Showing 123001 words to 126000 words out of 432432 words

Chapter 42 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete

kalleshi ba tace"Zan kiraka a waya,in nasamu lokaci,ta bude back door ta dau jakanta"
Jiki asanyaye Sofwan yaja motar,yayin da zuciyarshi ke cike da 6acin ran abunda tayi mashi,yasha wahalar kawota,amma ko godiya babu balle yayi tunanin sake samun wani abu awurinta,tuni yaji hawaye sun cika mashi idanunshi,tabbas hayam ta cuce shi sosai ba ƙaramar wahala yasha akanta ba,duk don ya mallake ta amma gashi nan ya tashi a tutar babu!dashi da Zero basu da bambanci ƙwara ma zero yana da amfani wurin yin lissafi,

Shu'umin murmushi haroon ya saki lokacin da hayaam ta ƙaraso jikin motar tashi,hannu tasa tare da buɗe gaban motar tashiga ta zauna tare da rufe motar,sannan ta mayar da idonta akan haroon daya zuba mata ido ko kyaftawa baiyi,
ita kanta saida tasha jinin jikinta da ganin irin zubin shi,cikin sanyin murya tace"Sannu ko,"
ɗan ta6e la66ansa yayi tare da cewa"Yawwa,amma naga baƙuwar fuska ina buƙatar ƙarin haske,"
Cike da kwarkwasa tace"Sunana Hayaaam,ni ƙanwar Aunty laila ce da kuma Aunty Amani,"
murmushin gefen fuska haroon yasaki kafin yace"Wow,no wonder that's why naga kamanceceniyar ki da Aunty laila,ashe ke ƙanwarsu ce,amma fa am really sorry game da abunda ya faru,securities ɗin gidan nan basu son ciwon kansu ba,in ba haka ba taya zasu ga mace kamila irinki sanye cikin dogon hijab kuma su hanaki shiga?
Sunnar dakai Hayaam tayi tana faman sakin shu'umin murmushi,aranta tace"dalilin dayasa na sanya dogon hijabi kenan saboda nasan cewa kowa zaiyi tunanin ni mutuniyar kirki ce,hmmmmm basu san cewa da fuska biyu nazo masu ba,"
(Rashin sani yafi dare duhu!hayaam batasan da wa take magana ba,"
"Kada na cika ki da surutu,bari nashiga dake cikin gidan,"
Ya faɗi tare da jan motar da gudun gaske ya shige cikin babban gate din gidan
(Finally hayaam ta samu nasarar shiga cikin gidan) 

*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃


*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*

*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*


*LOCATION KANO*

08062073990

Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka
Wadrobe balls
Madarar kulleccham
Vaseline kulleccham
Kajiji
Halut
Couscous
Khumrah
Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka
Wadrobe balls
Madarar kulleccham
Vaseline kulleccham
Kajiji
Halut
Couscous
Khumrah
Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku

It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.
Snack
Awarah
Farah
Zobo
Samosa
Cup cake etc
Contact me 09063302182or 09012179727.

