Showing 204001 words to 207000 words out of 432432 words
Chapter 69 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete
tamkar ɗanuwanmu,hakan baisa ka sanar damu cewa kana da ƴa ba,meyasa tun lokacin daka fara aiki agidan nan baka ɗauko yarinyar ka kawota gidan nan ba!....'ta inda take shiga bata nan take fita ba,
Jin waɗannan kalaman na Hajiya ameena yasa baba buzu fashewa da kuka yana cewa"na cuci kaina da ban sanar maku ba,ban ta6a tunanin cewa zaku kar6i yarinyar nan hannu bibbiyu ba hajia,da tuni na jima da kawo maku ita,kullum ina cikin takaicin rashinta a kusa dani,saboda itace kaɗai nake gani inji dadi aduniyar nan......'sosai baba buzu ke zubda hawayenshi,
Abu kuwa ganin mahaifinta na kuka yasa itama ta fashe da kukan,jikin hajiya ameena ne yayi sanyi,tausayinsu duk ya kamata,
tausasa muryarta tayi tace"baba buzu kukan ya isa hakanan,naji daɗin dawowarka musamman daka kawo mana wannan ƴar kyakkyawar yarinyar taka,kuma insha Allahu zamu bata kyakkyawar kulawa,zata zama tamkar ƴar cikina,dama kuma banda ƴa' mace,gashi inason ƴa mace,Ashe da rabon zan samu......'
Share hawayen shi ya shiga yi yana yi mata godiya,
"Yanzu abunda nakeso dakai,ka wuce ɗakinka kayi wanka zansa akawo maka abinci,nasan kun kwaso gajiya sosai kuna bukatar hutu,ita abu kabarta awurina,zan gyara maka ita sosai da anjima zata zo ta gaishe ka,"
Cikin shesshekar kuka baba buzu yace"hajiya bansan da wani irin kalamai zan gode maku ba,kunyi mun abinda bazan iya saka maku ba,kun jima kuna ɗawainiya dani kuma yanzu gashi zaku ɗauki ɗawainiyar yarinyata,Allah yasa ka maku da mafifincin alkhairinsa.....'sosai baba buzu ya shiga yi masu addu'o'i hakan ba ƙaramin dadi yayi ma Hajiya ameena ba,
Tun daga wannan lokacin Abu tazama tamkar ƴa awurin hajiya Ameena,baka ta6a gane cewa ba ƴar cikinta bace saboda yadda suke ruƙe ta hannu bibbiyu duk wata ɗawainiyarta tadawo kansu,hatta makarantar islamiyya dana boko babu wanda basu sakata ba,dama yarinyar akwai hazaƙa sosai,akwai son karatun addini,kullum zaka ganta rungume da kur'ani a hannunta tana karatu,ko aiki takeyi zaka ji tana ta rero karatun haddar da aka basu,bata ta6a zama bakinta shiru batare da tana karatu ba,wannan abun ba ƙaramin burge hajiya ameena yake ba,shiyasa batajin wuyar kashe mata kuɗi,saboda ita ta ɗauko malamin da zai dinga zuwa gida yanayi mata karatu,malamin makarantar islamiyyarsu wanda suke kira da Ya sayyadi,tun da zainab tafara zuwa makarantar islamiyyar asatin farko kullum sai yazo gaishe da hajiya ameenatu,idan yazo yayi ta zuzuta zainab awurinta yana yaba irin ƙoƙarin dake gare ta,hajiya Ameenatu najin daɗin hakan,Amma mahaifin Abu,baba buzu mai gadi mutumin bai kwanta mashi araiba,ya tsani yaga malamin nan yazo wurin Abu zai koya mata karatu,shisshigin da yake yi ma yarinyar yayi yawa,kullum sai yazo da ɗan rugwagwar mashin ɗinshi ƙopar gate din gidan wurinta,hakan ba ƙaramin ƙona ma Baba buzu rai yake ba,shiru kawai yake yi don bai da yadda zaiyi ya hana shi zuwa gidan,tunda hajiya ameenatu ta ɗauke shi amatsayin malamin da zai dinga koyama Abu karatu,tun Abu na da wata daya acikin gidan haris ya dawo batare da Abusufyan ba,saboda shi yace bazai dawo ba sai daddy mijin Aunty ameenatu ya bashi haƙuri,saboda yace shi yake 6ata tarbiyyar Haris,rashin jin maganar shi yayi yawa,koda haris ya hadu da Abu acikin gidan saiya mayar da ita tamkar ƙanwarshi,idan aka bata assignment na school shike zama ya fidda mata shi,harma ya koya mata karatu.
