Showing 348001 words to 351000 words out of 432432 words

Chapter 117 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete

take away na restaurant,
  Da sallama ya shiga cikin falon,wuce wa bedroom ɗin yayi,ba ƙaramin mamaki yayi ba,ganin yadda Jahad ta gyara ɗakin tsaf,komai yayi fess,kamar lokacin da Zainabun shi na nan,
  Murmushi ya saki tare da samun wuri kasa gefenta ya zauna,Ya ajiye ledojin,Hannu yasa abayanta ya ɗan bubbugi kafaɗarta"Jahad!tashi muci abinci,"
  Firgita tayi ta farka tana Sambatu"Ya Rafayet,baisan na taho ba...,"
  Ƙiris ya rage yaji abunda tace,
Hannu tasa da sauri ta toshe bakinta,tana kallonshi,Shima kallon nata yake yi,
   "Me kika ce"?girgiza mashi kai ta shiga yi,tana faɗin"bakomai Daddy,Ashe ka dawo,nagaji ne shi ne na ɗan kwanta don in huta,"
  Murmushi yayi tare da cewa"Ae naga aikin da kikayi,kin yi ƙoƙari sosai,"
  "Bari na ɗauko mana plate,"ta miƙe tare da nufar hanyar fita daga ɗakin,
  Sai da tafito sannan ta dafe saitin zuciyarta tana faman sauke ajiyar zuciya,a ranta tace"Allah yaso daddy baiji abunda nace ba,dashi kenan zai gano ni,"_
Tayi maganar tare da yin saurin wuce wa cikin kitchen ɗin,A cikin kwandon wanke wanke ta samu tray da plates tare da cups,gaban basin taje ta wanke su tass da klin da soso,ta ɗaurayo su,bayan ta kammala wankesu saman tray din ta jera su,Ta ruƙosu a hannunta sannan ta dawo cikin bedroom ɗin,
  "Salamu Alaikum"Ta kwaɗa sallama ta shiga ciki,Zuƙunnawa tayi ta ajiye trayn agaban Abusufyan,
  Janyo ledar tayi ta buɗe,tare da sanya hannu ta curo fried meat(tsiren nama)ta jera masu shi asaman tray,hannu yasa ya taimaka mata wurin ɗauko sauran kayan,Cool Drinks ne da sauran kayan maƙwalashe,atare suka shiga ci suna fira gwanin ban sha'awa,bayan sun kammala cin abincin,Abusufyan ya tattara kayan abincin da sukayi amfani dashi,Ya wuce dasu kitchen yabarta zaune tana shan lemu,bayan ta shanye,ta sanya robar a dustbin,komawa tayi saman gadon ta kwanta,cikinta yayi haƙe² saboda cin muguntar da ta yi,wani baccin ne ya sake ɗaukarta,