Abban sojoji part 2 �?
Bayan Haroon yayi parking ɗin motar,hayaam tayi mashi godiya tare da ɗaukar bag ɗinta,ta fito daga cikin motar sannan ta nufi cikin gidan,
  Shu'umin murmushin nan nashi ya saki yabi ta da kallo tare da cewa"Nifa bana abu don Allah,kowani tsautsayin ne da ƙaddara suka kawo ta cikin gidan nan!Allah yasa ta kwanan mana biyu...." ya jinjina kai tare da cewa "tsuntsu daga sama gasasshee!"ya ƙarashe maganar tashi tare da zura hannun shi cikin aljihun jeans ɗin dake a jikinshi,wayar shi ya ciro tare da duba screen ɗin, missed calls aka mashi da wata hidden number,
    shiru yayi yana tunanin taya zai bi kiran saboda kira ne mai mahimmanci a wurin shi gashi dole sai in shi mai 6oyayyiyar numbar ne ya kira ka,
  Yana cikin wannan tunanin sai ga kiran ya sake shigowa,cikin sauri yayi picking call ɗin tare da kara wayar a kunnan yana jiran jin me za'a sanar dashi
  Wata irin muryace ta irin hamshaqan matan nan waɗanda suka ji duniya ta soma magana"Haroon!kana shirin jamin bala'e ko?meyasa ka fiye shiririta ne?ko kamanta plan ɗin mu ne"?
   nan take haroon yashiga en ina murya na rawa yace"ban manta ba,inaso nabi komai a hankali......'bata bari ya ƙarasa maganar ba ta kwatsa mashi tsawa"Ya isa Haka! kasani wlh akanka bazan bari nayi gangancin rasa damar da nake da ita ba!haroon zaka iya rasa ranka muddin kace zaka kawomin wasa acikin lamarina!kai kasan wacece NI!bani da imani,"
  Wata irin zufa ce ta soma gangaro mashi daga cikin sumar kanshi,lokaci guda duk yabi ya rikice yashiga zazzare idanu,
   sautin dariyarta ce ta karaɗe kunnan shi,tsagaitawa tayi da yin dariyar sannan ta sassauto da muryarta wurin cewa"Am sorry fa,na tsorata ka ko?
Nannauyar ajiyar zuciya haroon ya saki tare da cewa"Yanzu me kike so ayi ne,just command me zanyi maki koma menene,"!
   "So nake ka kashe JUNAID!saboda shikaɗai ne hanyar da zanbi wurin ƙuntata masu,banaso junaid ya rayu,muddin yana araye toh farin cikin gidan zai cigaba da wanzuwa ne,ni kuma abunda bana so kenan!,"
     girgiza kai haroon yashiga yi tare da cewa"Kiyi haƙuri wannan ne karo na farko da kika ban umarni na musa maki tunda na fara maki aiki!junaid is innocent  I can't kill him,zan iya kawar maki da duk wanda kikeso acikin gidan nan,Amma banda junaid!banda Abbana,Rafayet kuma yafi ƙarfina banda wata hanyar da zan iya cutar dashi,sai ma in jefa kaina cikin matsala!"
   fashewa da dariya tayi tamkar zata fasa screen ɗin wayar,bayan ta tsagaita da yin dariyar taci gaba da magana"kasan koni wacece,kasan kuma abunda zan iya!idan har bazaka iya kawar mun dasu ba,to ni zan iya kawar dasu ta cikin ruwan sanyi,Haroon u must do what i command you!if not i wll expose ur secrets,kai kasan me zai biyo baya,ko ka kashe junaid ko kuma ni in kashe maka rayuwa gaba ɗaya...!!!!
   Waro ido waje Haroon yayi yana sauraronta,
  Cigaba da magana tayi"Maganar videon su Twins daka ɗauka,nasan ka goge na wurinka,amma akwai wani a hannuna,zanyi amfani dashi wurin tarwatsa zuciyar mahaifin nan nasu,da kuma masoyina Rafayet!inason ganin tashin hankalin shi sosai...."
  A tsorace haroon yace"Kada ki kuskura ki saki bidiyon nan!in ba haka ba asirina zai tonu ne!kuma kina sane da cewa,muddin asirina ya tonu to ke ma kin gama yawo!!atare zamu fuskanci sakamakon mu,zasu kamo ki ne aduk inda kika 6uya!!"
    ya ƙarasa maganar yana faman sakin huci yayin da idanun shi sukayi jawur saboda tsananin 6acin rai,