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka
Wadrobe balls
Madarar kulleccham
Vaseline kulleccham
Kajiji
Halut
Couscous
Khumrah
Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka
Wadrobe balls
Madarar kulleccham
Vaseline kulleccham
Kajiji
Halut
Couscous
Khumrah
Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.
Snack
Awarah
Farah
Zobo
Samosa
Cup cake etc
Contact me 09063302182or 09012179727.
*💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*
*Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari*,
Bayan wani lokaci
Tafiya takeyi tamkar batason taka ƙasa,jikinta na sanye da uniform na islamiyya,dogon hijab Brown colour har wuce guiwarta,wandon kuma milk colour,ta rufe fuskarta da nikab,yayin da hannayenta ke ruƙe da jakar makarantarta,da gudun gaske wata danƙareriyar mota ash colour ta faɗo cikin layin da take tafiya,gadan gadan mai motar ya tunkari inda Abu taja ta tsaya,waro ido waje tayi tare da ja da baya jikinta na kerma,koda mai motar nan ya ƙaraso inda take,sai ya shiga zagaye ta da motar gaba ɗaya ya tada mata ƙura,
Ƙanƙame jikinta tayi gabanta ya faɗi rass,tsoronta kar ace sace ta aka zo yi,
Sai da ya tabbatar da cewa ta gama tsorata sannan ya tsayar da motar wuri guda ta tsaya cak,
A ɗan tsorace abu ta buɗe idanunta tana kallon motar cikin ranta tana tunanin wanene wannan bawan Allahn daya firgitar da ita haka,
Bata ƙarasa zancen zucin nata ba taga ya zuge glass ɗin motar,lokacin da tayi arba da kyakkyawar fuskarshi sae da gabanta ya faɗi rasss!matashi ne wanda bazai gaza shekara 20 ba zuwa ashirin da daya,kana kallonshi zaka ga ƙuruciya atare dashi,jikinshi na sanye da crazy jeans sae farar t shirt agaban rigar an rubuta Am crazy,'da alama bashi kaɗae bane acikin motar,akwai wani agefen shi,
Muryar mace tajiyo daga cikin motar tashi tana cewa"Hey,ƴan mata,mun tsorata ki ko?ki yi haƙuri Babyn nawa ne sae a hankali,wai kin burge shi ne,shiyasa yayi maki wannan wasan,'.
rai atsananin 6ace take kallon fuskokinsu ta cikin niqab din fuskarta,bakowa yafi bata haushi ba face shi saurayin daya yi mata wannan ɗanyen aikin,arayuwarta ta tsani mutane masu wayewa irin tasu,kallo guda tayi masu ta gane cewa ba mata da miji bane,amma sun manne ma juna acikin motar kamar zasu haɗe su zama ɗaya,
jinjina kai kawai tayi tare da zuƙunnawa ta ɗauki jakar islamiyyarta da ta fadi,cikin sauri ta kama hanyar zuwa gida,biyo ta sukayi da motarsu,hakan yasa hankalinta ya tashi,saboda gudun kada Abbanta ya ga motar dake biye da ita,don kullum yana ja mata kunne akan karta kuskura wani ya tsaidata akan hanya ta tsaya,yanzu in ya ganta tare da wannan jibgegiyar motar dake bin bayanta batasan wane hukunci zaiyi mata ba,dole ya tuhume ta akan ina ta samo su,
"Baby,kana ganin zata faɗa mana address ɗinta kuwa?da alama yarinyar kamar za tayi ji da kai nake gani,kasan ƴan islamiyyan nan,ji su keyi kamar sunfi kowa tsoran Allah,suyi ta kame kansu acikin hijabi,suna yi ma mutane kallon shaiɗanu,'matashiyar dake acikin motar ce tayi wannan maganar,kuma duk akan kunnan Abu,
Saurayin yace"ae ko bata faɗa mana address ɗinta ba,zamuyi ta bin bayanta ne har mu gano gidansu,"
Jin wannan maganar yasa,yarinyar zuƙunnawa tare da kwale takalman ƙafafunta,kafin su ankara ta watsa da gudun gaske kamar zata tashi sama,ko waiwayensu batayi,har ta 6ace ma ganinsu,,
Tun daga nesa Baba buzu mai gadin dake a zaune saman benchi yana sauraron radiyo dake ruke a hannunshi,ya hango ta sai faman tsala gudu takeyi,hankali tashe ya miƙe tsaye yana jiran ƙarasowarta,koda ta ƙaraso a galabaice ta zube agabanshi,saman guiwowinta tana faman haki,
"Abu meya faru ne naga kina gudu haka?waye ya biyo ki"?
