Showing 246001 words to 249000 words out of 432432 words
Chapter 83 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete
yaran ina mahaifiyarsu take ne?tana da asali kuwa"?tayi tambayar cike da son jin ƙarin bayani,
Hayamm tace"Ina fa,ae rannan na tambayi azmee game da mahaifiyarsu,shine take sanar dani cewa mahaifiyar yaran Ƴar fa mai gadin gidan gwaggon katsina ne!basu da wani asali,buzaye ne ƴan niger,"
Aunty babba tace"tabɗijancan aikuwa Ammi bazata ta6a yarda dasu ba,kinsanta ta tsani mutun mara asali,gata ita kaifi ɗaya ce muddin tace bata yarda dasu ba amatsayin ƴa'ƴan Abusufyan to fa korasu zatayi daga gidan,yakamata muyi wani abu akai,tun kafin takai ga zuwa,"
Hayaam tace"meke nan zamuyi?kinsan fa gobene walimar kuma gobe zata zo,"
"Abunda zamuyi shine,Ae ina da numbar Ammin a wayata,zanyi amfani da sabon sim ɗina,wanda ban fara amfani dashi ba,zan kirata na sanar da ita game dasu tunkan taji a wurin wani,"acewar Aunty babba
dariya hayaam tayi tare da cewa"Gaskiya aunty laila kin iya haɗa tuggu,ni sam banyi tunanin hakan ba,wannan ce hanyar da zamu bi wurin tarwatsasu,idan kika kirata awayar ki tunzurata sosai,ki ɗaurata akan network har sai ta amince da kalamanki,ki sanar da ita cewa yaran shaggu ne,abusufyan yayi ma mahaifiyarsu ciki a 6oye,shine suka so su 6oye mata,don karta sani,"
Murmushi Aunty babba ta saki tana cewa"hakan yayi sosai,zan tsara komai yanzu........."tana cikin maganar taji alamar dirar motar ishaq,
Cikin sauri tace"Hayaam inaso ki ɗauko min hoton yaran kafin muzo gobe,zan kashe wayar yanzu ishaq ya dawo,
"Toh aunty laila,zanyi ƙoƙarin ɗauko maki hoton nasu,"
Daga haka sukayi sallama da juna,
Ajiyar zuciya aunty babba ta sauke,har taji wani sanyi a ranta saboda ta samu mafita,
Bayan sun kammala wayar hayaam ta buɗe ƙopar ɗakinta tare da fitowa,cikin sanɗa hayam take tafiya don kar wani ya ganta,a haka har ta ƙarasa bedroom ɗinsu sehrish,tura ƙopar tayi cikin sa'a ta samu ƙopar ɗakin a buɗe,leƙa kanta ta fara yi anan ta same su,suna ta sharar bacci wanda tun bayan sallar Asuba da suka tashi suka koma suna yin baccin,
Murmushi ta saki tare da sa kai ta shige ciki,adai dai bakin gadon nasu ta tsaya tare da ɗago da wayarta dama already a cikin camera take,Saita fuskarsu tayi dama kuma duk suna facing ɗin ceilling,kyakkyawan hoton fuskokinsu ta ɗauka,bayan ta kammala ɗaukar hoton,ta lalla6a batare da kowa ya ganta ba,ta koma bedroom ɗinta,cikin sauri ta tura ma Aunty babba hoton ta whatsapp ɗinta,
❤🤍❤
Wuraren karfe takwas,suka farka daga bacci,sehrish ce ta fara shiga toilet tayi wanka,bayan ta fito daga wankan jahad ta shiga ciki,gaban dressing mirror ta zauna ta gama shafe jikinta,ta feshe shi da turare,sannan ta koma ta ɗauko Jallabiya fara ta zura ajikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,musamman adon dake jikin rigar na stones,shiya ƙara ƙawata rigar,bayan tayi rolling kanta da mayafin rigar,ta fito daga cikin bedroom ɗin nasu ta wuce kitchen,cike da zumuɗin kaima babban yaya breakfast ɗinshi gaba ɗaya ta manta da abunda Uncle abusufyan ya faɗa mata,