   fashewa ta kuma yi da wata irin mahaukaciyar dariya kafin ta tsagaita da yin dariyar tace"Haroon!Iska bata ruƙuwa!domin ni tamkar iskar nake,kada kamanta ina amfani da baƙaƙen aljanu wurin gudanar da aiki na,kuma zanyi amfani dasu ne wurin ganin na tarwatsa dukkan zuri'ar Salahuddeen Hussein!wannan alwashi ne na ɗauka,rai uku masu mahimmanci suka kashe mun,ni kuma rayuka zan ɗauka!don bana yafiya arayuwata!"
  Shiru yayi bai ce komai ba kusan minti biyar, sam baison wani abu ya samu abbanshi shi kaɗae yafi ji sannan yace"Maganar yaran nan fa?su kuma ya zakiyi dasu?
   "Inaso saina fara sanya soyayyarsu acikin zukatan ƴan uwansu sosai,saboda inaso inyi amfani da wannan damar ne wurin ƙuntatawa dukkan wani jin daɗi na zuri'arsu,kamar yarda suka ƙuntata ma tawa zuri'ar,"
    Jinjina kai haroon yayi kafin ya kuma cewa"Yanzu menene plan ɗinki"?
   Wannan karan anatse ta soma magana"plan ɗina shine kawar da junaid,dalilin dayasa nakeson kawar da junaid shine!sihirina bazai ta6a tasiri akan Rafayet ba har sai an samu lagwanshi,kuma ba kowa bane lagwanshi ba fa ce Junaid,da zarar ya rasa junaid zaiyi sakaci da ibadarshi hakan zai bani damar yin aiki akanshi,kuma shi ya kasance Bugun zuciyar family ɗinsu inaso na ɗanɗana masu raɗaɗin rasa mutumin daka kwallafa rai akansa!sannan maganar bidiyon nan zan sake shi a social media kowa ya gani,daga zarar hakan ta faru nasan cewa Martabar family ɗinsu da kuma ƙimar da suke dashi a duniya gaba ɗaya zasu zube,kowa zai tsani zuriyarsu duk wata daraja da suke dashi a idon duniya zata tashi abanza ne!ni kuma hakan nakeso,kafin na saki bidiyon inaso kayi amfani da kuɗin da suka baka wurin barin ƙasar,ka koma malaysia da zama,na shirya maka komai najin daɗin rayuwa acan,giya da mata har saika gaji dasu,"
   shu'umin murmushin nan nashi ya saki aranshi yana ayyana irin rayuwar da zaiyi acan cikin daular da aka shirya mashi,nan take yaji cewa zai iya aikata komai takeso,
  Sam yama manta da waya yake yi saboda tsabar farincikin da ya ziyarce shi,mayar da bayanshi yayi a jikin seat na motar yana cigaba da sakin murmushi,
   "Kana jina kuwa,"muryarta ce ta ratsa kunnan shi,hakan yasa ya dawo daga dogon tunanin daya tafi,
   Sai da ya samu natsuwa sannan yace"Naji duk abunda kika ce,hakan yayi mun sosai,musamman da kika ambaci giya da mata,sai naji wani nishaɗi araina dama irin rayuwar da nakeson yi kenan,amma akwai wata shawara da nakeson baki,in ba damuwa,"
  Tace"ina sauraronka haroon,"
"Ga me da bidiyon tsaraicinsu twins,kada ki sake shi a social media pls,sun riga sun biyani kuɗi kamar yarda na buƙata,shiyasa nakeso ayi masu sassauci,mutun biyu kawai nakeson suga bidiyon nan Abban su da kuma wannan ifiritun sarkin jin kan nan,sannan maganar kashe junaid nasan ban isa na hanaki aikata abunda kika yi niyya ba,amma abunda nakeso ki bar komai a hannuna,ni ko ke babu wanda zai kawar dashi!kiyi amfani da sihirin ki kawai ta cikin ruwan sanyi yarda babu wanda zai zarge ni!!"
     Dariya sosai tayi da alama shawarar Haroon tayi mata,
   Sannan tace"daga yau komai zai fara"!!!
murmushi haroon ya saki tare da cewa"Allah yaba mai rabo sa'a"
  daga haka su kayi sallama ya kashe kiran,kasa fitowa daga cikin motar yayi ba don komai ba sai don kasalar da yaji ta baibaye shi,fuskar junaid kawai yake gani acikin idanun shi,😢