Muryar mahaifin nata ne ta dawo da ita cikin hayyacinta,
daƙyar ta iya cewa"wasu ne a mota,bansan kosu wanene ba,sae faman bibiyata sukeyi,shine na watso da gudu don karsu gane gidan da nake,"
Jin wannan maganar yasa ran buzun mai gadin ya 6aci sosai nan fa yashiga zazzaga masifa yana cewa"da kin bari sun ƙaraso don ubansu dana koya masu hankali,shikenan ba dama yarinya ta ɗan fita ɗauko karatu sae an samu wanda ya takura rayuwarta!zan yi maganin koma wane ɗan ja'irin ne yake son cutar mun dake.....'ta inda yake shiga batanan yake fita ba, a ƙarshe dae yace"tashi ki shiga ciki,kiyi wanka kici abinci ki kwanta ki huta kafin akira sallar magariba,ki kwantar da hankalinki kinji Abunah,ina nan ina jiran Koma wane ɗan iskan ne,saina koya masu hankali,'
Ajiyar zuciya abu ta sauke tare da miƙewa tayi mashi sallama,sannan ta shiga cikin gidan ta ƙopar gate ɗinsa,
Lokacin da ta shiga cikin main palour ɗin gidan babu kowa,alamar suna can upstairs bedrooms ɗinsu,don haka ta wuce nata ɗakin kai tsaye,
Bayan ta ajiye jakar islamiyyarta,ta cire hijab ɗin jikinta,ta ninketa tare da turata cikin wardrobe na kayanta,shaf shaf ta kammala cire kayan islamiyan nata ta wuce cikin toilet don tayi wanka,
After some minutes,ta fito daga cikin toilet ɗin jikinta ɗaure da farin towel,jikin nan nata har wani ƙalli yakeyi saboda hasken fatarta ga gyaran da take sha,agaban mirror ta tsaya tana ɗaure sumar kanta mai tsayi da yawan gaske,tana da yalwataccen gashin kai wanda yakai har qugunta,tana cikin ɗaure gashin kan nan nata kwatsam taji anyi mata gyaran murya abayanta,a firgice tajiyo don ta ga kowanene,lokacin da tayi arba da mutumin da yayi mata gyaran muryar acikin ɗakinta nan take ta zazzaro ido amatuƙar tsorace take kallonshi,
kwance yake asaman gadonta,ya miƙe ƙafafunshi yayin da hannunshi ke ruƙe da brazier ɗinta da ta cire kafin tashiga toilet,sae faman latsa breast curve ɗin yakeyi cike da tsokana,
Hankali a matukar tashe abu tace"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un...Nashiga uku....!'gaba daya taba ma ranta cewa al'jani ne shi,ba kowa bane wannan face saurayin nan daya tsoratar da ita da motarshi akan hanyarta ta dawowa daga islamiyya,shi da budurwarshi,
Muryarta na rawa tace"wa..wanene...kai dan Allah!me kakeso a wurina ne!taya akai kasan gidan mu har ka biyoni ɗakina"?
Ƙayataccen murmushi ya saki tare da cewa"bani da amsar tambayoyinki,ni dai kawai nagani inaso,in kika yi mun biyayya mu rabu lafiya,koda yake bazama mu ta6a rabuwa ba,saboda kinyi mun wlh," ya ƙarasa maganar tare da kai bakinsa ya manna ma bra ɗinta kiss
Runtse ido abu tayi agigice ta fasa ihu tana neman ɗauki,akan azo a fidda mata aljanin dake aɗakinta,
Da gudu ta watsa waje babban falon jikinta na kerma ta shiga cewa"Mommy!!mommy!!ya haris!daddy!!dan Allah kuzo ku taimake ni,Aljani aɗakina saman gadona....'
Jin sautin kukan Abu yasa hankalin Hajiya ameena tashi,da saurin gaske ta sauko downstairs ta nufi wurinta tana cewa"Abu meya faru ne kike ta kwaɗa ihu?
Cikin shessheƙar kuka tace"Wani ne acikin ɗakina saman gadona,bansan ko wanene shi ba,a kan hanyar dawowata daga islamiyya ya tsoratar dani da motarshi,shine yanzu kuma bayan na fito daga wanka na ganshi kwance saman gadona,'
Cike da mamaki hajiya Ameena tace"Wani kuma!acikin gidan nan saman gadonki?taya akai har ya samu damar shigowa cikin gidan nan....'