A kitchen ta samu azmee,har ta kusa kammala girkin,ganin yadda take ta aiki ita kaɗae yasa sehrish taji duk ba daɗi,muryarta a sanyaye tace"Ina kwana Aunty azmee,"
Juyowa tayi daga tsayen da take gaban gas cooker,fuskar nan ɗauke da murmushi tace"Lafiya lou ƴan matan abusufyan,fatan kun tashi lafiya"
"Lafiya lou,amma aunty azmee gaskiya banajin daɗi in naga kina aiki ke kaɗae,meyasa baki tashe mu ba,munzo mun tayaki aikin"?tayi maganar yayin da take ƙarasa shiga cikin kitchen ɗin,
Azmee tace"kada ki damu,na riga na saba da aiki,wannan ba wani abu bane,Abba ma ya nemi daya ƙaro masu aiki amma nace mashi ya barshi kawai,saboda na saba da yin aiki ni kadae,"
Girgiza kai sehrish tayi tare da cewa"that's impossible,gaskiya in har ba zaki amince a ƙaro masu aiki ba,to daga yau Ni dasu jahad zamu dinga tayaki aiki,don bazaiyiwu ba kiyi ta wahala ke kaɗai,"
murmushi kawai azmee tayi batare da tace Komai ba,
"Aunty azmee idan akwai abunda kika kammala inaso zan fara kaiwa dining in jera,kinga na rage maki wani aikin,"
"Ban kaiga shiryasu ba,amma sai dai idan zaki kaima Sgr nashi,sae na haɗa maki,ki kai mashi,"
Murmushi ta saki tare da cewa"Toh,"
Shirya mata breakfast azmee tayi acikin ƙayataccen tray,bayan ta kammala,sehrish ta ɗauki tray ɗin tare da fucewa daga kitchen ɗin,
tana cikin tafiya harta kusa hayewa upstairs taji anyi mata gyaran murya abayanta,cikin sauri ta juya don taga Wanene,ganin Uncle abusufyan yasa gabanta faɗuwa,saboda tana kallonshi ta tunano da abunda ya faɗa mata a daren jiya,
Muryarta na rawa ta furta"Daddy,"ƙarasawa yayi wurinta tare da tsayawa dab da ita fuskarshi a ɗaure yace"Me na faɗa maki jiya?tun yanzu zaki fara sa6amun"?
Hankali tashe sehrish tace"a'a daddy,wlh mantawa nayi,bazan ƙara ba,dan Allah kayi haƙuri,"
"Zo ki wuce ki mayar da kayan abincin kitchen,inyaso azmee taje takai masa,"
Jiki asanyaye Sehrish ta juya tare da kama hanyar komawa kitchen,duk wannan abun daya faru akan idon,Mommynsu junaid alexandra,tana tsaye abakin part ɗinsu na downstairs tana kallonsu,
Haka ta koma kitchen da kayan abincin idonta cike tab da hawaye,taci burin ta ganshi yau,amma Uncle abusufyan yayi mata tsiya,
Tamkar wadda aka zarewa laka haka ta shiga kitchen ɗin,Azmee na ganinta dauke da tray a hannu tace"Lafiya naga kin dawo da kayan abincin"?tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,muryarta tamkar zatayi kuka tace"Uncle ne ya hanani zuwa part dinsa da sunan aiki,tun jiya da daddare ya gargaɗeni akan Karna kuskura na ƙara yin aiki a ƙarkashinsa,bansan meyasa ya hanani ba,"
Cike da mamaki azmee tace"to fa!ko meyasa yayi hakan?kuma kin tabbata bakiyi wani laifin ba wanda yajawo har ya hanaki aiki a part ɗinsa"?
