Showing 345001 words to 348000 words out of 432432 words

Chapter 116 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete

matuƙar razanarwa,tashin hankali,A firgice junaid ya ware idanuwanshi shi kaɗae asaman gadonshi,Gabanshi ne ya faɗi rass!sakamakon Mutun daya gani tsaye agaban mirror ɗinshi sanye da baƙar jallabiya mai hula,a wani irin firgice junaid ya miƙe zaune tare da toshe kunnanshi ya fasa ƙara mai sautin gaske yana ambaton sunan Daddynsu maimaikon sunan Allah,
   Sosai ya shiga ja da baya,Hankalin shi a matuƙar tashe la66ansa na kerma ya shiga faɗin"Daddy!Mommy!Ya Rafayet!ya Omar!kuzo ku taimake ni!nashiga uku!dodo acikin ɗakina!Kashe ni zaiyi,'
   Ƙwayar idonshi tamkar zata faɗo waje saboda tsabar tsoro,
   Mutumin dake tsaye agaban madubin,wasu irin zaƙwa zaƙwan Akaifune a hannunshi,tsininsu tamkar na wuƙa,Ga uban gashi ajikin fatar hannunshi,juyowa yayi junaid na ganin fuskarshi ya rikirkice ya ruɗe,uban gashi ne ta ko'ina asaman fuskarshi,Ga wasu irin dogayen haƙora dake gareshi har sun sauko daga bakinshi,Idanuwanshi kuwa wa'iya zubilla,
  Gadan gadan ya tunkari junaid,A wani irin Sukwane,junaid ya wuntsilo daga saman gadon har yana tuntu6e wurin ƙoƙarin fitowa daga cikin bedroom ɗinshi,fisgar ƙopar yayi dama a buɗe ya barta,da gudun gaske ya fito tare da nufar bedroom ɗin Sgr yana kuka,Sai dai kafin ya ƙarasa wurin part din nashi,Sai ga wannan Mutumin ya bayyana,A gigice junaid ya fasa ƙara ya canza hanya ya nufi part ɗin marshal Omar,Nan ma kafin ya isa,Sai ga mutun ya ƙara bayyana,A galabaice ya sauko daga downstairs,bawan Allah Ya rasa wurin wa zashi,gashi duk ihun da yake yi yana kuka babu mai jin shi,
  *Junaid*!
Muryar jahad ce ta katse shi,da sauri ya juya wurin da sautin ya fito,a tsaye take tana kallonshi da gudun gaske ya nufeta tare da faɗawa jikinta ya ƙankameta yana faɗin"dodo!dodo!"
  