Ba ta kaiga ƙarasa maganar ba,sae ga Abusufyan ya fito daga cikin ɗakin abun,fuskarshi ɗauke da murmushi,
Ganin shi yasa abu yin saurin nuna shi da hannu tace"Ga shi nan mommy....wlh shine ..Aljani ne,"
murmushi hajiya Ameenatu tayi tana kallon Abusufyan tace"Son sai yau kaga damar dawowa gidan?irin wannan zuwan bazata haka?ka tafi kabarmu da kewarka ko?ko tunanin makaranta bakayi ba,ka kama hanya ka tafi kan abunda bai kai ya kawo ba,'
Langwa6e kai abusufyan yayi yana tsuke bakinshi alamar an 6ata mashi rai,
...zuru abu tayi tana kallon ikon Allah,aranta tana cewa"Ashe ɗan masu gidan nan ne,ni duk atunanina aljani ne shi,amma dae da alama baijin magana sosai,'
"Pls mom just forget about it,komai ya wuce tunda dae nadawo,"
Jinjina kai hajiya ameenatu tayi,kafin ta mayar da idanunta kan Abu dake tsaye sototo tana kallonsu tace"Calm down ur mind Abuna,wannan da kike gani ɗan yayata ne,sunan shi Abusufyan,bai jin magana amma kada wannan ya hanaki sakewa dashi,shima ki ɗauke shi tamkar Yayanki Haris,'
Jiki asanyaye tace"insha Allah mommy,"kafin ta ɗan wurga ido ta kallo shi har lokacin kashe mata ido yakeyi,hakan ba ƙaramin haushi yake bata ba,har tafara jin tsanarshi,
Tun daga ranar da Abusufyan ya dawo cikin gidan abu ta shiga uku dashi,ya hana rayuwarta sakat,duk inda ta sanya ƙafarta yana biye da ita,toilet ne kawai bai binta shi dai kawai burinshi ta sake dashi kamar yarda take shiri da haris,ita kuma tace bazata ta6a ɗaukarshi yayanta ba,saboda bai da kamun kai,bakomai yaja mashi hakan ba face Abubuwan da yake yi mata na rashin kunya,da kuma ƴan mata da take ganinshi tare dasu manne da juna,hakan ba ƙaramin ƙona mata rae yake yi ba,duk a tunaninta Abusufyan ɗan iska ne kamar yana bin mata,saboda ita tayi believing da abunda idanuwanta ke nuna mata,
Ana haka wata rana malamin nan nasu Sayyadi ya ɗaukota daga islamiyya asaman machine dinsa super cub,tun suna akan hanya motar abusufyan ke bin bayansu saboda ya hangota abayan mashin ɗin malamin,ranshi yayi mugun 6aci wani irin kashi ne ya lullu6e shi,saboda ya lura akwai soyayya tsakaninta da malamin nan nasu,babu yarda abusufyan baiyi da ita ba akan ta bari ya dinga kaita school amma taƙiya,da yake tana da kafiya sosai,mace ce mai wuyar sha'ani,
A bakin gate ɗin gidan sayyadi ya tsayar da mashine ɗinsa,abu ta sauko hannunta ruƙe da jakarta,tsayawa tayi suna ƙara gaisawa dashi,
"Abu har yanzu baki bani amsa ta ba"?
Sunnar da kai ta ɗanyi tana murmushi tace"amsar me kenan"?
sayyadi yace"oh har kin manta kenan?abu kinfa san ina sonki sosai,kuma kema kina sona,bana buƙatar mu 6ata lokaci atare da juna batare da munyi aure ba,banda burin daya wuce wannan, in ganki amatsayin matar aure na,'
Cike da jin kunyarshi abu tace"dan Allah ka ƙara mun lokaci,zanyi tunani akan hakan,'
Kafin sayyadi ya buɗe baki ya ƙara yin wata maganar,suka ji dirar motar Abusufyan agefensu,tun daga kan yarda yayi parking ɗin motar ya tabbatar masu da cewar ba'a hayyacinshi yake ba,
.zuba ma motar ido sayyadi yayi kafin ya mayar da idonshi kan abu yace"wanene acikin motar nan"?