*Boss Bature*

  ❤🤍❤

Wuraren ƙarfe 3 na rana Sgr ya dawo cikin gidan,Tun bayan da ya fita da safe Ko breakfast bai nema ba,saboda Emergency call ɗin da akayi mashi acan headquater ɗinsu,Jikinshi na sanye da Tank Top,light green,Tare da wandon kaki,Yayin da kunnanshi ke manne da wayarshi,Cikin harshen faransanci yake yin waya,
  Da sauri da sauri ya haye upstairs,direct ya wuce part ɗinshi,tunkan ya shiga ciki ya fara jin daddaɗan ƙamshi nakai mashi ziyara acikin hancinshi,gaba daya yayi tsammanin cewa zai same ta ne a part ɗin nashi amma baiga Kowa ba Wayaam,Bedroom ɗinshi ya shiga,Shaf shaf ya rage kayan jikinshi ya faɗa cikin toilet,After some minutes ya fito waist ɗinshi ɗaure da towel,Yana tsaye agaban mirror yaji motsin mutun acikin falonshi,
   "Who's there"?yayi tambayar yana jiran amsa,
  "Sehrish ce,"
Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da cewa"Come in,"
  Hannunta na ruƙe da tray na Lunch ɗinshi da ta shirya mashi,tana tafiya gabanta na faɗuwa rass rass
  Sallama ta fara yi mashi ya amsa,kafin ta sanya ƙafa ta shiga ciki,sum sum ta lalla6a ta ajiye mashi tray asaman table,Jiki na rawa ta juya zata bar ɗakin,
  Zuba mata ido yayi ta cikin mirror yana kallonta,tana ƙoƙarin ɗaga ƙafarta tabar ɗakin taji ya Ambaci sunanta kai tsaye"JAHAD"
  DARAAAM!!!!!!Taji gabanta ya faɗi,sanƙamewa tayi atsaye,hankalinta a matukar tashe,tuni zufa ta shiga wanke mata fuskarta,Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya abakinta,Abun ya ɗaure mata kai,farat ɗaya Sgr ya gane cewa ba Sehrish bace,Hatta junaid yau bai ganeta ba,kowa ɗaukar sehrish yake yi mata,saboda sunsa ma ransu cewa da jahad aka tafi,Shiyasa basu natsu sun gane cewa itace ba,"
   Wata irin zufa ce ta shiga gangarowa asaman fuskarta,ƙiris ya rage ta saki fitsari a wando,
Slowly ya juyo tare da tunkararta,jikinta sae kerma yake yi,hannunta ya ruƙo tare da juyo da ita ta gabanshi ya kasance suna fuskantar juna,wuƙi wuƙi tayi mashi da idanu tana faman mazurai na rashin gaskiya,
   Abun ya ɗaure mashi kai,Wai harshi zasuyi wa wayau,kamar wani soko,An gaya masu cewa a banza yakai muƙamin da yake dashi a yanzu,
   goya hannayenshi yayi asaman wide chest ɗinshi,Ya zuba mata ido yana kallon Ikon Allah,
   Saboda tsabar rashin gaskiya tun kafin ma yayi mata magana,murya na kerma tace"Amm...um..babban..yaya pls dan Allah kayi haƙuri ka yafe mun,Wayyo Allahna na shiga uku,"a ruɗe tayi maganar,tana yarfa hannuwanta,tsoranta kada ya kwashe ta da mari,
  Ruke ha6arsa yayi cike da mamaki yake kallonta from head to toe,
   Hawaye ne suka soma shararowa akan fuskarta,tun kafin ma taji hukuncin da zai yanke mata,Zuciyarta sae bugawa take yi ba ƙaƙƙautawa,
   "Where's she"?fuskarshi a ɗaure yayi tambayar,
  Sunnar dakai tayi kamar munafuka,daƙyar ta iya buɗe baki tace"Wlh baban yaya ni bani nace ta tafi ba,yau ne dama da asuba,ta same ni cikin damuwa take tambayata lafiya shi ne na sanar da ita cewa Ni banso nabi Daddy kano,bansan zuwa garin saboda abunda ya faru damu acikinshi...."
  Tunkan ta ƙarasa maganar yace"What!tafiya tayi without My Permission,"ranshi a matuƙar 6ace yayi maganar,
  "Ya salam"ya furta hakan tare da zura hannunshi cikin sumar kanshi,
Ya runtse idanuwanshi,
"Am sorry,babban yaya bazan ƙara ba,"_
Jinjina kanshi yayi tare da ware idanuwanshi akan fuskarta,yana kallonta duk tabi ta susuce,
   "Kin iya frog jump ko"?
Waro ido tayi tana kallonshi,girgiza kai tashiga yi alamar a'a,
...ruko hannunta yayi ya fito da ita cikin falonshi,fuskarshi a daure yace"Oya,start from here,karki kuskura ki tsaya,if not zaki ga abunda zai biyo baya,"
   Jahad tamkar zata fashe da kuka,Zuƙunnawa tayi tare da kama kunnanta kamar ɗan kwaɗo haka tafara yin tsallan tana zagaye kujerun,tun a first round jikinta ya fara gaya mata,Komawa yayi cikin bedroom ɗinshi ya ɗauki wayarshi daya bari agaban Mirror,Numbar Uncle Abusufyan ya lalubo,ya danna mashi Call,