"Aunty azmee ni banyi laifin komai ba,"ta ƙarasa maganar a yayin da take ajiye tray ɗin hannunta,
Shiru azmee tayi aranta tana mai mamakin hukuncin da Abusufyan ya yanke ma sehrish,to kodai don saboda basa shiri da Alexandra ne?tabbas zai iya yiyuwa hakane!tunda akwai gaba atsakaninsu,dole kuwa ya hana Sehrish tayi ma Sgr aiki,don bazai ta6a yarda ƴarsa tazama baiwarsa ba,
"Aunty azmee ko zaki iya nema mun alfarma a wurinsa yabarni in cigaba da aiki acikin gidan nan kamar yadda na saba,"muryar Sehrish ce ta katse mata tunaninta,
zaro ido azmee tayi tare da cewa"Ni ƴar ubanwa?na isa in shiga tsakaninki da mahaifinki?bazaiyiwu ba sehrish,shawarar da zan baki shine kawai ki bi Umarnin mahaifinki ki xauna lafiya,Shi kaɗae yasan dalilinshi na yin hakan,kuma in har kika yi mashi biyayya zakiga ribar yin hakan,"
ɗakyar ta iya haɗiye yawun bakinta,ga hawaye sae faman zarya sukeyi a fuskarta,
"Wannan hukuncin da mahaifinki ya yanke,yayi mun dai dai,don koda bai dakatar dake daga yi mashi aiki ba,to ni dakaina zan hanaki!"
Gaban Sehrish ne ya faɗi rass jin muryar Mommynsu junaid abayanta,Azmee kuwa na ganinta tasha jinin jikinta don tasanta sarai bata da mutunci ta wani 6angaren,
Juyawa sehrish tayi da sauri tana kallonta,
A hankali take tunkararsu yayin da take ci gaba da magana"Banason kusancinki dashi ko kaɗan!just maintain a good distance between u and him,In ba haka ba,You will see the trouble!!"Jikin sehrish har kerma yake yi don ba ƙaramin tsoranta takeyi ba,koƙarin 6oyewa a bayan Azmee takeyi,don gani take tamkar Alexandra zata bugeta ne,
Koda ta ƙaraso dab dasu,harara ta wurga ma azmee tare da cewa"Matsa daga gabana,da ita nakeson magana,"jiki na rawa azmee ta janye jikinta gefe guda,aranta tace"tashin hankali ashe har yanzu matar nan,bata canza ba,lallai akwai matsala,"
goya hannayenta tayi asaman ƙirjinta,yayin da suke fuskantar juna ita da Sehrish,saboda tsabar tsoro ƙiris ya rage sehrish ta saki fitsari,ko idonta bata iya dagawa ta kalleta saboda yadda tayi mata tsaye aka,
Wani irin kallo Alexandra ke bin Sehrish dashi,tun daga ƙasa har sama,yatsina fuska tayi tare da cewa"Ur name"?
Murya na kerma tace"Sehrish,"
Jinjina kai alexandra tayi tare da cewa"saboda daddynki ya hanaki aiki a part ɗin rafayet shine kike kuka?why?
..girgiza kai sehrish tashiga yi tana cewa"a'a..ba saboda haka nake kuka ba...."
"Kukan menene toh"?ta sake jefa mata tambaya a karo na biyu,
"Babu komai,"ta bata amsa tana faman zazzare idanu,
Murmushin gefen fuska alexandra ta saki kafin ta kuma cewa"dama ana kuka ne just without any reason?ki faɗamun gaskiya mana,kodai kin faɗa tarkon shi ne"?
Waro ido waje Sehrish tayi hankali tashe tace"a'a ba haka bane,kawai ina kuka ne saboda tsoron hukuncin da babban yaya zai yanke mun in ya gane cewa na daina yi masa aiki,"
Ta6e baki alex tayi tare da cewa"Just calm down ur mind,Bama zai ta6a damuwa akan hakan ba,kiyi ma mahaifinki biyayya,kuma ki nisanta kanki dashi kamar yadda nace,hakan zaifi maki kwanciyar hankali,"tana kai ƙarshen maganarta,ta juya cike da isa tare da fucewa daga kitchen ɗin,
Fitarta keda wuya Azmee ta mayar da idonta kan sehrish saboda ta lallashe ta,amma ina,tuni sehrish ta watsa da gudu tabar kitchen ɗin,
A bakin ƙopar dakinsu ta tsaya tana faman shessheƙar kuka,zuciyarta har wani tafarfasa takeyi mata,dole tayi kuka saboda tasan cewa ta rasa Sgr na har abada,tunda mahaifiyarshi ta nuna bata sonta,zuƙunnawa tayi a ƙopar ɗakin tana cigaba da kukan nata,ta jima zuƙunne a wurin cikin wani irin yanayi mara daɗin ji,tana jiyo muryarsu jahad acikin bedroom ɗin,suna tattaunawa kan wankan da zasu ɗauka gobe ranar walima,hada zancen saloon ɗin da daddynsu yace zai kaisu ayau,