   ******************
Lokacin da Hayaam ta shiga cikin gidan da sallama abakinta tashiga main palour ɗin,tsayawa tayi da tafiya ganin babu kowa acikin babban falon,takun tafiyar da taji ne yasa ta juyawa ta gefen hagunta tana kallon mai tafiyar,bakowa bace face Sehrish sai faman sauri take yi don ta shiga kitchen,har yanzu shigar ɗazu ce a jikinta,amma ta yafa mayafi ajikinta tayi rolling ɗinshi,
   ta wutsiyar idonta ta hangi mutum hakan yasa ta dakata da yin tafiyar ta ɗan juya don taga wanene,karaf idonta suka haɗu akan na Hayaam,cike da mamaki take kallonta,batasan ko wacece ita ba,amma ganin hasken fatarta yasa tayi tunanin ko ƴar uwarsu Junaid ce,
   tunkararta sehrish tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta ƙarasa inda hayaam take,tunkan sehrish ta ƙaraso zuciyar Hayaam ta shiga bugu,don ta gane cewa itace Ƴar aikin da Aunty laila take bata labarin cewa tana rayuwa acikin gidan,yarinyar da Abbansu ya mayar da ita ɗiyar shi,
   fuska ɗauke da murmushi sehrish tace"Sannu da zuwa,"
   hayaam tace"yawwa,ina mutanen gidan nan?naji shiru ko ba kowa ne"?
  sehrish tace"duk sun fita,amma junaid da Fawan suna acikin bedroom ɗinsu,sai Aunty azmee tana acan cikin kitchen,
   Jinjina kai Hayaam tayi har ta buɗe baki zata kuma cewa wani abu,sai ga Azmee ta fito daga cikin kitchen ɗin,ganin Hayaam yasa ta soma Sakin fara'a kamar gonar auduga,cikin sauri ta tunkaro wurinsu tana cewa"Wata sabon gani!Anya ba idona ne ke nuna min badaidai ba?
  dariya hayaam tayi tare da wuce sehrish ta tunkari wurin Azmeen suka rungume juna,
  ɗago da ita azmee tayi daga jikinta tana cewa"Oh ni Hayaam!ashe dama zan sake ganinki a duniyar nan?gaskiya kun yada zumunci!ina ji tun bikin Amani yaushe rabon ki da gidan nan!
   Sai faman washe baki Hayaam takeyi ba don komai ba sai don sanin cewa Azmee zata kar6eta hannu bibbiyu kuma zata goya mata bayan zama acikin gidan,
     "Kai Aunty azmee,nafa zo bayan bikin Amani kin dai manta ne,gaskiya nayi missing ɗinku sosai,shiyasa ma nace dole nazo naganku,"
  Magana takeyi amma hankalinta na akan Sehrish,dake tsaye tana sauraronsu,
   Azmee tace"mu ma munyi kewarki sosai,amma dai bada wuri zaki koma ba ko?don bazan bari ki tafi batare da kin zauna mana ba,". 
   Anzo wajen da tafiso nan fa tashiga washe baki tana cewa"ae Aunty azmee har sai kun gaji dani,in dae ba ku kuka kore ni ba,amma ni ina nan ba inda zanje,"
  murmushi Azmee tayi tare da cewa"Ae bama wanda zai kore ki hayaam,".
  taƙarasa maganar tare da mayar da idonta kan sehrish tace"wannan Hayam kenan!ƙanwar matar yayansu ishaq,da kuma Amani wadda tazo ran nan harna gabatar maki da ita"?
  wani irin bugu taji zuciyarta tayi mata ba don komai ba,sai don tuna kalaman Amani da tayi in har wannan takasance ƙanwarta ce,lallaikam akwai matsala,
  da ƙyar sehrish ta ƙaƙalo murmushin yaƙe sannan tace"Allah sarki,ashe kanwarsu ce,naga suna yanayi da Aunty amanin,"
   ta6e baki hayaam tayi jin abunda sehrish tace,
   ruƙo hannunta Azmee tayi tare da cewa"Kada na cika ki da surutu,mu shiga ciki ki huta don nasan ba ƙaramar gajiya kika kwaso ba,"
  atare suka wuce ciki da Azmeee,zuru sehrish tayi ita dai tun da tayi arba da Hayaam taji sam bata kwanta mata arai ba,kama hanyar shiga kitchen ɗin tayi tana cikin tafiya taji muryar junaid ya ambaci sunanta,
   dakatawa tayi da tafiyar sannan ta ɗan juya tana kallon shi,fuskar nan tashi a yamutse alamar daga bacci ya tashi,sai faman sakar mata wannan kyakkyawan murmushin nashi yake,
   acikin ranta tace"Shagwa6a66e halan yunwa yake ji ne,"
   ƙarasa saukowa yayi daga saman stairs ɗin kai tsaye wurinta ya nufa,
     Lokacin da ya ƙaraso inda take tsaye muryar shi cike da kasala yace"Reesh har yanzu Abbanmu bai dawo ba"?
ɗaga mashi kai tayi alamar eh,tamkar zaiyi kuka yace"dama nasani,tunda wannan abokin nashi yazo mai farin gemu,nasan cewa ba zai barshi ya shigo ciki ba,yana can yaja shi sun tafi yawo gidan abokanansu,"