A lokacin Abusufyan,Na acikin kitchen ya tu6e rigarshi daga shi sai shorts,ya dage sai aikin goge goge yake yi da ƴan wanke wanke,ya gyara kitchen ɗin tsaf,
  Fitowa Sehrish tayi hannunta ruƙe da wayarshi,har tuntu6e take yi wurin yin sauri donta kai mashi wayar,tana baccinta mai daɗi ringing ɗin wayar shi ne ya tashe ta,

"Daddy,ana kira,"ta ƙarasa maganar yayin da take shiga kitchen ɗin,hannu abusufyan yasa ya kar6i wayar,duba screen din wayar ya fara yi,
   *My first in-Law* Shi ne sunan daya bayyana akan screen ɗin,Yayi mamakin ganin kiran Sgr,Picking call ɗin yayi ya kara wayar a kunnanshi,
   "Assalamu Alaikum"
On the other hand,Sgr ya amsa mashi"Wa'alaikum salaam,Uncle kun isa Lafiya"?
.  "lafiya Lou,ae tun ɗazu muka ƙaraso,"
   "Okey,inason magana da sehrish ne,tana a kusa"?
   Murmushi abusufyan yayi tare da cewa"Ae bada ita muka zo ba,ko ka manta ne?
   "Uncle,Da ita ka tafi bada Jahad ba,yanzu haka jahad tana a part dinta,Sunyi musaya ne,"
  Cike da mamaki abusufyan yace"Jahad tana a gida!"
  Gaban Sehrish ne ya faɗi rass,wuƙi wuƙi tayi da ido,ɗagowa abusufyan yayi tare da kallonta,Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,sai lokacin ya shaida cewa Sehrish ce,ya ɗauko amatsayin Jahad,Ko ya akai suka shirya Wannan batare da kowa ya ankara ba,
  Sunnar dakai ƙasa tayi,ganin irin kallon da daddynsu yake yi mata,
  Rai a6ace ya miƙa mata wayar"Kar6i nan,"
  Hannunta na kerma ta kar6i wayar,hankalinta a matuƙar tashe,ta sanya wayar a kunnanta,muryarta tamkar zata yi kuka tace"Ya rafayet........"
   Tunkan ta ƙarasa maganar ya daka mata tsawa"Shut up!"nan take ta shiga taitayinta,
    "da iznin wa kika bar garin nan"?_
  Idanuwanta ne suka cicciko da kwalla,Sae faman kallon uncle take yi,sam baiji daɗin abunda sehrish tayi ba,don yasan ƙarshe kanshi abun zai ƙare,
   "Am sorry ya rafayet,dan Allah kayi haƙuri,Bazan ƙara ba,"
  dogon tsoki yaja,Kafin yace"Come back home,In ba haka ba,Ranki zai 6aci,"yana faɗin hakan yayi rejecting kiran,
  Fashewa tayi da matsanancin kuka,
Hannu abusufyan yasa ya kar6e wayar,
  "Koma meya laifinki ne!Ashe baki da hankali Sehrishi!Why kike son Jamin ina zaman lafiyana?,Taya zaki kamo hanya batare da iznin Mijinki ba,?"
   Cikin shesshekar tace"dan Allah daddy,kayi haƙuri,na kwallafa raina ne akan son zuwa,nasan nayi laifi,Kuma nayi danasanin yin hakan,Amma dan Allah daddy,Ka roƙan mun alfarma a wurinshi,Yabarni in zauna,Saboda yace in koma gida yau ɗin nan,"ta ƙarasa magana tare da sanya hannu tana share hawayenta,
  "I can't Call him Sehrish,rafayet bazai saurari kowa ba a halin yanzu,Kawai kije ki shirya kayanki,in kaiki tasha ki hau mota,"
Jin haka yasa ta ƙara fashewa da matsanancin kuka,tana faɗin"dan Allah daddy,kada ka mayar dani,Nashiga ukuna,"
  Sosai take kuka,Shi kanshi ya tausaya mata,duk yadda take shakkar Sgr amma ta kama hanya ta baro gidan batare da izninshi ba,tabbas ba ƙaramin son zuwa takeyi ba,
   Muryarshi a sanyaye yace"Kiyi hakuri daughter,babu yadda zamuyi dole ki bi umarnin Mijinki,lokaci yana ƙurewa,ki je ki shirya kayanki,mu tafi tasha,"
  Juyawa tayi da gudun gaske,Ta koma ɗaki,Saman gadon ta faɗa tare da fashewa da wani sabon kukan,