gaba ɗaya taji komai ya fita ranta,don har wani zazza6i taji ya saukar mata ajikinta,ita kaɗae tasan raɗaɗin da takeji acikin zuciyarta,hannu tasa tare da share hawayenta sosai don karsu hosana su gane cewa tayi kuka,bayan ta kammala goge hawayen ta miƙe,tare da buɗe ƙopar ɗakin tashiga ciki,
Jahad na zaune gaban mirror tana shafa powder a fuskarta,hosana kuma na tsaye gaban wardrobe tana cewa"Nama rasa wani kaya zansa yau,saboda inaso in na kammala shiryawa inje in tashi Ya Omar daga bacci don nasan cewa bai kaiga tashi daga bacci ba,"ta ƙarasa maganar tare da ɗan juyawa ta kalli jahad tace"daddy yace yau zai kaimu Saloon ko?to da yaushe zamu fita?donni hada ƙunshi za'ayimun a hannuna,yanzu ma in naje ɗakin ya Omar zan tambayeshi wani kalar ƙunshi yakeso ayimun baƙi ko ja," jahad tace"Soyayya daɗi,kunshin ma sai an tambayi ya omar wani kala yakeso kenan?to gyaran gashin fa?shi bazaki tambayeshi wani kala yakeso ba?
murmushi hosana tasaki tare da cewa"dole ma in tambayeshi wani kalar gyaran gashi yakeso ayi mun,"_
Suna cikin magana muryar Sehrish ta katse su da cewa"Ƴan uwana rabin raina,me kuke tattaunawa akai ne?naji kamar ana gulmar ƴa omar,ko kunnena ne,'tayi maganar tana ƙoƙarin danne damuwarta,gefen gadon ta samu ta zauna,tana faman sauke ajiyar zuciya,
.juyowa sukayi suna kallonta,hosana tace"Sehrish ina kika je,na tashi ban ganki ba,har naji tsoran kada ace wannan halittarce mai ƴan idanu ta ɗauke mana ke"
Dariya sehrish tayi tare da cewa"ni harna manta da wannan abun,koda na tashi daga bacci ban iya tuna abunda ya faru jiya ba,sae naji kamar duk a mafarki ne,"
Hosana tace"Ae taji tsoro ta gudu,yau da daddare in tadawo,zan aro bindigar yaya Omar in harba mata bullet acikin idanunta,"atare suka fashe da dariya jin abinda hosana tace,hada kwatantawa da hannunta yadda zatayi shooting din guguwar,
Jahad tace"Cika baki kawai,kin manta kukan da ki kayi mana ajiya?kinfi kowa tsorata,ba don nayi maki addu'ar ɗaukewar fitsari ba,da ba'asan me zai biyo baya ba....'dakyar ta ƙarasa maganar saboda dariyar da tazo mata,
cike da nishaɗi suke yin firar tasu,kafin lokacin yin breakfast yayi atare suka fita,Hosana ta wuce part ɗin Omar,yayin da su kuma suka wuce dining,Sehrish dae jurewa kawai takeyi,suk ta gaza sakewa saboda rashin sanya sgr a idanunta,gashi bai sauko downstairs ba,saboda Azmee takai mashi nashi a part ɗinsu,kuma sam bai tambayeta akan Sehrish ba,Hakan na nufin cewa Sgr bai damu da ita ba ko kaɗan,dama haroon yace Iskace ke wahalar da mai kayan kara,
Yana kwance yana sharar bacci,hosana ta shiga bedroom ɗin nashi,lalla6awa tayi ta haye saman gadon har wurinshi ta ƙarasa,saitin fuskarshi tana kallon zunzurutun kyawunsa,
Hura mashi iska tayi a fuskarshi,nan take ya ɗan motsa tare da yatsina fuskarshi,murmushi hosana ta saki tare da kai hannu ta toshe mashi hancin shi,aikuwa a gigice ya farka batare da ya sani ba ya tattara dukkanin ƙarfinshi ya cakumi hosana tare da yin wurgi da ita,gaba daya ta tafi yaraf ta kife ƙasan tiles ɗin daga gefen gadon,nan take ta fashe da kuka saboda hancinta daya daki ƙasa,shi duk atunaninshi wani ne ya kawo mashi hari shiyasa yayi mata haka,kuma yana yin wurgin da ita,yaci gaba da baccinsa,dama duk a cikin magagin bacci ne yayi mata hakan,
Cikin baccinshi ya jiyo sautin kukanta tana cewa"Wayyo Allah,hanci na ya fashe,ya Omar ka kashe ni,"
A firgice ya ware idanunshi tare da miƙewa daga zaune yakai idanunshi wurin da sautin kukan ke fita,anan ya samu hosana dafe da hancinta a zaune dirshan tana kuka,
Hankali atashe ya sauko daga saman gadon ya zukunna agabanta yana tambayarta lafiya?garin yaya taji ciwo a hancinta,
Cikin shessheƙar kuka tace"bakaine ka cakume ni ba,kayi wurgi dani daga saman gado na faɗo ƙasa har hancina ya bugu,"
Waro ido waje yayi tare da cewa"Ni kuma dakaina"?
