Showing 363001 words to 366000 words out of 432432 words

Chapter 122 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete

da ɗaukarsu hotuna da wayarta,kafin suka wuce tare da barin palourn,komawa hosana tayi saman sofa ɗin tana jiran dawowar Ya Omar,

Wurin motarshi suka nufa,da kanshi ya buɗewa jahad mota,ta shiga,kafin ya zagaya other side ɗin,ya buɗe ma kanshi motar ya shiga,
juyawa ta ɗan yi tare da kallon fuskarshi,Murmushi ta samu akan fuskarshi,
  Cikin sanyin murya tace"Babyna,"
  "Na'am" ya amsa mata tare da wurga idanuwanshi akanta,
  Kashe mashi ido ɗaya tayi kafin tace"Junaid,I love u so much,I can sacrifice my life for u,"
  Ƙayataccen murmushi ya saki,tare da cewa"Me too,",yana ƙoƙarin tashin motar yaji gabanshi yayi wani irin mugun bugu mai sautin gaske ji kake daraaam!har razana sai da yayi,lokaci guda yanayin fuskarshi ya canza,ganin ya kasa tashin motar yasa jahad,cewa"Babyna,Lafiya naga yanayinka ya canza"?
  Ashagwa6e yace"jahad,faduwar gaba nake ji,kamar wani mummunan abu zai faru dani,haka nake ji,"muryarshi a kasalance yayi maganar,
  Cikin sanyin murya tace"In sha Allah babu abunda zai faru da kai babyna,idan har fitar nan da zamuyi bata kwanta maka arai ba,ni inaga kawai mu koma gida..."tunkan ta ƙarasa maganar,yace"a'a,Bazamu fasa ba,na sa rai sosai akan fitar nan,"
  Jinjina kai jahad ta ɗan yi tare da zura hannu cikin ƴar purse ɗinta dake ajiye saman laps ɗinta,Phone ɗinta ta curo tare da buɗeta,adai adai lokacin app ɗin da take amfani dashi na V muslim wurin yin azkhar yayi mata alert na cewa time ɗin yin evening azkhar yayi,
  Juyawa ta ɗanyi tare da kallon junaid,wanda jikinshi duk yayi sanyi,
  "Babyna,yakamata muyi azhkar kafin mu fita daga gidan nan,"
   Ashagwa6e yace"jahad ni ban iyaba,bansan ya zanyi ba,"
  Moving tayi close to him tare da nuna mashi screen ɗin wayarta"kalli ka gani,App ne nake using dashi yana da matuƙar amfani,kuma yana taimaka mun wurin tunasar dani lokuttan yin sallah da kuma yin azhkar,koda ace baka iya ba,zaka iya yi yayin da kake kallo kana karantawa acikin zuciyarka,"
Murmushi ya ɗan saki kafin yace"Its ok my juliet,mu fara atare,"
  Nan suka shiga yin azkhar ɗin acikin zuciyarsu,har suka kammala,tukunna
yaja motar da gudu ya nufi hanyar fita daga gate ɗin gidan,a bakin gate ɗin ma sai da jahad ta ƙara tunasar dashi akan yin addu'ar fita daga gida kuma atare suka furta"Bismillah,Tawakkaltu Alallah,wala haula wala ƙuwwata illa billah",

Fitar motarsu keda wuya,Sai ga motarsu Marshal Omar na shigowa cikin gidan,Hatta gifcinsu sai da marshal Omar ya gani,
  "Yalla6ai,kamar motar junaid ce ta wuce yanzun nan"major ne yayi maganar,
Omar dake zaune a back seat na motar yace"I think so,"
  "Amma yalla6ai,kada kace nayi shisshigi,ni dai aganina bai kamata junaid na fita yawo shi kaɗai ba without security guards atare dashi,duk da munsan Allah ke tsare bayinsa,"
shiru Marshal ya ɗan yi yana nazarin wani abu kafin yace"Ni kaina na jima ina tunanin hakan,last time har maganar mu kayi da Rafayet,amma daga baya kowa ya share maganar,"
Major yace"gaskiya yakamata aduba,saboda yaron yana da farin jini sosai,kuma kowa yasan irin son da kuke yi mashi,duk wani mai hakon family ɗinku zai iya biyowa ta wurinshi ne"_
Jin wannan maganar ta Major,yasa hankalin Omar ya tashi,saboda an sha faɗa masu cewa junaid,Shi ne lagwansu,Duk wani wanda zai kawo masu hari acikin masu son ganin bayansu,dole sai an ƙuntatawa junaid sannan za'a ta6a zuciyoyinsu,