Jikin abusufyan ba ƙaramin sanyi yayi ba,yaso ace akwai wata hanyar da zai iya taimaka mata,don ta zauna a kanon,Amma ba halin yin hakan,
  yana cikin wannan zancen zucin wayar shi ta shiga ruri,da sauri yakai idonshi kan wayar dake hannunshi don yaga mai kiran nashi,Sunan Yaya Hossein ne ya bayyana akan screen din wayar,
  Da sauri ya answer kiran ya kara wayar a kunnanshi"Assalamu Alaikum,Yayana na kaina"_
  On the other hand,Abba yace"wa'alaikum salam ƙanina na kaina,Ya kake fatan kun isa kanon lafiya,"
  Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Mun ƙaraso tun wuraren goma,"
  Abba yace"Madallah,naji daɗi sosai,kai dawa kuka tafi ne"?
   Shiru ya ɗanyi yana tunanin halin da sehrish take ciki,ranshi ne ya bashi cewar Ya sanar ma Yayan nashi,May be ya iya dakatar da Sgr ɗin,
   Calmly ya soma magana"Ya hossein,Wlh an samu matsala,Da jahad na shirya tafiya,bansan ya akai ba,su ka yi musaya ita da sehrish,dama ta kwallafa rai akan son zuwa kano,To yanzu haka zancen da nakeyi maka,Muna tare da Sehrish ɗin,Kuma Sgr ya gane cewa da ita muka zo kano,ya bada umarnin ta koma yau yau ɗinnan,baiwar Allah tana cikin damuwa,yanzu haka tana can tana kuka,"yaƙarasa jawabin yana jiran jin amsar da abba zai bashi,
   "Kada ka damu,Ka lallasheta ta kwantar da hankalinta,Ni zanyi mashi magana,duk yadda mukayi dashi,in sha Allah i will inform you,"_
  Ajiyar zuciya abusufyan ya sauke tare da cewa"Nagode sosai,Yayana nakaina Allah yabar zumunci atsakaninmu,"
   "Ameen Ameen,ƙanina,"abba ya amsa mashi before suyi sallama,
   Har hankalinshi ya ɗan kwanta duk da yana zullumin amsar da abban zai bashi,don yasan halin Sgr wani lokacin idan ya burkice,mai tankwarashi sae Allah,

