Showing 351001 words to 354000 words out of 432432 words

Chapter 118 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete

zasu sama cikinsu,Oder sukayi aka kawo masu lafiyayyan abinci,kamar wasu kuraye haka suka tasarwa abincin suna Ci,Sai da suka ci suka ƙoshi,tukunna suka koma saman gadon,Suka dasa wani sabon baccin,ba tunanin yin sallah,a ƙagare suke washe gari yayi su wuce cikin dajin,
 
*Boss Bature*

   ❤🤍❤

Har Wuraren ƙarfe 12,Abusufyan bai dawo cikin gidan ba,gashi yabarta ita kaɗai,da farko bata damu ba,falo ta dawo ta zauna saman sofa,daya ke akwai nepa,hasken globe ya gauraye ko'ina,hannunta na ɗauke da littafin oummansu tana karantawa,Kalaman soyayya ne acikinshi,a cikin drawer ta samu littafin,Wani page ta buɗo acikin littafin Sunan oummansu ne akai dana Ya sayyadi,Aikuwa rai a6ace ta sanya hannu ta yage takardar tare da yin wurgi da ita,Mayar da hankalinta tayi sosai akan littafin tana karanta love messages ɗin dake aciki,da zarar taga wanda ke ɗauke da sunan ya sayyadi,jikinta har rawa yake yi wurin sanya hannu ta yage shi,

Tana cikin wannan karance karance,kwatsam!Aka ɗauke da wutar nepa,nan take duhu ya gauraye ko'ina,babu haske ko misƙala zarratin,gashi ta baro wayarta saman drawer cikin ɗakin,Sanin kanku ne sehrish muguwar matsoraciya ne,Tuni ido ya raina fata,Hankalinta yayi mugun tashi,jikinta ya shiga yin kerma,kamar gunki haka ta ƙame a zaune ta gaza motsawa,tana cikin wannan yanayin na tashin hankali,Tajiyo takun takalmin mutum,A matukar tsorace ta shiga ambaton sunan Daddynsu da ƙarfi"Daddy!daddy!dan Allah kana ina,nashiga uku,'
  Gabanta ne ya fadi lokacin da ta tuna cewa,daddynsu da Motarshi ya fita,da ace shine ya dawo cikin gidan to tabbas zata ji sautin ƙarar shigowar motarshi,
   Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,jin motsin mutumin na tunkarota,a razane ta saki littafin dake a hannunta,ta miƙe daga saman sofa ɗin tashiga ja da baya,tana tafiya saɗaf saɗaf,hawaye duk sun wanke mata fuskarta,zuƙunnawa tayi ta soma yin rarrafe a hankali tana ƙoƙarin gano ƙopar ɗakin oummansu,cikin rashin sani takai hannunta saman wani gwangwanin maltina,aikuwa ya bada wani irin sauti rakwakwas,a gigice sehrish ta miƙe,gudu gudu sauri sauri,ita kanta batasan inda zata tunkara ba,Unfortunately tayi tuntu6e da wani abu,gaba ɗaya ta tafi zata faɗi ƙasa,ta saki wata irin razananniyar ƙara,
  Sai dai kafin takai ƙasa,Taji an damƙi qugunta,kwakkwaran ruƙo akayi mata,kafin aka janyota da ƙarfi,ta faɗa saman ƙirjin mutumin,koma waye wannan ba ƙaramin mutun bane,ƙarƙarfan gaske,
  Tashin hankali domin son sanin wanene wannan mutumin,Mu haɗu gobe inda rai da lafiya,In Allah yasa muna da rabon ganinta kenan💋Boss Bature💋*



Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*

*Father of soldiers*

*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*






Am really sorry,🙏


Tayi matuƙar tsorata dashi,kasa ɗagowa tayi daga jikinshi,jikinta sae kerma yake yi,lokaci guda daddaɗan ƙamshin turarenshi ya daki hancinta,nan take ta ruɗe tana ƙoƙarin gano a ina tasan ƙamshin nan,duk duniya mutun ɗaya ne ta sani mai irin wannan ƙamshin turaren mai matuƙar ratsa zuciya,Ruɗewa tayi tana so ta canko wanene,kuma tana kokwanton anya hakan zai iya kasancewa gaskiya?zame hannayenta tayi daga saman waist ɗinshi da ta ruƙe,ta matsar dasu har izuwa mid back ɗinshi,Gabanta ne ya faɗi rass jin ta shafo doguwar sumar kanshi,muryarta na kerma ta furta sunanshi"BABBAN YAYA..!"tana ambaton hakan,Wutar ɗakin ta dawo nan take haske ya gauraye ko'ina tamkar da Rana,zuba mashi ido tayi tana kallon kyakkyawar fuskanshi wadda ke sanye cikin face mask black colour,Launin rigar jikinshi ya lumshe idanuwanshi,slowly ya ɗan waresu akan fuskarta,Ae tana ganin blue eyeballs ɗin nan nashi,Ta ƙara tabbatar da hasashenta,abun yayi mugun ɗaure mata kai,kallonta yake yi from head to toe,fuskarta duk tayi zufa saboda tsabar firgicin da ta shiga,ga hawaye jaga jaga a fuskar,duk don saboda an ɗauke da wutar nepa ta ganta acikin duhu,