Muryarta na rawa tace"yayana ne Abusufyan,'
ɗan ta6e bakinshi yayi yana jinjina kai,
Atsiyace abusufyan ya buɗe murfin motar ya fito,jikinshi sai faman rawa yake yi,kai tsaye wurinsu ya nufo sai faman huci yake yi,
Wani irin mugun kallo ya jefa mata tare da nuna mata hanyar gida yace"Ke wuce ciki!tun kafin ranki ya 6aci shashasha kawai wadda batasan ciwon kanta ba!ki rasa da wa zakiyi mu'amala sae wannan ƙarmasasshen mutumin,ko uban miye abun so ajikinshi!mutumin da ya kusa tsaran ubanki!"
Hankalin abu ba ƙaramin tashi yayi ba jiki na rawa ta kama hanyar shiga gida,
Muryar sayyadi ce ta dakatar da ita"Abu kada ki tafi!bangama magana dake ba,"
Zuba ido abusufyan yayi yana kallon ikon Allah,tsayawa abu tayi saboda umarnin da sayyadi ya bata akan karta tafi,
Rai amatuƙar 6ace Abusufyan ya daka mata tsawa tare da cewa"ke!har ni zan baki umarni kiƙiyi mun biyayya saboda wannan munafukin mutumin malamin ƙarya!"
Waro ido waje sayyadi yayi yana kallonshi,
Abu kuwa jin an ta6a masoyinta yasa tace"Abusufyan ya isa haka!karka ƙara zagar mun malamina,wannan mutumin da kake gani yafi mun kai so dubu,saboda yana da ilimin addini kuma shi yake koyamun karatu,mutum ne shi mai kamun kai ba kamar kai ba....'jin kalaman abu akan shi yasa sayyadi ya shiga sakin murmushi yana kallon Abusufyan dake tsaye zuciyarshi na tafarfasa,
Tuni idanunshi sun ciko tab da kwalla saboda bai iya jurar 6acin rai ba,Zainab ta bada shi awurin malaminsu,
daƙyar yake iya haɗiyar yawun bakinshi da ya gama ƙafewa,jinjina kanshi ya shiga yi kafin daga bisani ya soma magana cikin sanyin murya"Naji duk abunda kika ce abu,amma inaso ki sani bakowane malami bane yake zama mutumin kirki,don kawai ya ruɗe ki da karatun kur'ani yana jawo miki aya da hadisi yana fassara maki su,shine yasa kike tunanin cewa shi mutumin kirki ne?mutun nawa kika sani yana da haddar al'qur'ani akanshi amma hakan bai hana shi aikata zunubin daya ga dama ba....."?
ɗaure fuska sayyadi yayi yace"Kaga ɗan saurayi yarinyar nan ta nuna cewa bata sonka,dan Allah karabu da rayuwarta mana haba,ita malami takeso mahaddacin al'qur'ani ba ɗan tasha ba mai yawo da mata acikin gari,'
Wannan maganar ba ƙaramin fusata Abusufyan yayi ba,har baisan lokacin da ya ware tafin hannunshi ba ya kifa ma sayyadi mari asaman kuncinshi,kafin abusufyan ya zame hannunshi daga kan fuskar Sayyadi yaji saukar mari ɗauuuu a kan fuskarshi agigice ya juya yana kallonta hankalinshi amatuƙar tashe bai ta6a tunanin cewa abu zata iya ɗaga hannu ta mareshi ba,tunda yake arayuwarshi ko dunguri wannan wani bai ta6a gigin yi mashi ba,sai yau da Abu ta mare shi saboda ya mari sayyadinta,
Hawaye ne suka soma gangarowa daga cikin idanuwanshi,muryarshi har kerma takeyi wurin cewa"A..ab..bu..ni kika mara saboda na mari wannan ƙasƙantaccen mutumin mai fuska biyu!?
ɗaga hannu tayi zata ƙara kwasa mashi mari,kamar daga sama taji an ruke hannunta kafin tayi wani aune kuma taji saukar mari zazzafan gaske akuncinta,
A firgice ta juya tana kallon shi,bakowa bane ya mare ta ba,face mahaifinta shi da kanshi baba buzu,
Fashewa tayi da matsanancin kuka tana cewa"baba...yau kai da kanka ka mare ni?"
A faɗace yace"idan kika sake buɗe baki kikayi magana saina kikkifa maki wasu marukan,sakarya kawai wadda batasan halacci ba,yanzu saboda wannan mutumin kika mari abusufyan ko?
wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarshi jin yarda mahaifinta ya goya mashi baya,sayyadi kuwa ranshi ba ƙaramin 6aci yayi ba,sae faman mazurai yake yi,
Kafin yace"haba