  "Major thank u so much for ur advise,and in sha Allah zanyi wani abu akai,'

Bayan Major yayi parking ɗin motar,Ya buɗe ya fito tare da zagayawa ya buɗewa Marshal,Saukowa marshal yayi,ya nufi cikin gidan,lokacin da ya shiga babu kowa a main palour ɗin,Bedroom ɗinshi ya wuce,Shaf shaf ya cire kakin dake ajikinshi,Ya wuce cikin toilet,after some minutes ya fito daga cikin toilet ɗin,sanye da short a jikinshi,Agajiye yake ga wani irin bacci da yake ji,Saman gadonshi ya haye,in a short time bacci ya ɗauke shi,

A hankali Hosana ta turo ƙopar dakin nashi,tun tana kabbara sallar la'asar ta jiyo shigowar mota cikin gidan,jiki na rawa ta sallame bayan ta gama sallar ta fito,saboda tana da tabbacin cewar Ya Omar ɗinta ne ya dawo,murmushi ta saki ganinshi kwance da gajeran wando ajikinshi,ya baje sai faman sharar bacci yake yi,lalla6awa tayi cikin sanɗa ta haye saman gadon,saman jikinshi ta hau,har zuwa saitin fuskarshi,ta ƙura mashi ido tana kallon kyakkyawar fuskarshi,bata da da burin da ya wuce ta takura mashi arayuwarta,
   "Bari nagani,idan na toshe mashi hancinshi da bakinshi,ta ina zai yi numfashin,"
  Hannu tasa,cike da mugunta,ta toshe mashi hancinshi da bakinshi,ta danne su da tafin hannunta,aikuwa nan take numfashinshi ya soma tattokarewa,A razane ya farka lokaci guda,ya rarumeta batare da ya ankara ba,yayi wurgi da ita,da iya ƙarfinshi na ƙarshe,kai tsaye hosana ta faɗi ƙasan gadon yaraf!kanta ya bugu sosai,fashewa tayi da matsanancin kuka tana fadin"Wayyo Allah na,Ya Omar ka kashe ni wllh,"
  Tunda yaji muryarta,ranshi ya 6aci sosai,saboda ita taja har yayi mata hakan,ko kwanakin baya ta ta6a yi mashi irin hakan har yayi wurgi da ita,miƙewa yayi daga zaune tare da kai idanuwanshi wurin da take yashe a ƙasa tana kuka,
  Da wata irin kasalalliyar murya yace"Why Hosana!why!"?
   Sai faman shessheƙar kuka take yi,tama gaza ɗagowa da kanta,
  Guntun tsoki yaja,kafin ya sauko saman floor ɗin,hannu yasa ya janyota jikinshi ya rungumeta a saman faffaɗan ƙirjinshi,yana ɗan bubbuga bayanta,Cikin lallashi yace"Am so sorry My Hosana,duk laifinki ne,meyasa kike son takuramin ne?
  Cikin shesshekar tace"ya..ya..Omar,nifa wasa nake yi maka fa..."
  "Haka ake yin wasa a garinku?You are trying to kill me,and u are saying that it was a joke!"
   "Ya Omar,nima fa a wani Chinese film ne nagani,Na jakican,shi ne na kwaikwaya,"
  A ruɗe ya ɗago da kanta daga saman ƙirjinshi yace"Ke!ashe dagaske baki da hankali,saboda kawai kin kalli film kinga anyi haka sai kice nima zaki jaraba akaina?angaya maki cewa abunda ke cikin film dagaske ne?Su idan sunyi sun rayu,to ni idan kika yi mun kashe ni zakiyi,"
  Runtse idanuwanta tayi ganin yadda yake ta surfa mata faɗa,
  Tsagaitawa tayi da yin kukan da take yi"Am sorry Ya Omar bazan ƙara ba,"
  Harara ya ɗan watsa mata"kinfi kowa iya bada haƙuri,idan kikayi laifi kamar matar aure ta gari,"
  Murguɗa mashi baki tayi,lokaci guda ya samu kanshi cikin wani irin yanayi,zuba mata ido yayi yana kallon dress ɗin dake ajikinta,Jeans da t shirt sunyi matuƙar bin shape ɗin jikinta,jin yayi tsit yasa ta ɗan buɗe idanuwanta,ganin ya zuba mata ido ko ƙyaftawa baiyi ba,yasata fara tunanin kome yake kallo ajikinta,Ganin yana kallon ƙirjinta yasa tace"Ya Omar sun ƙara girma ko"?
Waro ido ya ɗan yi tare da cewa"Mekenan?"
Hannu tasa tana nuna mashi breasts ɗinta,
  "Ya salam,"ya furta hakan tare da ɗan rufe idanuwanshi yace"nifa,basu nake kallo ba,kayan jikinki ne suka burgeni,sunyi maki kyau sosai,"ya ƙarasa maganar tare da miƙewa tsaye yana kallonta,
   "Idan kana jin yunwa in kawo maka abinci"?tayi tambayar tana kallonshi,
   ɗaga mata kai yayi alamar eh,sannan yace"pls,inaso in ɗan kwanta in huta kinga baccin bai ishe ni ba,idan kika kawo mun Lunch ɗin,ki ajiyemun shi saina farka zanci,"
  Amsa mashi tayi da toh,kafin ta miƙe da sauri da sauri ta fuce daga ɗakin,saman gadon ya koma ya kwanta,bakomai bane ya faɗo mashi aranshi ba,fa ce maganar da suka yi da Major dangane da Junaid,hakanan ya dinga jin kamar yayi kuskuren barinshi ya wuce da motarshi,dama ya sani tun a time ɗin yasa security sun bi Bayan Motarshi...........


