Showing 429001 words to 432000 words out of 432432 words
Chapter 144 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete
lalubo Layin Hafsat ya danna mata kira,Kamar jira takeyi ta ɗaga kiran,
"Daughter ina sauraronki!maganar menene kikeson Yi dani"?
"Daddy dan Allah ka taimaka,Nasan zaiyi wuya ka fahimceni,wlh Mommy tana cikin mawuyacin hali,Ta zama abun tausayi,ta kira ni da wani layi jiya tana kuka tana rokona cewa inyi maka magana ka yafe mata,Ta gane kuskurenta,Rayuwarta ta wulakanta Daddy a gefen bishiya take kwana zaune ba bacci,dare da rana a wurin nan take Yini......."
Tunkan Hafsat takai ƙarshen Maganarta,Ishaq ya katse ta"ke yanzu kin yarda da maganarta?Kodai kun haɗa baki ne da ita?
Da sauri hafsat tace"Wlh daddy da gaske take,Ae nasa ta ɗauko mun video ɗinta,Wayarma fa aronta takeyi don ta kiramu,Zan tura maka video ɗin ta whatsapp yanzu,zaka shaida abunda nake faɗa maka,"
Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da cewa"its okey,Am waiting for the video,"yana kai ƙarshen maganar ya katse kiran,Kafin Ya kunna wifi ɗinshi ya shiga whatsapp,Messages ne suka fara shigowa cikin wayar,can sai ga saƙon hafsat ya shigo,
Chat ɗinsu Ya shiga,Anan ya samu video ɗin data tura mashi,yatsanshi yasa ya ɗan ta6a video ɗin nan take Ya soma loading,ƙura ido Ishaq yayi akan Screen ɗin wayar yana kallon video ɗin,
Bai ta6a tunanin zaiga laila a irin wannan ƙasƙantacciyar rayuwarba,a gefen bishiya take zaune,gefenta kwanon bara ne,ƙafarta ɗaya ta lalace babu kyan gani wani irin ruwa ke fita acikinta,Sae kuka takeyi tana magana
"Don Allah Ishaq ka taimaki rayuwata,ba don halina ba,dan Allah da manzonsa zakayi,Nasan nina jefa kaina cikin wannan halin,Ku kalli irin wurin da nake rayuwa,kowa ƙyamar taimakona yake yi,babu mai son zuwa wurina saboda warin da nake yi,"_
Saboda tsabar tashin hankali,Da sauri Ishaq ya kashe video ɗin tare da yin wurgi da wayar saman sofa ɗin,
Jingina bayanshi Yayi ajikin kujerar,tabbas Yaji tausayinta amma abunda ya ɗaure mashi kai shine taya akai taje Enugu!Uban me yakaita?don a iya saninshi bata da wata alaƙa da garin,Ya jima a haka kafin Ya ɗauki wayar Ya sake kiran Hafsat,
Tana ɗaga kiran Yace"Naga video ɗin,wlh hafsat ba don zuciyar musulunci ba,babu abunda zaisa na taimaki Laila!ke bari in faɗa maki zan taimaketa ne kawai Saboda Allah!Taci albarkacinki hafsat!Zansa a ɗaukota akaita asibiti,Inyaso ko ƙafarce su cireta A maidata maiduguri,Amma ni bazan sake rayuwa da laila ba,"
Fashewa hafsat Tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,daƙyar ta samu ta tsagaita da yin kukan tace"Nagode sosai Daddy,koma miye laifinta ne,ita taja ma kanta,naji daɗi sosai Daddy Am really proud of u,"
"Yaushe zaki dawo gida!kinsan cewa hutun aikin da kika ɗauka ya qare ko"?
"Eh daddy,Ina nan ina shirin dawowa amma yanzu gidan bazaiyi mun daɗi ba,nafison na zauna a wurinsu Abba,tunda ga ƴan uwana acikin gidan inyaso sai ka nema mun transfer na dawo aiki a Abuja,"
"Idan kika koma Abuja,ni kuma fa?nikaɗai akeso inyi ta zama a kaduna "?
A ɗan shagwa6e hafsat tace"idan zaka ƙara aure,Sai in dawo nan,"
Murmushi ya saki anzo dai dai inda yafi so,
"Calm down ur mind,just ki dawo gida kawai,Cikin ƴan kwanakin nan Nima zanyi aure,"
Yana jiyo sautin dariyarta,alamar taji daɗin maganarshi,sun jima suna waya kafin suka Yi sallama,
*Boss Bature*
*AMANI*
Tana kwance saman gadonta,Amal ta faɗo cikin ɗakin Hannunta ruƙe da wayarta,hawa saman gadon tayi har zuwa inda Amani ke kwance tana sharar bacci,Hannu tasa tana bubbuga ƙafarta,
"Aunty Amani!ki tashi ana kira,"
Daƙyar ta iya buɗe idanuwanta masu ɗauke da bacci,sun ɗanyi jawur dasu,rai a6ace ta kalleta"Bana hanaki tashi na daga bacci ba in aka kira ni"?
