarin cewa,zan fara tarbar Ya Omar ne kafin kai,kuma banso in karya alƙawarin dana ɗauka,"
   Abusufyan yace"ae gashinan ko?Dama na yafe mashi ke,Ni ga ƴan tagwaye na nan,su da suka damu dani,'yayi maganar yana nuna su sehrish,
  Zumbura baki tashiga yi,tana murmura masu baki,
  Ruko hannun Omar tayi tare da jan shi tace"Mu tafi ya Omar,kayi wanka kaci abinci,Sannan ka kwanta ka huta,"Bin bayanta Omar yayi fuskarshi ɗauke da Murmushi,
  Girgiza kai Abusufyan yayi tare da cewa"Allah ya shirya min ke Hosana,Abun naki sai addu'a,"
  Ya ƙarasa maganar tare da ruƙo hannayensu Sehrish suka wuce cikin palourn,sun ɗan zauna anan suka ƙara gaisawa da daddyn nasu kafin daga bisani,suka barshi ya wuce bedroom ɗinshi don ya huta,

Wuraren ƙarfe 12 na dare,lokacin har sun kammala dinner ɗinsu tuni,Sun koma cikin bedroom ɗinsu,batare da 6ata lokaci ba,Su ka shirya cikin kayan baccinsu,sun kwanta ajere cikin lallausan bargonsu,
  Kwankwasa ƙopar ɗakinsu akayi kwankwan,
    "Wanene"?jahad ce tayi tambayar,saboda itace ta rage  idonta a buɗe,
  "Zo ki buɗe mun kopa,"da sauri ta saukko daga saman gadon jin muryar junaid,
  Hannu tasa tare da buɗe kopar,Yana tsaye cikin sleeping dress dinsa white colour,hannunshi ruƙe da Shopping bag,". 
  Junaid dama ba kayi bacci ba?tayi tambayar tana ƙare mashi kallo,sae hamma yake saki,
   Ashagwa6a yace"Na fara bacci mana,Mommy azeema ce ta tashe ni,saboda kawai wannan saƙon na rishi da tace na kawo mata,"
  Yayi maganar yana nuna mata ledar hannunshi,
   "Eyya,Amma banji daɗi ba,but am sorry,kawo saƙon na ajiye mata,don har bacci ya ɗauketa,"
  Miƙa matar bag din yayi,ta sanya hannu ta kar6a,sannan ta juya zata shiga ciki,da sauri ya ruƙo hannunta tare da janyota ta faɗo jikinshi,hugging ɗinta yayi tightly tare da cewa"I really missed u my Juliet,"
  Lumshe ido

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login