*Boss Bature*

Ƙarar shigowar Message,da ta ji ne yasa takai hannu tare da ɗaukar wayarta dake ajiye agaban mirror,yayin da take zaune asaman kujerar gabanshi,tana yin makeup,janyo wayar tayi tana karanta message ɗin daya bayyana akan screen ɗin wayar,
   _Abra,inason magana dake,amma bana so kowa ya sani,koda Aunty Laila ce_
  Mamaki ne ya kamata ganin anyi mata saƙo da new number,kowaye wannan,ɗaukar wayar tayi tare da miƙewa tsaye,a lokacin Aunty babba na cikin toilet tana yin wanka,

Arab gown ce ajikinta,pink colour abunka ga fara tass,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,fitowa tayi daga cikin bedroom ɗin nasu,ta miƙi hanya kamar zata fita daga corridor ɗin,Sai da ta bada tazara sosai,Sannan ta dannama numbar kira,tana fara ringing aka ɗaga,
  Tun kafin tayi sallama,taji muryar hayaam tace"ABRAH"!tun daga kan yadda ta kira sunanta yasa gabanta ya faɗi rass,
   "Aunty hayaam kece"?
Bata amsa mata ba,sae ma fashewa da tayi da kuka mai sautin gaske,hakan ya ƙara ɗagawa Abra hankali,a ruɗe ta shiga faɗin"Aunty hayaam meya faru dake ne?meyasa kike kuka?dan Allah kiyi mun bayani,"