A lokacin da kiran abban ya shiga wayarshi,Yana zaune asaman sofa,ya aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,Yana sanye cikin jeans da t~shirt,yayin da jahad ke zukunne agabanshi,Tayi kneel down fuskar nan tayi jaga jaga da ita,tasha kuka har ta gode wa Allah,
   Hannu yakai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman front table din gabanshi yayi picking call ɗin,tare da kara wayar a kunnanshi,Ya furta"assalamu alaikum,"
   Acan 6angaren abba ya amsa mashi"Wa'alaikum salaam,My son ya kake ya gida,ya kuma aiki"
   "Alhamdulliah"
Abba yace"Yawwa,Rafayet dama game da yarainyar nan ne,Sehrish,"tunda yaji ya ambaci sunanta,Ranshi ya bashi cewar sunkai ƙararsa ne,
    "Dan Allah rafayet,ka ƙyale yarinyar nan ta zauna,ba jimawa zasuyi acan ba,Yarinyar nan ta kwallafa rai akan son zuwa can shiyasa harta tsallake ta tafi ba tare da saninka ba,Amma kai shaida ne akan yarda takeyi maka biyayya sau da ƙafa,duk wani abu da zai 6ata maka rai,tana ƙoƙari don taga ta faranta maka rai,pls rafayet ta ci albarkacin wannan,"
  shiru yayi batare da yace komai ba,
  Har sai da abban ya sake cewa"Rafayet naji kayi shiru,"
  Ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa"its Okey daddy,na haƙura,"Yanayin yadda yayi maganar,bada son ranshi ba,
   Muryar abba ɗauke da farin ciki yace"Ko kaifa,Wlh har naji daɗi acikin raina,Allah yayi maka albarka "
"Ameen"daƙyar ya iya furta hakan,Sallama su kayi ya janye wayar daga kunnanshi,
  mayar da idanuwanshi yayi kan jahad yace"U can go"
  Miƙewa tayi tana faman ɗangyasa ƙafarta,tabar falon nashi,ba ƙaramin jiki taji ba,Saukowa tayi downstairs tana cigaba da yin shessheƙar kukan,
  adai dai lokacin junaid ya faɗo cikin falon,Tsayawa yayi yana kallonta,ƙarasawa yayi da sauri wurinta yana faɗin"rishi lafiya meya faru"?
...ɗagowa tayi da idanuwanta waɗanda sukayi ja saboda kukan da tasha,Waro idonshi ya ɗanyi tare da ambaton sunanta"JAHAD"
   Cikin shesshekar kuka ta amsa mashi"Na,am"
   Hannu yasa ya tallabo fuskarta,"Dama bada ke aka tafi kano ba"?
  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,sannan tace
"Tare da sehrish aka tafi,amma dani muka shirya tafiya,Shine mukayi musaya ni da sehrish,yaya rafayet ya gano ni,Shine ya hukunta ni Hada tsallan kwaɗi ya sani,"
   Hannuta ya ruko,tare da samun wuri saman sofa suka zauna,
   Ranshi aɗan 6ace yace"Allah dana son da haka bazan bari Babban yaya ya sanyaki yin tsallan kwaɗi ba,Meyasa zai sanya juliet ɗita,Aikin wahala,'?
   hannu yasa yana share mata hawayen dake sauka akan fuskarta,cikin lallashi yace"stop crying my juliet,Allah in baki daina zubar da hawayenki ba,Nima zan fara kukan,". 
  Cike da zolaya,ya sanya hannunshi yana murza idanuwanshi,kamar zaiyi kukan,
  Da sauri ta ruƙo hannunshi tana faman sauke ajiyar zuciya tace"Nadaina".
  murmushi ya saki tare da cewa"Yaushe zamu fita yawo?Da anjima ko gobe"?
  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Mu bari sai gobe,Yanzu har la'asar tayi,Nafiso mu fita da wuri,mu zaga garin nan,"
   "Yadda kikeso haka za'ayi,"ya karasa maganar,tare da kai la66ansa zai sumbaci gefen fuskarta,Karaf idanuwanshi suka sauka akan na SGR dake ƙoƙarin saukowa downstairs,da sauri ya janye la66ansa,ya shiga ƴan kame kame,
  girgiza kai kawai sgr yayi don yaga abunda junaid ɗin ke ƙoƙarin yi,Fita yayi daga cikin falon batare daya tanka masu ba,

  
*Boss Bature*

*Sehrish*

hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,jin cewa an barta ta zauna a kanon,taji daɗi sosai acikin ranta,duk da tana fargabar hukuncin da Sgr zai yanke mata idon suka koma gida,