Sai faman sauke ajiyar zuciya take yi,hankalinta har ya kwanta da ta tabbatar cewa shine,Tayi tunanin wani mugunne yazo don ya cutar da ita,tayi farin cikin ganinshi sosai kamar tayi ihu,Amma ta wani 6angaren tsoran hukuncin da zai yanke mata take yi,duk a tunaninta yazo ne don ya hukuntata,tunda ya bata Command taƙi bi,
   Ganin irin kallon da yake yi mata ne yasa tayi saurin sunnar da kanta ƙasa,tana wasa da yatsun hannunta,
    Hanky ya zaro daga cikin trouser pocket ɗinsa,Ya miƙa mata tare da cewa"Take it,"hannu tasa ta kar6a,ta shiga goge fuskarta sosai,
   "In kawo maka ruwa kasha"?cikin sanyin murya ta ambaci hakan,
   Girgiza mata kai yayi alamar a'a,kafin ya wuce cikin falon,Ya zura hannayenshi biyu acikin aljihun wandonshi,
  juyowa tayi tana kallonshi,A dai dai lokacin suka jiyo sallamar Abusufyan"Assalamu Alaikum",
   Amsa mashi su kayi da"Wa'alaikum salaam,"
  Shigowa cikin falon yayi,hannunshi ruƙe da key ɗin Motarshi,
  Koda yayi arba da Sgr,cike da mamaki yace"Rafayet!Ashe dagaske ne,Abban ku ya sanar dani cewa,zai yi wa Omar magana ko shi ko kai wani yabiyo bayanmu don yaso yana nan muzo dashi,Banyi tsammanin cewa kaine zaka zo ba,Yanzu kawai ina karyo kwana da motata naga sojoji zagaye da gidan nayi ta mamaki cikin raina,Gaskiya ba ƙaramin daɗi naji ba," ya karasa maganar a yayin da yake ƙoƙarin rungumarshi,da alama Abusufyan ba ƙaramin daɗi yaji ba,Sai murmushi yake yi,
   "Na same ku lafiya,"?
"Lafiya lou Alhmdllh,Naje masallaci ne,na biya naga wani Abokina daga can kuma na wuce wani store zanyi mana siyayyar kayan abinci,Inata fargabar nabar yarinya ita kaɗai acikin gida",
  Sgr yace"nayi mamakin ganinta ita kaɗai zaune acikin gidan,time ɗin dana shigo kuma bansan meya faru ba,duhu ko'ina,so sai daga bayane hasken ya dawo,"
  Abusufyan yace"Ae ɗaukewa su kayi da wutar ne,yanzu nima ina kan hanyar dawowa naga sun dawo da ita,"
  wurga idonshi yayi kan Sehrish dake tsaye hannunta ruƙe da hanky dinsa,ta kammala goge hawayen,
  "Daughter,zonan mana,"ya kirata da hannunshi,wurinsu tazo ta tsaya tana facing din Abusufyan,
   "Faɗamun meya faru?bayan na tafi"?
murmushi ta ɗan yi,batare da tace komai ba,
   Mayar da idanuwanshi yayi kan Sgr yace"Amma dai ba nan zaka kwana ba ko"?
   "I will spend the night here,"
Abusufyan yace"ba ka ga yadda gidan yake ba ne?Ni nasan bazaka iya bacci acikinsa ba,Yakamata ka wuce hotel kawai,ina ganin zaifi maka daɗin zama,"
  Girgiza mashi kai yayi"No,i wanna stay here," gyaɗa kai abusufyan yayi tare da kallon sehrish yace
  "Sehrish ki kaishi bedroom ɗin da kika gyara,ya zauna acan,Amma dai banso ba wlh,Don nasan cewa zaka takura sosai,Ga zafi ga sauro duk da na siyo maganin sauron,Amma bana tunanin zai iya dakatar da saurayen dake acikin gidan nan,"
  Amsa mashi tayi da toh,Sannan ta juya tare da kallon Sgr tace"Mu shiga ciki,"
  Gaba tayi yabi bayanta,daƙyar yake iya taka kasan palourn,saboda daudar dake a wurin duk da sun gyara shi,
  Shiga cikin bedroom ɗin su kayi atare,Wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana ƙarewa ɗakin kallo,
  "Kana bukatar wani abu,in kawo maka,"
   "No need"ya ambaci hakan a yayin da yake zaro wayarshi daga cikin aljihun wandonshi,
"Sehrish!"Abusufyan ne ya kwala mata kira,da sauri ta juya ta fita daga ɗakin,
  Komawa tayi cikin palourn A tsaye ta same shi,Ga kayan da yayi masu siyayya hada gass cylinder saboda yin girki,Sojoji ne suka shigo dasu,A cikin buhu guda biyu,sae cylinder ɗin da suka ajiye nan,
  Ƙarasawa tayi wurinshi,"Gani Daddy,"
   "Kunyi magana dashi ya fada maki ko yana buƙatar wani abu?"
"a'a bai bukaci komai ba,"
Shiru Abusufyan ya dan yi,ganin damuwa akan fuskarshi yasa tace"Meya faru daddy," hannu yasa ya ɗan shafa sumar kanshi kafin yace"Daughter,bazai iya kwana acikin gidan nan ba,Ni nasan waye rafayet,Wlh nayi mamakin ganinshi banyi tsammanin cewa shi zaizo ba,Kalli fa gidan nan ki gani,babu wani shiri da mukayi,yanzu da zarar an ɗauke da wutar nepa,Shikenan zafi zai rufe mu,kuma ko kaɗan baison zafi,Gashi da ƙyankyami toilet idan bana bedroom ɗinshi ba,baya shiga na kowa,Kuma dole ya buƙaci yin wanka,Ni bansan ya zamu ƙare dashi ba,"
  Murmushi Sehrish tayi,ita kanta ta jinjina ma ƙarfin hali irin na Sgr,yadda yake da ƙyanƙyamin nan,Amma a haka yace zai kwana acikin gidan,Koya zasu ƙare,?
  "Daddy,kada ka damu,tunda yaji ya gani,zai kwana anan ɗin ka ƙyaleshi kawai,"
  Gyaɗa kai Abusufyan yayi tare da cewa"Shikenan kawai,Yanzu dai bari na shiga da kayan abincin nan kitchen,"
  Yayi maganar tare da sa hannu ya dauki buhu ɗaya,hannu tasa itama ta kama ɗayan buhun,taja shi izuwa cikin kitchen,bayan sun kammala kwashe kayan sunkai kitchen,
  Ta dube shi tare da cewa"Zan iya dafa mana ko taliya ce?
  Abusufyan yace"Kina jin yunwa ne"?
  "A'a,bana ji,saboda kai dama zan dafa,naga bamu ci Dinner ba,
  "Ki barshi kawai,akwai kayan tea dana siyo da bread,idan kina jin yunwa ki haɗa ki sha,Yanzu dae bacci nake ji,"
  Yayi maganar yana hamma,
"A ina zamu kwana"tayi tambayar tana kallonshi,
"Ki wuce inda mijinki yake mana,Ni zan kwana a palour ne,Ki dauko mun bargon da zan ɗan shimfiɗa in akwai"
  "Toh" ta amsa mashi tare da
  Kama hanya ta fuce daga cikin kitchen ɗin,Shima fitowa falon yayi ya tsaya a tsaye yana jiranta,