On the other hand,Hayaam ta miƙa ma Amani wayar tare da cewa"kiyi mata bayani,"
  Gyaran murya Amani tayi tare da ambaton sunan Abra,
  Duk sunbi sun ɗaga mata hankali,muryarta har kerma takeyi wurin cewa"Dan Allah kuyi mun bayani,kun sanyani acikin duhu,"
  "Abrah!ki natsu ki saurareni,"jinjina kai abra ta shiga yi tana fadin"ina sauraranki Aunty Amani,meya faru ne naji Aunty hayaam tana kuka,
  Amani bata 6oye mata komai ba,game da abunda ya faru da hayaam da kuma guduwar Aunty babba daga asibitin,da kuma wasikar da ta bar mata,wasu irin zafafan hawaye ne suka soma gangarowa akan fuskar Abra,hankalinta a matuƙar tashe tace"Nashiga uku!kenan nima wata rana idan ƙaddara ta same ni,Aunty laila zata iya guduwa ta barni?
  Amani tace"ƙwarai kuwa!saboda bata da Imani kuma bata da tausayi,karki so kiga yadda na samu hayaam a asibitin nan a wulakance,kamar wadda tayi hatsarin mota amma a haka laila tabarta,saboda bata da amfanin da zata yi mata,To kema muddin kika kuskura kika bita wurin bokan nan rayuwarki ta faɗa halaka,Kuma wlh da zarar amfaninki ya ƙare a wurinta shikenan kin zama Waste product!Zata yi watsi dake ne,"jin wannan maganar yasa Abra ta fashe da matsanancin kuka,wani irin tsoro ne ya kamata,don Aunty babba ta zama abun tsoro a wurinta,ta girgiza da jin rashin imaninta,
Da gangan Amani ta dinga tunzura abra don ta tsoratar da ita akan karta goyi bayan Aunty babba suje wurin bokannan,
  "Abra!ina ƙara jan kunnanki,karki kuskura ki bi ta,Kiji tsoron Allah,ki tuna cewa wata rana zaki koma gare shi,kada kiyi silar da za'a cutar da rayuwar wasu,Aunty laila bata da Imani,tanaso ta jefa rayuwarku cikin haɗari ne,kuma tana yin amfani da ku ne don ta cimma burinta,kuma da zarar amfanin ku ya ƙare a wurinta,zata yi watsi daku ne,ta kama gabanta,Ga hayaam nan dai yanzu ta gane kuskuren da tayi,tana mai dana sanin abunda ta aikata,"
  Amani nakai ƙarshen maganarta,ta miƙa ma hayaam wayan"kiyi mata magana,"
  Kar6ar wayar hayaam tayi tare da karata a kunnanta,Kukan da Abra keyi har cikin zuciyarta,dama tasan dole taji raɗaɗin acikin zuciyarta,ɗan uwa ba wasa ba,
  Cikin Sanyin murya tace"Abra,baki ga yadda na koma ba,bani da wani abu daya rage na ƴa mace a jikina,komai ya lalace,Yanzu ma bana jin kaina amatsayin mace,"
  Wani sabon kukan Abra ta ƙara fashewa dashi,cikin shessheƙa tace"Aunty hayaam wlh bazan bi ta ba,sai dai taje ita kaɗai,Ashe ba son mu take yi ba,bata ɗauke mu abakin komai ba,Amfani kawai take yi damu don ta cimma burinta,Ni wlh bansani ba Aunty hayaam,harfa tambayarta nayi ina kike amma tace mun wai batasan inda kika tafi ba,kinacan kina yawon gantali,Ashe kina gadon asibiti rai hannun Allah,yanzu haka fa da nake yin maganar nan,tun jiya muka iso Enugu da ita,Yanzu haka ma shirin zuwa wurin bokan muke yi,
  Hayaam tace"Abra,ki natsu ki saurare ni,kada ki bari tasan da shirinki naƙin binta wurin boka,saboda bata da imani tana iya kasheki,in kika 6ata mata rai,Abunda nake so dake shi ne,Duk wani kuɗi dake a wurinta,ki tattarasu gaba ɗaya ki sanyo su acikin jakarki,muguwar rabi da kwata na kuɗin dake a hannunta nawa ne,amma saboda tsabar rashin Imani ta kwashe hada nawa ta gudu dasu,"
  Jinjina kai Abra tayi yayin da take share hawayenta,
  "Aunty hayaam,yanzu tana acikin toilet,bari nayi sauri na tattara kayana,in biyo mota in dawo nan,"
  Hayaam tace"Yawwa,kiyi sauri kada fa kiyi kuskuren da zai sa ta gane cewa guduwa zakiyi ki barta,". 
  "In sha Allah bazan bari ba,"
.daga haka su kayi sallama,

Ajiyar zuciya hayaam ta sauke tare da kallon Amani dake zaune gefen gadon,tace"Har hankalina ya kwanta,So nake Aunty laila ta ɗanɗani kuɗarta,taji irin raɗaɗin dana ji acikin zuciyata,
  Murmushi Amani tasaki,tare da cewa"Nafi ki jin daɗi Hayaam,A shirye nake dana taimaka muku wurin ganin kun gyara rayuwarku,"acikin ranta kuma tace"Ita kuma waccen bijimar,Sai nasa ta tsani kanta,duk wani makusancinta saina kwace shi ya dawo a ƙarkashin ikona,So nake ta gane kuskuran da ta aikata arayuwarta,"