Bugun ƙafarshi da akayi ne yasa shi yin firgit ya farga daga baccin da yake yi,Duk zufa tabi ta jiƙa jikinshi sharkaf,kukan da yake yi acikin mafarkin har azahiri yake yinshi hannunshi rungume da pillow,
  Biji biji ya fara gani acikin eyes ɗinshi kafin idon nashi su washe,
  A hankali ya ambaci sunanta"Aunty Azmee,"yayi maganar tare da tashi daga zaune yana kallonta,
   "Meya faru dakai ne junaid?tunda nashigo nagan ka kana ta koke koke cikin bacci,"ajiyar zuciya ya sauke tare dakai idonshi kan wall clock ƙarfe 9 na safe,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,Ko sallar asuba baiyi ba,
  Cike da damuwa yace"Aunty Azmee wani mummunan mafarki nayi wallahi,Na tsorata sosai,Amma dana farka na ganki sae hankalina ya kwanta,Allah na gode maka da ya kasance ba gaske bane,da yanzu shikenan Na rasa rayuwata,"
   Zama azmee tayi daga gefen gadon mashi,cike da kulawa tace"Junaid!Anya kayi addu'a kafin ka kwanta bacci?
  girgiza mata kai yayi alamar a'a
"Ni nasani ae,tun lokacin baya nake fama dakai akan yin addu'ar bacci before ka kwanta,amma kaƙi jin maganata,"
  Muryarshi tamkar zai yi kuka yace"Aunty azmee,wlh inaso nima na dinga yin addu'ar,amma bansan meyasa ba,karatu baya zama cikin brain ɗina,bazan 6oye maki ba,ban iya komai ba,ko a karatun sallah iya surori biyarne akaina dasu nake yin sallah,amma bayansu wlh ban iya wani abu ba,komai na karanta bai zama acikin kaina,"
  Tsananin tausayinshi ne ya kama azmee,har cikin ranta ta damu da halin da junaid yake ciki,tana jinshi tamkar ɗan cikinta,
   "Junaid ita addu'a,zaka iyayinta da ko wani irin Yare,Allah yana ji kuma zai amsa maka ne,Inaso ka dage da yin addu'a,nima kuma zan tayaka in sha Allah,"
  Ba ƙaramin daɗin maganarta yaji ba,
"In sha Allah Aunty Azmee zan dage da addu'a,nagode sosai da irin kulawar da kike bani,"
  Murmushi azmee ta saki tare da cewa"kada ka manta fa,nifa na shayar dakai,Na so ka sosai junaid,tun lokacin da kana jinjirinka,ban mantawa Abban ku ya ke kawomin kai,
yini kake a wurina,lokacin yayyanka na zuwa aiki wasu kuma ba su kammala secondary ba,mu kaɗai muke kasancewa acikin gidan,Inyi maka wanka,in shafe maka jikinka da mai in gyara maka sumar kan ka,sannan in canza maka kaya,idan na kammala yi maka wannan,sai in shayar da kai,har bacci ya ɗauke mu saman gado,Kasan me"?
  Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"a'a sai kin faɗa,"
  Taci gaba da cewa"idan na farka naga babu kai a kusa dani kamar in zauce...."
  "Saboda me"?Yayi tambayar da ɗan mamaki a fuskarshi,
   "Saboda na tsani araba ni dakai,Su fawan da zarar sun dawo daga school,har ɗakina suke zuwa su ɗauke ka,"
  Fashewa yayi da dariya sosai har dimples ɗinshi suka lotsa,Bayan ya tsagaita da yin dariyar yace"Ni bansan meyasa kowa ke sona ba,Ina da farin jini sosai,ko yau muka haɗu da mutun cikin ƴan mintina sai ki ji yace ina burgeshi,"yayi maganar with proud,
  Murmushi Azmee ta saki,kafin tace"Because of ur Glamorous personality,kana da kyakkyawar zuciya,shiyasa ka ke sace zuciyar mutane cikin ƙankanin lokaci,"
..cike da zolaya yace"Shiyasa jahad ta zauce akan sona,"yayi maganar yana dafe saitin heart dinshi,
  Dariya azmee tayi tare da miƙewa tsaye tana cewa"Ga breakfast can yana jiran ka a dining,Jahad ba ta nan balle ta kawo maka a ɗakinka
  Dafe saitin zuciyarshi ya kuma yi hankali a ɗan tashe yace"Aunty Azmee kina nufin cewa,Juliet dina bata nan?yanzu saida Uncle Abusufyan ya tafin mu da ita ko"?a shagwa6e ya ƙarasa maganar yana ɗan bubbuga ƙafarshi,har cikin ranshi baiso tafiyar jahad ba,Yaci burin su fita shan ice cream yau,
  Fucewa Azmee tayi daga cikin ɗaƙin tana dariya,
  Saukowa yayi daga saman gadon jiki asanyaye ya wuce cikin toilet,