Lokacin da ta shiga bedroom ɗin,A kwance ta samu Sgr yana bacci ya ƙure fankar ɗakin har ƙarshe,iska ta ko'ina,hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,wurin wardrobe ta wuce ta sanya hannu ta buɗeta,daga gida na kasa blanket din suke tare da bedsheet,hada mosquito net,
   Bargo ta dauko mashi,Sannan ta koma falon,har lokacin Abusufyan na atsaye,yana jiranta,
   Ƙoƙarin shimfiɗa mashi tayi,da sauri yasa hannu ya kar6i bargon tare da cewa"Yawwa My Own Daughter,nagode sosai,"
"Sae Allah yakaimu Daddy,"fuskarta asake tayi maganar,
  "Allah ya kaimu lafiya,take care of my son,don't allow even one mosquito to bite his skin,If not ranki zai 6aci,"cike da zolaya yayi maganar,
  Fashewa tayi da dariya,tare da juyawa tana faɗin"don't worry daddy,In sha Allah i will look after him,very well,"
  Gyara kwanciyarshi yayi saman sofa ɗin,cikin lokaci ƙanƙani bacci yayi awon gaba dashi,
  Komawa cikin bedroom ɗin tayi,bedsheet ta dauko acikin wadrobe ta shimfiɗa a kasa,sannan ta matsa wurin gadon,ta ɗauko pillow guda ɗaya ta ajiye shi saman zanin gadon,
   Wurin switch taje,ta kashe light ɗin ɗakin,Nan take duhu ya gauraye ɗakin amma ba sosai ba,akwai hasken ƙwan dake a falo guda daya da aka bari akunne,ya ɗan haska ɗakin nasu,
    Moving tayi izuwa wurin gadon inda Sgr ke kwance yana bacci,addu'o'i ta shiga karantowa tana ɗan tattofa mashi,bayan ta kammala ta koma saman shimfiɗar da tayi,ta gyara kwanciyarta,sai da itama ta karanta addu'o'in tabi ta shafe jikinta kafin ta rufe idanuwanta,bacci 6arawo yayi awon gaba da ita,