  maganar shi ba ƙaramin dariya taba Sehrish ba,
   "Amma dae baka da mutunci junaid,abokin abban naku ne kake ce ma mai farin gemu"?
   turo baki yayi cike da shagwa6a yace"eh mana,farin gemu gare shi,ae ba ƙarya nayi ba,
Ya ƙarasa maganar da cewa"nidai yanzu ki taimakamin bana jin daɗin bakina farfesu nakeson sha,"
   bin lips dinshi tayi da kallo yarda yake magana ashagwa6e,sunyi dark red dasu kamar wanda yashafa jan baki,
      Tunanowa tayi da maganar shi ta ɗazu da ya furta mata kalmar so,acikin ranta tace"yanzu ace dagaske junaid sona yake yi,tabbas zan iya haƙura da wanda nakeso don na aure shi,saboda ba ƙaramin tausayi yake bani ba,komai nashi kuma yana burgeni,sai dai bansan ya rayuwar auren mu zata kasance ba,yarda yake shagwa6a66en nan ba ƙaramar wahalar shi mace zata ci ba,wannan rainon shi ma zanyi kenan?kullum sai ya tashi tsakar dare da kukan rigima,don haka sai in tanadi feeder da zan rinƙa haɗa mashi madara yana sha.......'
Kasa ƙarasa zancen zucin nata tayi saboda dariyar data zo mata,tafin hannunta tasa tare da rufe bakinta,ta ƙumshe dariyar don karta fito da ita,junaid ya gani ranshi ba ƙaramin 6aci zaiyi ba,
  Harara ya watsa mata tare da cewa"meyasa kike kallona ne?kuma kinsa hannu kin rufe mouth ɗinki da alama baki da gaskiya sehrish,"
   kafin tace wani abu,sai ga haroon ya faɗo cikin main palour ɗin,jin takon tafiyar shine,yasa gaba daya suka juya suna kallon shi,adaidai lokacin shima ya ɗago da idanunshi kai tsaye suka sauka akansu,
Nan take sehrish taji gabanta ya faɗi rass,saboda ta tsani ganin shi acikin idanunta,
  da alama wurinsu yake tunkarowa,murmushi junaid ya shiga sakar mashi yana cewa"Ya haroon sannu da dawowa,"
    "Yawwa baby junaid,me kuke yi anan ne"?
.   yayi maganar yayin da yake ƙarasawa wurinsu,
   sunnar dakai sehrish tayi batare da ta ɗago sun haɗa ido dashi ba,
  Junaid yace"muna magana ne da sehrish,"
  ɗan ta6e bakin shi yayi kafin yace"okey,ka wuce ciki inason magana da ita,"
   batare da musu ba junaid ya wuce cikin palourn tare da samun wuri saman 3 seater ya zauna,
    ja da baya sehrish tayi aɗan tsorace tana jiran jin mai zai ce,
   "Kinyi kyau sosai,shigar jikin ki tayi mun,"ya fadi yana faman bin wandon jikinta da kallo,
   Shiru tayi mashi batace komai ba,jira kawai take yayi ƙoƙarin ƙure mata ta watsa a guje,
   "dama nasan ba zaki ce komai ba,hakan yayi mun sosai,bakomai ne yasa nace inason magana dake ba face don in baki wata shawara mai kyau,sai dai bansan ko zaki ɗauka ba
  Sai lokacin ta ɗago da idanunta tare da kallon shi tace"wata irin shawara kenan?kada kayi tunanin cewa zan ɗauki shawarar ka,saboda kai ba abun yarda bane!nagama yarda da duk wani abu da zai fito daga wurinka,burinka kawai ka cutar dani!"
   hannunshi ya zura acikin aljihun shi tare da ƙara matsawa dab da ita yace"shawarar ba akanki bane!akan junaid ce!
   daram!!taji gabanta ya faɗi a ɗan rikice take kallon shi,
   "Nasan tunda na ambaci sunan junaid,yanzu zaki so ki saurari me zance,don na lura ba ƙaramin jinshi kike yi ba,"
  Murya na rawa sehrish tace"me...me..kake son cewa ne agame da junaid?me junaid yayi ne?
    Maimakon ya bata amsar tambayarta sai cewa yayi"ran nan nayi maki ƙarya na cewa ni shaiɗanin aljani ne,wannan maganar ba gaskiya bace,abunda ya faru shine akan idona Omar yashigo cikin falon nan kai tsaye naga ya wuce upstairs sai raina ya bani cewa dole zai ji sautin kukan ki,kasancewar part ɗinshi dana sgr basu da tazara sosai a tsakaninsu,maganar cewa ni na shaƙe maki maƙoshinki alokacin da kika zo ambaton sunana agaban Marshal Omar shima duk ƙaryace,bani nayi maki hakan ba,kawai nayi guessing ne kuma da alama na canka dai dai,nasan kin tsorata alokacin kuma kinyi tunanin cewa ni ba Mutum bane,don haka inaso kisa aranki cewa Ni haroon cikakken mutum ne kamar kowa,"yana ƙarasa maganar tashi yasa ƙafa zai wuce

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login