*Boss Bature*

  ❤🤍❤

*Marshal Omar*

Fitowar shi kenan daga cikin toilet,Waist dinshi ɗaure da towel hannunshi kuma na ruke da wani short yana goge ruwan dake ɗiɗɗigowa daga jikinshi,
  "Ya Omar"muryar hosana yaji acikin kunnanshi,da sauri ya juya don yaga ko itace,Kwance ya sameta saman gadonshi ko kayan baccinta bata cire ba,
  Cike da mamaki yace"Kee!me kike yi acikin bedroom ɗina"?
   "Ya Omar nifa zuwa nayi kawai don na gaishe ka"tayi maganar a ɗan shagawa6e,
   "Haka ya dace kizo gaishe dani?ko sallama babu,kawai sai dai na fito daga toilet na same ki a kwance saman gadona,"Yayi maganar fuskarshi aɗan daure,
  Murguɗa mashi baki tayi tare da cewa"Ae ɗakin Mijina ne"
  Harara ya watsa mata"waye mijin naki?Allah ya kiyaye in auri mai ɗan kai irin naki,"
  Gwalo tayi mashi tare da cewa"Oho dai,a haka ka gani kuma kake so,"_
  ƙiris ya rage ya fashe da dariya,amma sai yayi saurin kawar da dariyar don kada taga kamar ma wasa yake yi mata,
   "Get out from my bedroom!"a ɗan tsawace yayi maganar tare da nuna mata hanyar fita daga bedroom ɗin,
  Maƙe mashi kafaɗa tayi,"Wlh ba inda zani ya Omar,Kazo ka ɗauke ni,ka fitar dani idan ba ka son gani na,"
  girgiza kai kawai yayi tare da ƙarasawa gaban mirror dinshi,
   "Kaya fa zansa,pls ki fita daga waje idan na kammala saiki dawo,kin ji My baby"
   "Ae wlh ba inda zani je,Ae ba wani abu bane don ka sanya kaya agabana,tunda aure zamuyi,"
  Shiru yayi bai kara tanka mata ba,
Jin yayi banza da ita yasa ta kuma cewa"Ya Omar"shiru yaƙi amsa mata kiran nata,
  Ci gaba da magana tayi"Wai ya Omar,idan munyi aure,to taya zamu haihu muma"?
  Banza yayi bai tanka mata ba,
Bata damu da hakan ba,sai ma ci gaba da maganar tayi,
  "Ya Omar,kana ganin nima zan iya haihuwa?Kuma ma Taya za'ae na samu cikin"?
  Hauka maganinka Allah,ya furta hakan acikin Zuciyarshi,
   "Ji ya Omar ina magana ka wani share ni,idan baka faɗamun ba,to taya zan sani,"?
  Ƙin tanka mata yayi,a hasale tace"Shikenan tunda ba zaka bani Amsa ba,wlh idan Daddy ya dawo zanje in tambayeshi ne,don ni bazan bari ayi abun kunya ba,Ayi mun aure bansan komai ba,
  A ƙule ya juyo tare da kallonta yace"Ke,Tashi ki fuce mun daga ɗaki"
  Maƙe mashi kafaɗa ta kuma yi"anƙi a fita Ya omar,"
  Abun ya ɗaure mashi kai,ita ko shakkarshi bata ji,neman ma abunda zata yi mashi ya bugeta take yi don tasan cewa bazai iya ta6a lafiyar jikinta ba,
  "Idan kanaso in fita cikin lalama,to ka fara faɗamun taya zan samu ciki idan munyi aure"
  "Shine abunda kikeson sani"?yayi tambayar yana kallonta hadi da dage mata gira,ɗaga mashi kai tayi alamar eh,
Aikuwa Nan take ya sanya hannunshi ya zame towel ɗin daya ɗaure qugunshi dashi,
  Tashin hankali! A gigice Hosana ta fasa wata irin razananniyar ƙara,Kafin kace me kamar walkiya haka tabar ɗakin da gudu tana kuka,ta firgita sosai
  Mayar da towel ɗin yayi ya ɗaure waist ɗin sosai,sai faman tiƙar dariya yake yi,har da dafe cikinshi,
  "Maganinki kenan,nasan daga yau ba zaki sake yi mun irin wannan question ɗin ba,Yarinya sai kace mai iskokai,Ni bansan ya zan ƙare da ita ba,A haka dai nakeso,kuma zan kula da abuna"ya ƙarasa zancen zucin fuskarshi ɗauke da murmushi ya wuce wurin wardrobe ɗinshi,sai daga baya ya dinga tunanin kada hosana fa taje ta faɗa ma wani abunda ta gani tunda ba hankali gareta ba,Tuna wannan yasa yayi saurin ɗauko jallabiya ya zura ajikinshi,da sauri ya sauko downstairs yana nemanta,

Azmee ya hango tana jera kayan abinci asaman Dining na breakfast dinsu,da sauri ya tunkareta,tunkan ya ƙarasa wurinta tajiyo takun takalmin mutun,ɗagowa tayi tare da kallonshi,ganin Marshal yasa ta saki fuska tare da gaisar dashi,
   "Barka da safiya Omar,an tashi lafiya,"
A gaggauce ya amsa mata"lafiya lou,amman pls ko kinga gifcin Hosana,"?
  "kamar dai naso naga giftawarta,lokacin ina ƙoƙarin fitowa daga kitchen,kuma naji kamar shessheƙar kuka ta ke,"
  "Ina kike tunanin ta shiga ne,"
Shiru Azmee ta ɗan yi tana tunanin wurin da taga hosana ta nufa,
  "Yawwa,ina tunanin bedroom ɗinsu ta nufa,"
  Tunkan ta ƙarasa maganar ya kama hanya da sauri da sauri ya nufi ɗakinsu,a buɗe ƙopar take hannu yasa ya turata,tunkan ya shiga ciki,Ya jiyo shessheƙar kukan Hosana,Yana yin sallama taji muryarshi da gudun gaske ta sauko saman gadonsu ta faɗa toilet ta datse ƙopar,tana ci gaba da yin kukan,
..Sehrish na kwance saman gadon,ta ƙudundune cikin bargo,tun da Asuba da ta farka asaman gadon Sgr lokacin ya shiga toilet domin yin alwala,ta saɗaɗa tabar bedroom ɗin nashi,ta dawo ɗakinsu,