Bayan sallar la'asar,Suka shirya tsaf domin zuwa hotoro,Unguwar da sukayi rayuwa a cikinta,Abusufyan ne ke driving ɗinsu,tana zaune a gefenshi tana latse latsen wayarta,Yayin da can ƙasan zuciyarta ke cike fal da fargabar zuwa anguwar,A hankali Motar ta shararowa da matsakaicin gudu,izuwa cikin unguwar bai direta a ko'ina ba sai a ƙofar gidansu,don bai manta da kwatancen gidan ba,duk da yaɗan so ya ruɗe saboda sabbin gine ginen dake a wurin,kasa fitowa sehrish tayi daga cikin motar,Saboda yanayin da tashiga,ta tsani yin toxali da unguwar,Saboda bata son duk wani abu da zai tuna mata rayuwarsu ta baya,

Fitowa abusufyan yayi daga cikin motar ya zagaya,ya bude mata ƙopar,"Daughter,mun ƙaraso fa,"jiki asanyaye ta fito daga cikin motar,yayin da idanuwanta ke cike tab da kwalla,A wani slow ta wurga kwayar idonta akan gidajensu,Ginin ya tsufa sosai,duk fentin ya ƙoƙe,ya gajarce,An garƙame gidan da ƙaton ƙwaɗo,duk yayi tsatsa,da alama anjima ba'ayi amfani da gidan ba,mayar da idanuwanta tayi akan gidansu maman sadeeq,A rufe yake gidan da makulli,Gidan ya tsufa shima Amma bai kai gidansu tsufa ba,saboda an canza mashi fenti,