Around 1:30 na dare,Ƴan nepa suka yi tsiyar tasu da suka saba,Tashin hankali,Ƴan sakanni da ɗauke wutar fanka ta tsaya cak,Wani irin zafi ya fara ziyarta ɗakin,Sai ga mutanen da gudun gaske sun fara kwararowa cikin ɗakin,Buuuuuuuuuu da wani irin kuka mai sautin gaske,tun yana juyi saman gadon yana kai hannu yana buge sauron dake ƙokarin attacking ɗinshi,har ya fara ƙokarin farkawa,Wata irin zuface ta soma tsastsafo mashi ajikinshi,Sharkaf ya jiƙe,tuni numfashinshi ya soma kokawar fitowa daga hancinshi,kamar an toshe shi,A firgice Sgr ya farka yana faman zazzare blue eyes ɗinshi,Hankalinshi yayi mugun tashi,arayuwarshi ya tsani sauro ko miskala zarratin baisan halittar nan,bai taso a inda ke akwai taba,Amma yasanta sarai a matsayinshi na Dr yasan irin cututtukan da take haifarwa,Gashi ya tsani duk wani abu da zai naƙasa lafiyar jikinshi,tuni jikinshi ya soma kerma,hannu yasa ya ɗebe rigarshi gaba daya,ya shiga kokawar korarsu daga kusa dashi bayan ya kunna fitilar wayarshi dakin yayi haske,ji kake fass fass!kaff kaff!!haka ya dinga bubbugesu,duk yabi ya ruɗe,

Cikin bacci Sehrish ta dinga jin muryarshi yana faɗa da sauraye yana fadin"Don't come close to me!Am gonna shoot you"tashin hankali Sgr fa ya zauce da alama,duk sun rikitashi sun mayar dashi ƙaramin mahaukaci,Idan ya sanya riga bala'e biyu,ga zafi ga sauro,idan ya cire rigar kuma Sauraye zasu sha jini,bai da choice,
  A firgice ta farka,hankalinta a matukar tashe ta mike daga kwancen da take saman bedsheet ɗin,Wurin shi ta ƙarasa,yanayin da ta ganshi gaba ɗaya ya rikice ba ƙaramin tausayi ya bata ba,gaba daya yabi ya susuce ya hargitsa sumar kanshi,
   "Ya Rafayet,"ta ambaci sunan shi da wata irin kasalalliyar murya ta mai bacci,ƙoƙarin hawa saman gadon tayi don ta taimaka mashi ta kore mashi su,kafin su san abunyi,ae tana hawa saman gadon,ya ƙanƙameta ya rungumeta sosai,A faɗace yake ce mata ta kori saurayen su fita su bar ɗakin,ko ya harbesu da bindiga,tuni taji hawaye sun cicciko mata acikin idanuwanta,tsananin tausayinshi ne ya kamata,dama sai da Uncle yace bazai iya kwana a cikin gidan ba,Amma yace zai iya,wani iko na Allah,babu halittar da Sgr ke jin shakkarta irin sauro,Gashi Yau Allah ya haɗasu,ƙananun ƙwari sun firgita babban kwaro,Shaggu sun ga Farar fata,burinsu kawai su tsotsi jininshi,Dama abu tubarkalla masha Allah,
  gaba daya hannayenta na asaman bayanshi,ya cusa kanshi a kirjinta,numfashin shi da wani irin huci yake fita,
   Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Ya rafayet,dan Allah ka natsu,zanje wurin daddy na kar6o mana maganin sauron,"tayi maganar tana ƙoƙarin janye jikinta daga nashi,ƙin barinta yayi,yaƙi yarda ta motsa daga jikinshi,gani yake kamar in tabar wurin Saurayen zasu shanye mashi jinin jikinshi ne,
  Ganin yaƙi sakinta yasa takai hannu ta ɗauki rigarshi da yayi wurgi da ita gefe saman bedmattress ɗin,Ruƙo rigar tayi a hannunta,ta shiga kore mashi saurayen dake akewaye dasu,