Kaitsaye ya wuce ƙopar toilet ɗin ya tsaya tare da ambaton sunanta"Am really sorry Hosana,nasan ban kyauta maki ba,ke ce kin takuramin that's why nayi maki hakan,kuma ni fa amsar tambayarki kawai na baki ba wani abu ba,
  Cikin shessheƙar kuka yaji tace"Ya Omar baka da kunya wlh,Ni babu ruwana dakai,Wlh bansan ganinka,bansan ganin wannan abun naka"
Hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,
  A ruɗe ya shiga faɗin"hosana!baki da hankaline?so kike ki tona mun asiri,har wani ya ji mu?kin manta ni zan aureki,"?
   A tsiwace tace"wlh saina faɗama daddy idan ya dawo,ince ka nuna mun abunka,"
  Hannu yasa tare da dafe kanshi,ya furta"Wayyo Allah na,Ni Omar,naja ma kaina,"
  Ƙasa ƙasa yayi da muryarshi cikin lallashi ya soma magana,
   "My Hosana pls,ki yafe mun,bazan ƙara ba wllh,kome kikeso zanyi maki,"
   "Wlh ya Omar,ko kukan jini zaka yi saina faɗama daddy cewa kai ɗan iska ne,Ni bazan aure ka ba,"
  Tsawa ya daka mata tare da cewa"Ki faɗima duk wanda zaki faɗimawa ƴar rainin hankali,Wlh kuma kika kuskura kika faɗama wani sai na sa6a maki,kuma babu ni babu ke,Ƙasar ma zan bari gaba ɗaya in tafi can in auri baturiya,". 
  Rai a6ace ya juya tare da barin ɗakin nasu,
  Sai da taji alamun fitarshi daga ɗakin,sannan ta wanko fuskarta ta,ta buɗe ƙopar toilet ɗin ta fito waje,abun ya dameta sosai buɗe ƙopar ɗakin tayi ta fuce,A dining ta same shi zaune shi da junaid suna yin breakfast,Azmee na yin serving ɗinsu,
  Kamar wadda aka zarewa lakar jikinta haka ta ƙarasa ta samu wuri kusa dashi ta zauna,
    "Aunty Azmee ina kwana"?fuskar Azmee ɗauke da murmushi ta amsa mata,"Lafiya lou Jahad,kin tashi lafiya...."da sauri junaid yace"Aunty azmee wannan ce jahad?kalli fa ƴan kumatun fuskarta ki gani,Hosana ce,"
  Dariya azmee tayi,shi kanshi Omar yaso ya ɗan dara,ita kuwa tsuke fuska tayi tare da jifarshi da harara tace"ina ruwanka da kumatuna"?
   murguɗa mata baki junaid yayi dama basu jituwa atsakaninsu,Ƴar tsama sukeyi,
    juyawa ta ɗan yi gefenta tare da kallon Marshal,Ya tamke fuskar nan babu annuri acikinta,
   Saitin kunnanshi takai bakinta cikin sanyin murya tace"Ya Omar bazan ƙara ba,kuma bazan tona maka asiri ba,dan Allah kada ka tafi ka barni,"
  side smile yayi tare da cewa"Its okey,nima wasa nake yi maki,bazan iya tafiya nabarki ba,"
  Murmushi ta saki,har hankalinta ya kwanta,
    Hannu Azmee takai zata ɗauki plate ta zuba mata abinci,ganin ta zura hannunta acikin plate ɗin Omar suna ci atare yasa ta fasa,Abun ba ƙaramin burgeta yayi ba,

*KANO TA DABO TUMBIN GIWA KODA ME KAZO AN FI KA* acewarsu ba,Don ni ban yarda ba,
💋Boss Bature💋*



Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*

*Father of soldiers*

*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



Na biya bashi😏

Masu buƙatar littafin Suyi mun magana direct ta layina amma fa message ta whatsapp kawai,Ko an kira ba'za a samu ba, 08103884440

❤🤍❤

Tun wuraren ƙarfe Goma,Motarsu Abusufyan tayi dirar mikiya acikin jahar Kano,Da kanshi yake yin driving ɗinsu,Jahad na manne a kafaɗarshi tana sharar baccin da bata ƙarasa ba a gida,
  Tunda suka shigo cikin garin murmushi ya wanzu akan fuskarshi,Bakomai yake tunawa ba fa ce irin rayuwar da yayi acikin garin tun lokacin ƙuruciyarshi,
   "Jahad!ki tashi mun ƙaraso fa,"cike da farin ciki yayi maganar,
Sai da ya ambaci sunanta kusan sau 5 kafin ta amsa mashi,tare da miƙewa daga zaune tana yin hamma,ta cikin face mask ɗin dake a fuskarta,
  Buɗe idanuwanta tayi tare da juyawa tana ƙarewa garin kallo ta cikin glass ɗin Motar,hakanan ta dinga jin faɗuwar gaba rass!rasss!lokaci guda kuma tashiga tariyo abunda ya faru acikin rayuwarsu azamansu garin,