A 6angaren abra kuwa,tun bayan da suka kammala yin wayar,jiki na rawa ta koma Room ɗin nasu,A hankali ta tura ƙopar ta fara leƙawa ciki,don taga ko ta fito daga wankan,Ajiyar zuciya ta sauke,ganin bata fito ba,da sauri ta faɗa cikin ɗakin,Jikinta sai kerma yake yi,asaman bedside drawer,ta samu jakar Aunty babba,hannu tasa ta ɗauki handbag ɗin,tare da zagayawa ta Other side ɗin ta ɗauko ƴar purse ɗinta,saboda tsabar sauri jin Aunty babba na motsi kamar zata fito daga cikin toilet ɗin,aikuwa a gigice ta buɗe ƙopar ɗakin ta fuce,da gudun gaske,mutanen dake kai komo a cikin hotel ɗin sai kallonta sukaye,wasu kallon burgewa suke yi mata saboda rigar jikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,gashi bata sanya mayafi akanta ba,ƙafafunta ko takalma babu,

Hankalinta bai kwanta ba,har sai da ta fito daga cikin hotel ɗin,gudu gudu sauri sauri ta miƙi hanya tana tafiya tana waiwayon bayanta kada ace Aunty laila ta biyota,Masu motoci sai parking sukeyi agabanta suna yi mata tayin shiga motarsu,amma taƙi sauraron kowa saboda gudun kada wani ya cutar da rayuwarta,kamar yadda aka yiwa Hayaam,baiwar Allah ta tsorata sosai,gashi babu wanda ta sani a garin,haka bata san ko ina ba,ba ƙaramin galabaita tayi ba,

    *Koya Abra zata ƙare?Shin ina Aunty Babba dake a cikin toilet tana wanka?Batasan an yashe ta ba*

*Boss Bature*

   ❤🤍❤

Kano state

Wuraren ƙarfe 6 na marece,Slowly motocin Sgr suka shiga cikin unguwar batare da jiniya ba,saboda patient ɗinsu da suka ɗaukko,a back seat na motar Abusufyan suka kwantar da ita,Abusufyan shi ne ke driving ɗin motar,fuskarnan tashi a washe,kamar wanda aka yima Albishiri da Gidan Aljanna,Sehrish na agefenshi sae faman sakin murmushi take yi tana waiwayawa,bakinta yaƙi rufuwa,a ƙagare take dasu ƙarasa gidan,ko ta samu ta kira sauran ƴan uwa ta sanar dasu cewa An samo Oummansu,

Bayan motar su Abusufyan Motar dake ɗauke da Baban Sadeeq ce,tare da Maman Sadeeq,ɗaya daga cikin motocin Sgr ne,wanda wani soja ke driving ɗinsu,
Mamaki yaƙi barinsu,musamman Maman sadeeq,abun ya ɗaure mata kai har tagaza rufe bakinta,
Kasa kasa tace "Baban Sadeeq kaga wani iko na Ubangiji"?
  Murmushi Baban sadeeq yayi tare da kallonta yace"dama ae naji ma ina sanar dake cewa,Allah yana tare dasu,kuma shi zai kula da abunshi,Yau nasan kin shaida maganata,"
Murmushi ta saki tunawa da wannan kalami na Baban sadeeq,a duk lokacin da ta rufe shi da faɗa kan cewa sunƙi ɗaukar mataki akan Ya sayyadi,yana ta cutar da bayin Allah,an zuba mashi,sai babban sadeeq yace mata"Bazan iya tunkarar mutumin nan ba,Mutumin da kana ja mashi ayar ƙur'ani yana fassara maka?taya zan iya tunkararshi?in dai akan yara ne Allah yana tare dasu,Kuma shi zai kula da abunshi,"
  "Amma gaskiya Baban sadeeq,nayi matuƙar mamaki,har yanzu fa ji nake yi kamar mafarki nakeyi wlh,wai yanzu waɗannan danginsu rishi ne?bayin Allah,wlh na tayasu murna sosai,"
  Baban sadeeq yace"Ni ji nake kamar nafi kowa farin cikin wannan ranar wlh,Alƙawarin dana ɗaukarwa kaina,Ya cika yau ga abu ga Ƴa'ƴanta,ga kuma danginsu,Godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata'ala,"

A bayan motarsu dasu Baban sadeeq suka,Motar dake biye da tasu,nurse ce ɗaya tare da Dr,An zo dasu ne don a nuna masu gidan,Saboda sune zasu ci gaba da zuwa suna duba lafiyarta,security guards sun sanya motocinsu a tsakiya,gaba da baya duk motocin Soldiers ɗinne,Sgr baisamu ya biyo bayansu ba,Sun wuce Hotel shi da Armstrong,