Hawaye ne suka soma shararowa akan fuskarta,juyawa ta ɗanyi tare da kallon abusufyan dake tsaye,jikinshi duk yayi sanyi,Saboda tunawa da wasu abubuwa da suka faru a rayuwarshi,
  Mutanen dake kai komo acikin Layin nasu sai faman leƙensu sukeyi,musamman ƴan yaran anguwar,
  "Daddy,Kamar basu nan fa,naga gidan a rufe,"
  Uncle yace"Bari na samu yaro na tambayeshi,Muji ko sun tashi ne,"
  Yana ƙoƙarin rufe bakinshi,Yaji anyi mashi sallama ta bayanshi,Muryar wani dattijo ne,juyawa yayi tare da kallon mutumin,tsoho ne amma ba irin tukuf ɗinnan ba,jikinshi na sanye da koɗaɗɗen yadi,ƙafafunshi na sanye da wasu siɗaɗdun silifas duk sun fita hayyacinsu,kamar mahaukaci,
   Da sauri abusufyan ya miƙa mashi hannu donsu gaisa,
 Dattijon ya maƙe hannunshi tare da cewa"Haba Alhajin Allah,baka ga yadda hannuna yake ba duk datti a haka zaka gaisa dani,"
  Murmushi abusufyan ya sakar mashi,"dan Allah kada ka hanani gaisawa dakai,"
  Mika mashi hannun tsohon yayi suka gaisa,Sannan yace"bawan Allah,ban ta6a ganinka acikin unguwar nan ba,Kuma da alama kamar wani ku ke nema ko"?
  abusufyan yace"ƙwarai kuwa,wannan Ƴa tace,Munzo daga abuja ne,Muna neman..umm....."bai ƙarasa maganar ba,saboda ya manta da sunan mutumin,
  Sehrish ce ta ƙarasa mashi maganar"Malam nura muke nema,malamin makarantar islamiyya,"
  Dattijon yace"Ae nan ne gidan shi,Sae dai kash,Sunyi tafiya zuwa kankia wurin jana'izar Wani kawunshi daya rasu,"
  Jin haka yasa yanayin fuskar abusufyan ta ɗan canza,zuwa damuwa,
  "Amma,tun yaushe suka tafi"?
  Dattijon yace"tun makon daya gabata,Amma jiya munyi waya dashi ya sanar dani cewa Yau ko gobe zasu dawo,"
  Ba ƙaramin daɗi suka ji ba,don har sai da abusufyan ya ɗanyi murmushi,
  Hannu yasa cikin aljihunshi ya zaro kuɗi sababbin ƴan dubu dubu kusan dubu goma sha biyar ya miƙa ma dattijon,
Washe baki tsohon yayi tare da sanya hannu biyu ya kar6i kuɗin,tare da cewa"yalla6ai kamar ka sani wlh yau gidana da yunwa muka tashi,yara sai kuka sukeyi,Hakanan na gaji da zama cikin gidan, nace bari na fito na nemi na abinci,Ashe arziƙi ne ke kirana,Allah na gode maka,da ka haɗani da wannan bawan naka,Ya Allah kamar yadda ya farantamun rai,kaima ka faranta mashi nashi,ka biya mashi buƙatunshi na alkhairi,'yana addu'ar hada ƴar kwalla akan fuskarshi,
   Atare suka dinga haɗa baki suna Amsa mashi"ameen ameen,
  Abusufyan yace"baba taimakon da zakayi mana,idan sun dawo dan Allah ayi gaggawar sanar damu,Bari na baka lambar wayata,
  Ya ƙarasa maganar tare da zura hannunshi cikin aljihun wandonshi ya ɗauko wayarshi,
  Hannu dattijon yasa,a gaban aljihun rigarshi,Ya curo ƴar ƙaramar wayarshi tecno,taji jiki duk tafita hayyacinta,miƙa ma abusufyan wayar yayi"kar6inan yaro,sanya mun numbarka,kayi mun saving ɗinta da sunan Mai mutunci,Zanfi ganewa,Da zarar sun dawo in sha Allah,bi'iznil lahi,koda ƙarfe ɗayan dare ne zan kira in sanar dakai,"
  Murmushi suka saki gaba ɗayansu,kar6ar wayar abusufyan yayi,madannan jikinta duk sun nutse ciki,daƙyar ya samu ya rubuta mashi numbar,yayi mashi saving da Mai mutunci,Sanna ya mayar mashi da wayar"Gashi baba,mun gode sosai,Sai naji ka,Allah yasa adace,"
  Tsohon ya amsa mashi da ameen ameen,ae tunda ka farantamun raina,Kaima sai Allah ya faranta maka naka,har addu'a sai nayi maka idan nayi sallah,
  "Ina godiya sosai,"ya karasa maganar tare da ruƙo hannun sehrish suka shige cikin mota,key yayi ma motar,a hankali yayi reverse,tare da karya kwana,da gudun gaske ya fuce daga cikin unguwar,
  Nasarawa suka koma,a bakin gate din gidan ya sauke sehrish,Saboda zuwa masallaci,An fara kiran magrib,Miƙa mata key ɗin gidan yayi"kar6i nan,ki rufe gidan da kyau,Bazan dawo da wuri ba,Saboda inaso naje nayi mana siyayyar kayan abinci,dana amfani,"_
  "Toh daddy adawo lafiya"tasa hannu ta kar6i key din,kafin ta juya ta nufi cikin gidan,tsayawa yayi acikin motar yana kallonta,har saida ta 6ace ma ganinshi,ya tabbatar da ta rufe ƙopar gidan,Sannan ya tashi motar ya fuce,

   A 6angarensu Aunty babba kuwa,basu isa Enugu ba sai wuraren ƙarfe sha ɗaya na dare,Sunsha uwar tafiya,ba ƙaramin jiki suka ji ba,Acikin garin suka kama ɗaki a hotel,Tunda suka shiga ɗakin,kowaccensu ta baje saman gadon ɗakin,suka shiga sharar bacci kamar wasu matattu,Ga uwar yunwa na cinsu,sai da sukayi bacci mai isarsu,Kafin suka farka neman abunda

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login