Jinjina kanta tayi tare da cewa"Eh mana,saboda kawai na toshe maka hanci,
🙏🙏🙏
*💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*
❤🤍❤
*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*
Hannu yasa tare da tallabo fuskarta yace"Hosana bada sani na nayi maki hakan ba,laifin ki ne,meyasa zaki toshe mun hancina?so kike na mutu'?
Girgiza kai tayi"a'a,banso ka mutu,ae ni wasa nayi maka ko,"tayi maganar tana satar kallon fuskarshi,
"Faɗa mun me ya kawoki bedroom ɗina har saman gadona"?
A ƙule tace"nifa nazo ne na tashe ka don kaje ka ci abinci,naga kowa ya fito banda kai,kuma zasu iya cinye abincin duka,"
fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Waya faɗa maki za'a cinye abincin,ae ko ban fita ba Azmee zata kawo mun ne har cikin part ɗina,"
Shiru tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,ɗagowa ta ƙara yi zata saci kallonshi suka haɗa ido,ganin yadda yake kallonta ko ƙyaftawa baiyi hakan yasa ta ɗaure fuska cikin shagwa6a tace"Ya omar wannan kallon fa,ka wani tsare ni da ido,"
yadda tayi maganar ba ƙaramin burgeshi tayi ba,ya jima yana kallonta batare da yace wani abu ba,har sai da ta hasala rai a6ace tace"shikenan tunda ba zaka mun magana ba,bari na tashi na tafi,dama ko abincina banci ba,saboda kawai inzo in tashe ka daga bacci,amma ko farin ciki ba kayi ba,'
Ajiyar zuciya ya sauke tare da ruƙo hannunta cikin nashi"Hosana,so nake ki faɗa mun gaskiya,kina sona da gaske?kuma zaki aure ni? Waro ido waje hosana tayi tana kyakkyaftasu kamar na ƴar tsana jin abunda yace,a ruɗe tace"Ya Omar!aure fa!"_
Jinjina mata kai yayi tare da cewa"eh,aure hosana ko baki shirya ba,"
Turo baki ta ɗanyi tana ƙunƙuni ƙasa ƙasa,hankalinsa kam harya ɗan tashi saboda ganin yadda ta tsorata don yayi mata zancen aure,dama fargabarsa kada sai anje wurin nema mashi auranta tace bata shirya ba,don yasan ba cikakken hankali gare ta ba,
Lalla6ata ya shiga yi"pls hosana,ki faɗamun gaskiya,zaki aure ni"?