Duk wannan budurin da akeyi,Abusufyan na kwance saman doguwar kujerar,Shi kanshi zafi ya ishe shi ga saurayen a kewaye dashi,Amma hakan baisa ya farka ba,sae faman juyi yake yi,
   (Allah sarki,haka talaka ke fama,da zarar an ɗauke da wutar nepa lokacin zafi,Ya rasa inda zaisa kanshi,ga sauro ga zafi,yayin da masu kuɗi ke can suna shan sanyin A.c,a lokacin zafi,idan kuma na sanyi ne su kunna room heater,Talaka kuma Ya hura garwashin wuta😥)

Jikinshi sae kerma yake yi,Duk da ya ɗan ji sauƙin Zafin saboda fiffitar da take yi mashi tana kore mashi saurayen,ko gajiya bata yi baiwar Allah,Haka ta hana idonta bacci,ta zauna tana kula dashi,sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi,har lokacin yana manne da ita,
   A hankali bacci yayi awon gaba dashi,kamar wani jinjiri,gyangyaɗi ta fara yi,tana fiffitar bacci na fisgarta,idanuwan nan sunyi jawur dasu,taƙi bari bacci ya ɗauketa,saboda gudun halin da Sgr zai shiga,idan ta daina yi mashi fifitar,
   Tafin hannunta ta sanya asaman fine face dinsa,ta shafa gefen fuskarshi har izuwa saman pink lips ɗinshi,kafin ta mayar da hannun saman dogon wuyanshi,fatar wurin tayi haske sosai mai matukar jan hankali,la66anta takai asaman cheek ɗinsa ta manna mashi kiss,ɗagowa tayi tare da aza tsinin hancinta cikin sumar kanshi,daddaɗan ƙamshin dake fitowa daga wurin ta dinga shaƙa,tana faman lumshe idanuwanta,da hannu ɗaya take yi mashi fiffitar,

  Tana cikin wannan yanayin,ta galabaita sosai saboda baccin da take ji,Ƴan nepa suka dawo da wutar,a hankali fankar ta soma jujjuyawa,nan take iska ta karaɗe ko'ina na bedroom ɗin,wani irin farin ciki ne ya ratsa zuciyarta,
   "Allah na gode maka,da suka dawo da wutar nan,nayi farin ciki sosai,"
   Lokaci guda Mosquitoes ɗin nan kowa ya kama gabanshi,saboda wutar mai ƙarfi ce,iska duk ta kaɗa shaggun,
  A hankali ta lalla6a ta janye Sgr daga jikinta,ya koma saman mattress ɗin,ta dauki wayanshi ta kashe fitilar ta daura ta saman bedside drawer,gefenshi ta kwanta,tare da jan bargo ta lullu6e jikinta,banda nashi saboda ta lura dashi baisan Zafi ko misƙala zarratin,