NASARAWA G.R.A

Shine Sunan Unguwar da hajiya Ameenatu Wato Gwaggon katsina tayi rayuwa acikinta tare da ahalinta,a hankali motarsu ta shigo cikin unguwar da matsakaicin gudu,A dai dai jerin wasu manyan gidaje na masu hali,Abusufyan ya tsayar da Motar a bakin gate,
   "Daddy wannan gidan wanene'?tayi tambayar tana kallon fuskarshi,
murmushi ya ɗan yi tare da cewa"Wannan gidan da kike gani acikinsa nayi rayuwa tare da mahaifiyarku,Kuma anan kakan ku Marigayi baba buzu yayi gadi,Allah ya jiƙanshi da rahama,
  Amsa mashi tayi da Ameen,kafin suka fito daga cikin motar,
  "Allah sarki,Kullum idan nadawo a wancan lokacin,Baba buzu nake samu zaune saman benci yana dafa ruwan bununsa,da zarar ya hango motata zai fara yi mun kirari,Ya buɗe mun gate don in shiga daga ciki," acewar Abusufyan,
Jefi jefi mutane ke giftawa acikin unguwar,tun bayan da suka bar kano a lokacin baya,Mijin Gwaggon katsina ne ke zama a cikin gida kafin Allah yayi mashi rasuwa,Tun daga lokacin kuma babu wanda ya ƙara zaman gidan,ko Dr harris idan yazo kano ya kwammace ya kama hotel ya zauna acikinsa,
   Hannu ya zura acikin aljihunshi ya curo key ɗin gidan,Ya ƙarasa tare da zura key ɗin ajikin ƙopar dake manne da gate ɗin gidan,Wurin har ya fara tsatsa,ya ciccije daƙyar ya samu ya buɗe ƙopar,
  Ya ruƙo hannunta suka shiga daga ciki,
   Zuba ma gidan ido tayi tana kallonshi,A ranta tana ayyana irin rayuwar da mahaifiyarsu tayi acikin gidan,Ya haɗu duk da ginin Ya tsufa sosai,akwai fili sosai,Ga wurin buga ball nasu Abusufyan,Ga moto park,da sauransu,
Kaitsaye suka nufi Ƙopar da zata sadaka da Babban falon gidan,ita kuwa ta zuba ido tana ƙarewa gidan kallo,Uwar yanace ta ko'ina yayi datti,ga tarin ƙura musamman ajikin glass ɗin windows dana doors,
  Buɗe masu ƙopar yayi da key ɗin hannunshi,Yayi gaba tabi bayanshi,Kamar mai jin tsoro haka ta zura ƙafarta ciki,Matsakaicin falo ne,Yadda kasan bola,ledoji,yayi da sauran tarkace a kasanshi,Tiles ɗin kuwa duk yayi dirty kura ta rufe shi,Sofas ɗin dake a ɗakin duk sun gajarce sunyi ƙanƙanta,yadin jikinsu yayi diƙiƙi,
  "Daddy,ina ɗakin da Oumman mu tayi rayuwa acikinshi?ka nuna mun inaso naga ɗakin,"
  Da yatsan hannunshi ya nuna mata bedroom ɗin da abu tayi rayuwa,da sauri ta nufi ɗakin,shima yabi bayanta,A datse ƙopar ɗakin take amma babu key ajikinta,da ƙarfi yasa hannu ya turata,ji kake ƙiiiiiiii,ta buɗe a slow,
  Faɗawa cikin ɗakin tayi tana bin kayan cikinshi da kallo,labulayen duk sunyi ƙura,sun nannaɗe sun cukuikuye,Carpet ɗin bakin kofar ya fita hayyacinshi,Single bed ne acikin ɗakin,sai wardrobe ta bango,itama duk tayi ƙura,book shelve,Da dressing mirror da sauran tarkace,komai yafita hayyacinshi,
   Qur'ani ta hango saman bedside drawer ɗin gadon,
  Tun kafin tayi magana Abusufyan yace"Wancen qur'anin da kike gani na mahaifiyarku Ne,mace ce mai son addini tana ƙoƙari sosai,bata wasa da ibada,da haka ta sace mun zuciyata,"
  Hawaye ne suka soma sintiri akan fuskarta,ƙarasawa tayi gaban drawer ɗin ta sanya hannu tare da shafa al'qur'anin,ta kakka6e ƙurar dake akanshi,ɗago dashi tayi a hankali ta manna mashi kiss,
   "Daddy inason qur'anin nan sosai,zamu tafi dashi,"ta ƙarasa maganar tare da buɗe handbag ɗin dake hannunta,ta zura shi ciki,"
  School bags ta hango guda biyu,Anyi hanging ɗinsu a saman bango inda aka bubbuga ƙusa,
  Da sauri ta ƙarasa tare da kai hannu ta curo jakunkunan,ta sauko dasu ƙasa,ta zuƙunna tare da buɗe jakar,Littattafan addini ne cikinsu,Ahlari ne,Tajweed,Fiqhu,da sauransu,ɗayar jakar kuma da ta buɗe Littattafanta ne na boko da take zuwa school dasu,komai nata mai tsari,
  Abusufyan kuwa wurin wardrobe ɗin kayanta ya wuce,buɗewa yayi yana kallon jerin wasu daga cikin kayanta,Uniform ɗin islamiyyarta ya ɗauko,tare da rungumesu a ƙirjinshi,Sae lokacin hawaye suka shiga zarya akan fuskarshi,
   Bazai ta6a mantawa ba,da rana ta farko daya fara sanyata acikin idanuwanshi,a lokacin tana kan hanyar dawowarta daga school,
   "Jahad,"ya ambaci sunan ta tare da juyawa yana kallonta
  "Na'am Abba,tayi maganar tare da miƙewa ta ƙarasa gabanshi,
   "Kin ga waɗannan kayan,dasu ne na fara ganin Oummanku,Uniform ɗinta ne na islamiyya,"
  Murmushi ta saki tare da sanya hannu ta kar6i kayan,Rungumesu tayi ajikinta,Sae ta dinga jin tamkar Oumman tasu ta rungume,
  6ata lokaci sukayi sosai suna bincike acikin ɗakin Zainabu abu,
Daga bisani ne Yunwa ta fara kamasu gashi gidan babu abinci,Yanke shawarar zuwa nemo masu abincin yayi,ya barta acikin gidan,Gyara masu ɗakin oummansu ta shiga yi,Taci baƙar wahala sosai,Bayan ta share ɗakin har wanke shi tayi,A kitchen ta samu bokiti da ledar detergent,ga ruwa available,sosai ta wanke ɗakin sai ga tiles ɗin yayi haske sosai,Cire zanin gadon tayi ta ɗauko wani acikin wadrobe,Ta shimfiɗa masu bayan ta kakka6e gadon,ta goge jikinshi,

Hatta glass door din sai da tabi tayi scrubbing ɗinsu,ta goge yanar ɗakin,lokaci guda kamanin ɗakin suka canza,Komai na son gyara,Toilet ta shiga nan ma tataras dashi duk sai a hankali,sae da ta fara gyarashi fess,Sannan ta samu ta ɗan watso ruwa tare da ɗauro alwala,
  Darduma ta dauko cikin wadrobe ta shimfiɗata,ta kabbara sallar azhar,A tsanake tayi sallar tana kammalawa,agalabaice bacci ya ɗauketa saman dardumar,

Wuraren ƙarfe 2:30 Abusufyan ya shigo cikin gidan hannunshi ɗauke da Ledojin da yayi masu

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login