daƙyar ta iya buɗe baki tace"Ni yanzu tashi zanyi in tafi,dama zuwa nayi fa don in tambayeka,wani kalar ƙunshi kake so ayimun baƙi ko ja,"
ya lura cewa batason zancen auren shiyasa ta kawo maganar ƙunshin,cikin sanyin murya yace"Nafison jan lalle zai fi yi maki kyau,kuma ba mai yawa ba ƙunshin,ƴar flower kawai za'a zana maki mai kyau,"
Yana kai ƙarshen maganar,hosana ta miƙe tana faman shan ƙamshi,da sauri ta juya ta bar bedroom ɗin nashi,bin bayanta yayi da kallo har ta fuce,jiki asanyaye ya miƙe tare da nufar toilet ya shige,
Hosana na fita daga cikin bedroom ɗin nashi,a falonsa ta tsaya tana faman zabga murmushi,tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha,Yau ya Omar ya nuna yana sonta harma yanayi mata zancen aure,ta rasa ma wa zata fara faɗamawa,sai faman zagaye zagaye takeyi a cikin falon,
Wuraren ƙarfe biyu da rabi na rana,Abusufyan ya ɗaukesu acikin motarshi kamar yadda yayi masu alƙwarin kaisu wurin saloon da kanshi,hosana da jahad suna a bayan motar duk sun ɗau wankan jallabiya sun laga mayafi,Sehrish na agaban motar kusa da driver seat inda Uncle abusufyan ke zaune yana driving ɗinsu anatse,Su jahad da hosana sae fira sukeyi tare dashi,amma ita ko uffan bata tanka masu ba,dama tunda ta shigo cikin motar Abusufyan ya lura da yanayinta,
gyaran murya yayi mata hakan yasa ta ɗan dago da kanta ta kalle shi,
"Meyake damunki ne Daughter?tunda kika shigo cikin motar nan baki tanka mana ba,ga ƴan uwanki suna ta fira a tsakaninsu amma ban dake".
Muryarta asanyaye tace"Babu komai,"
"ko don saboda na hana ki kai ma Sgr abinci ne"? Yayi maganar batare daya kalleta,
Cikin sauri tace"a'a ba haka bane,kawai bana jin daɗin jikina ne,"
"Ban yarda ba daughter,saboda shi ne yasa kika shiga damuwa,"_
Shiru tayi bata ce komai ba,murmushi abusufyan yayi kafin yace"banyi hakan don na takura maki ba,face don na ɗaukaka darajarki,nasan ba zaki fahimce ni ba a yanzu amma nan gaba da kanki zakiyi mun godiya akan hakan,idan kuma hakan ya 6ata maki rai,kiyi haƙuri,'ya ƙarasa maganar adai dai lokacin da suka ƙaraso wurin Saloon ɗin,parking ɗin motar yayi jahad da hosana suka fita waje,tana ƙoƙarin buɗe motar ta fita ya ambaci sunanta"Sehrish,"juyowa tayi tare da kallon fuskar daddyn nasu tace"Na'am daddy,"
"Murmushi kawai nakeso kiyi mun kafin ki fita,"
fashewa tayi da dariya har fararen hakoranta suka bayyana,duk a tunaninta wani abu mai muhimmanci ne yasa ya kirata,ashe kawai don ya tambayi murmushinta ne,shima dariyar yakeyi,kafin su fita daga cikin motar atare,
**************
Fitowarshi kenan daga wanka,yana cikin shirya kanshi cikin riga da wandon jeans,yaji an kwankwasa ƙopar ɗakinshi,daga muryarshi yayi tare da cewa"ƙopar a buɗe take,"yayi maganar tare da juyawa yana kallon mai shigowar,
Cike da mamaki yace"Ya HAROON!kaine!dama kana nan,"
Shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare da ƙarasa shiga cikin bedroom ɗin nashi yana cewa"Ina nan mana junaid,kaine ka manta dani,kowa ma ya manta dani,"
"Ya haroon ba haka bane,wlh ni ban manta dakai ba,kana araina,"
ta6e baki haroon yayi alokacin da yake tsayawa agaban junaid suna fuskantar juna yace"Ka ƙara kyau da haske,hankalinka kwance baka da wata damuwa,ba kamar ni ba,kullum cikin damuwa nake,zuciyata har nauyi takeyi mun saboda halin da nake ciki amma babu wanda ya damu dani,yau ko mutuwa nayi babu wanda zai damu,sae ma farin ciki da za'ayi,"
Jin wannan maganar ta haroon yasa jikin junaid yin sanyi,wani irin tausayin shi ya kamashi,muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"pls Ya haroon dan Allah kadaina faɗin wannan maganganun,wlh bana jin daɗi,"
"Junaid ƙarya nayi ne?an damu dani acikin gidan nan ne?kowa yayi watsi dani,babu wanda ke damuwa dani,tamkar bare haka nakeyin rayuwata,hatta azmee da