*Boss Bature*

Wuraren Sallar asuba,Abusufyan ya farka,Saukkowa yayi daga saman Sofa ɗin,yana faman murza wuyanshi,Wurin yayi mashi zafi saboda kujerar tayi mashi karanta,ya takure kansa sosai,Ƙopar ɗakinsu yaje tare da sanya hannu yana ɗan kwankwasa ƙopar,
   Sehrish ce ta farka,saukowa tayi daga saman gadon,sai da ta fara kunna hasken ɗakin,sannan taje ta buɗe ɗakin,
  "Daddy,"ta ambaci sunanshi,
"Na'am,Daughter,"
"Wlh jiya munji jiki daddy,dama haka Yaya Rafayet ke da jin Zafi? Ga sauraye suka takura masa,jiya daga ni harshi bamu samu isasshen bacci ba,"muryarta tamkar zata yi kuka tayi maganar,
"Ae dama saida nace mashi,Yaje hotel amma yaƙiya,banji daɗi ba gaskiya,duk ban shirya ma zama gidan ba,dana sani tun kafin muzo,nasa an gyara shi,An sanya generator da A.C an kuma yi mashi feshin maganin sauro,Amma ban yi tunanin hakan ba,Wllh koni jiya naji jiki,"
  Ya ƙarasa maganar tare da cewa"Yanzu ya yake?Yana lafiya kuwa,"?yayi tambayar yana jiran amsarta,
  "Ya samu bacci,da suka dawo da wutar,bansani ba ko yana lafiya ko kuwa,Still dai bacci yake yi bai farka ba,"
  Jinjina kai Abusufyan yayi tare da cewa"je ki taso munshi,Yazo mu tafi masallaci,Lokacin salla yayi,"
  "Toh daddy"tayi maganar tare da juyawa ta shige cikin ɗakin,

Yadda tabarshi haka ta same shi,kwance yana bacci,
  Zama tayi daga gefen gadon,sannan ta ambaci sunanshi"Ya Rafayet"!shiru bai motsa ba,sake kiran nashi tayi"Babban yaya ka tashi,time ɗin sallah yayi,"_
  Ganin yaƙi motsawa yasa takai hannunta saman damtsen hannunshi,ta ɗan bubbugashi,dogon numfashi yaja a hankali ya soma ƙoƙarin buɗe idanuwanshi,
  Biji biji ya fara ganinta,kafin idanuwan nashi suka washe,
  "Ankira sallah,Daddy yana jiranka a palour,"
  daƙyar ya iya furta mata Okey,miƙewa yayi daga zaune,yakai hannu ya ɗauki shirt ɗinshi,Ya zurata ajikinshi,Hada ido su kayi da ita,da sauri ta kawar da idonta gefe guda,miƙewa tayi daga tsaye,ta bashi wuri don ya wuce,
  Saukowa yayi daga saman gadon,Ya kama hanyar fita daga ɗakin,
  "Adawo lafiya,"
"Okey,"yasa kai ya fuce,

Bayan fitarshi,toilet ta shiga,ta ɗauro alwala,bayan ta fito ta ɗauko darduma ta shimfiɗa,a natse ta kabbara Sallah,tana gama yin sallar ta ɗebe hijabin ta ninke dardumar ta turasu cikin wadrobe,
  Wani irin bacci take ji acikin idanuwanta,saboda jiya bata samu isasshen bacci ba,Cire doguwar rigar jikinta tayi tare da sagala ta saman Murfin wardrobe ɗin,
  Toilet ta wuce,Saboda jikinta duk babu daɗi,After some minutes ta fito jikinta sanye da Brazier,tare da Short,farare,ba ƙaramin kyau su kayi mata ba,dama dasu ta shiga wankan,
   Tunda ta fito kuma,baccin ya ya ci gaba da addabarta don ba karamin dadin jikinta taji ba,bata samu ta sanya kaya ajikinta ba,Saman gadon ta haye taja bargo cikin ƙankanin lokaci bacci yayi awon gaba da ita,bata ƙara sanin inda hayyacinta yake ba,

*Marshal Omar*

Yayi nisa a cikin baccin shi,yajiyo muryar Hosana tana raira mashi waƙa,
    _Wataran wata rana_
   _za'a kaika gidana_
    _matsayin mijina_
    _kaine madara na_
_na matsu!na matsu na matsu inga wannan rana_
Cike da jan faɗa take yin wakar hada matsawa saitin kunnanshi,Rai a matuƙar 6ace ya farka,tare da wurga mata uwar harara,tana zaune saman gadon tayi zaman cin tuwo,
  A faɗace yace"Hosana!bana hanaki shigomin bedroom ɗina ba?Meyasa baki jin maganata ne"
  Hura mashi hanci tayi tare da murguɗa baki tace"Haramun ne idan nashigo ɗakin ɗan uwana,?to idan ma haramun ne,Sai ka aure ni kowa ma ya huta,"
Hannu yasa tare da dafe kanshi,yana faɗin"Allahumma ajirni fi masibati,wa'aklif ni khairan minha,"
  A ƙule tace"Ya Omar,Ni ce masifar"?
  Banza yayi da ita bai tanka mata ba,
  Jin yayi shiru yana kallonta,yasa tace"haushina kake ji ko?to ka kashe ni mana kowa ya huta,"
  Yunƙurawa yayi tare da miƙewa daga zaune,yace"Meyasa kike mun

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login