A parking space suka tsayar da motocin nasu,fitowa Abusufyan yayi tare da zagayawa ya buɗe gidan baya,Hannu yasa ya kinkimo abu,tare da azata asaman kafaɗarshi,gaba ɗaya suka kama hanyar shiga cikin falon gidan,tun kafin su shiga ciki sehrish ta fara ganin canji alamun kamar anyi gyara acikin gidan,shi kanshi Abusufyan yayi noticing hakan,

Main palour ɗin suka shiga,Nan fa suka sha mamakin ganin an canza Sofa set ɗin falon izuwa sababbi,Hatta ƙasan falon wani jigunannan carpet ne aka shimfiɗa ya mamaye ko'ina,ga wani irin sanyi na A.c dake ratsa ko'ina cikinshi,Abun ya ɗaure masu kai,
   "Abba kodai munyi mistake ne"?Sehrish ce tayi maganar,
  "Ba kuskure mu kayi ba sehrish,ni kaina nayi mamaki,daga gani aikin Sgr ne,Shi ya sanya aka gyara gidan,dama ina ta fargabar awani wuri zamu aje Oummanku"yayi maganar,a yayin da suke tunkarar Bedroom ɗin abu,ciki ya shiga da ita,nan ma an sanya A.c ɗin,daga gani duka gidan aka gyara,hatta furniture ɗin duk an canzasu,Naira tayi aiki daga safe zuwa maraice gidan ya koma tamkar na amarya,amaryar ma yar masu fada aji,a hankali ya kwantar da ita saman gadon,wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana ƙare mata kallo cikin zuciyarshi kam hamdala yake tayi,
  Sehrish dake tsaye tana kallon fuskar Oumman tasu,sae faman sakin murmushi takeyi,ji take kamar ta faɗa jikinta ta rungumeta sosai,'
  Sehrish ki zauna gefenta,bari na fita wurinsu Baban sadeeq,mun barsu a palour,"yayi maganar tare da miƙewa ya fuce daga ɗakin,
  Wuri Sehrish ta samu daga gefen gadon ta zauna,tana kallonta,
  "Allah ya baki lafiya Oummanmu,Nasan zakiyi farin ciki sosai,idan kika ga yadda ƴan ukunki suka koma,Ashe da rabon mukai wannan lokacin araye,mu dukkanmu"?hawaye ne suka soma saukowa daga saman fuskarta,kwantar da kanta tayi daga gefen Oumman,ta sanya hannunta tare da ruƙo nata,

Lokacin da Abusufyan ya koma palourn,A zaune ya samu Malam Nura tare da Maman sadeeq saman 3 seater,Nurse ɗin kuwa tana zaune saman 2 seater ita da Doctor,

After few minutes da shigarshi palourn,Sae ga wani Soja ya shigo hannunshi ruke da manya manyan ledoji na restaurant,A bayanshi kuma wani sojan ne hannunshi ruke da Katan katan na lemunsha,Saboda tsabar farin ciki,bakin Abusufyan yaƙi rufuwa,dama tunanin da yake yi kenan,gashi sun shigo da baƙi kowa ya kwaso yunwa gidan kuma ba wani abunsha,Balle abinci,
   Ƙarasowa ciki sukayi tare da ajiye kayan a tsakiyar palourn,
   Atare suka haɗa baki wurin cewa"Sgr ne,yace a shigo maku dashi,zaizo anjima,"
  Murmushi Abusufyan ya ɗan saki tare da cewa"Okey,mun gode sosai,Allah ya kawo shi lafiya,"
Juyawa su kayi atare suka bar ɗakin,

  Sehrish ya kira,ta ɗauki ledojin takaisu kitchen,acan ta haɗo masu kayan abincin A cikin warmers ta jerasu a saman tray,Saman dining table ta jera masu su tare da drinks,Gaba ɗaya nan suka harhadu,dama kowa ya kwaso yunwa,don sun jima a asibitin nan,Nan fa kowa ya shiga ɗurama cikinshi abinci,bayan sun ci sun ƙoshi,daga bisani,wuraren sallar magrib,Nurse ɗin tare da doctor su kayi

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login