Sunnar dakai Amal tayi"Am sorry,dama Aunty hayaam ce ta kira tana kuka......"hankali aɗan tashe Amani ta yunƙura tare da mikewa zaune tana faɗin"kuka kuma!Allah yasa lafiya,"ta ƙarasa maganar tare da kar6ar wayarta da Amal ke miƙo mata,
Call log ta shiga,Anan taga kiran da hayaam tayi mata,
Calling ɗin layin tayi,bayan Hayaam ta ɗaga kiran Amani ta kara wayar a kunnanta,tun kafin tayi sallama taji shessheƙar kukan Hayaam
"Subhanallahi!wai meke faruwa ne?hayaam ki buɗe baki kiyi magana mana,"a ɗan ruɗe tayi maganar,
"Kodai Wani ya rasu ne"?
Sai lokacin Hayaam ta soma magana"Aunty amani muna cikin masifa!munga rayuwa,rayuwarmu ta wulaƙanta a idon jama'a......"anan hayaam ta kwashe dukkan abunda Ya faru bayan komawarsu maiduguri ta sanar da ita,
Saukowa Amani tayi daga saman gadon tana ambaton"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,.
"Allah yajiƙan Mammy,Allah ya gafarta mata zunubbanta,Amma banji daɗin irin mutuwar da tayi ba,ƙaddara ta riga fata,da kunsani tun farko baku barota ba,
Cikin shessheƙar kuka hayaam taci gaba da magana,
"Munaji muna gani,zama gidanmu ya gagaremu,Mutane sun ɗaura mana karan tsana,Yanzu haka a gidan Malam limam muke,matanshi sun tsanemu,suyi ta tseguminmu suna zaginmu,Abinci basu bamu sai in liman yana acikin gidan,Abra ma sai addu'a domin kuwa ta fara samun ta6in hankali,sai sambatu takeyi tana faɗin duk ita taja,Itace tayi silar mutuwar Mammy...."kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da ya cuyota,
Daƙyar Amani ta lallasheta"kuyi haƙuri ku rungumi ƙaddara,in sha Allah komai zai wuce,Yanzu nidai zanyi ƙoƙari wurin ganin na taimaka maku,Ko gidan ne a gyara maku shi,kafin Allah ya kawo maku mazajen aure,don kuwa yin auren shikaɗaine rufin asirinku,in ba haka ba mutane bazasu daina tsangwamarku ba,"
(Wlh matsalar mutananmu kenan,idan mutun Ya aikata zunubi arayuwarshi yazo ya yi nadama ya shiryu,Sai su dinga tseguminshi suna ƙyamatarshi,Shi kanshi Allah daya halicce mu yana son bayinsa waɗanda suka Tuba daga aikata zunubi,Amma wasu mutanan da ruƙo,shiyasa wasu ko sun shiryun daga baya sai su koma ruwa saboda mutane,Wannan babban kuskure ne saboda mutane ka koma kana aikata barna,Makomarka zaka duba,In zaka tuba dan Allah zakayi,Dan kuma kanka,ba don mutun ba,a karshe ina mai jan hankalinmu da mu kiyaye harshenmu don zai iya jefamu a halaka,aduk lokacin da wata mummunar kaddara ta fada ma wani muyi Addu'a mu nemi tsarin Allah kada mu rinka zundenshi don muma bamu fi karfin Allah ya jarabemu ba,Allah ubangiji ya rabamu da mummunan kaddara yasa mufi karfin zukatanmu,Amin )
Sosai Hayaam ta shiga yi mata godiya,kafin daga bisani Su kayi sallama,
*Boss Bature*
Wuraren ƙarfe 6 na marece,Sehrish na kwance saman gadonsu abun duniya ya isheta,duk ta shiga damuwa saboda rashin samun kwakkwarar hujjar da zasu kama Azmee,tana cikin wannan zancen zucin taji an banko kopar ɗakin,A firgice takai idanuwanta kan mai shigowa,Jahad ce ta faɗo ɗakin fuskarta sharkaf da hawaye,a ruɗe Sehrish ta shiga tambayarta Lafiya,
"Bakisan meke faruwa ba,Ga Abba can ya yanke jiki ya faɗi rai hannun Allah,"jin wannan maganar yasa Sehrish ta sauko daga saman gadon jikinta na kerma ta nufi hanyar fita ɗakin,atare da jahad suka fita,
Abunda ya faru,Alex na zaune gefen gado tana jiran fitowarshi daga toilet,tun da ya shiga shiru bai fito ba,tun tana sa ran fitowarshi harta fara tunanin ko lafiya kusan Awa ɗaya da rabi yana acikin toilet ɗin nan,Miƙewa tayi ta nufi toilet ɗin tasa hannu ta kwankwasa ƙopar"Abban Junaid!"ta kira sunanshi da ƙarfi,Shiru bai amsa mata ba,a ƙarshe dai ta yanke shawarar shiga ciki,tana tura ƙopa ta same shi kwance saman tiles,idanuwanshi sun jirkice,jikinshi sai kerma yake yi,Fasa ƙara Mommy tayi anan ta zube tana jijjigashi,Ganin cewa dagaske fa baya acikin hayyacinshi yasa ta miƙe da gudu ta fito daga ɗakin tana kuka,
A lokacin Abusufyan da abu suna zaune a main palour tare dasu Hosana da Jahad,Tun daga kan yarda ta faɗo falon Yasa su miƙewa suna tambayar lafiya,Kasa buɗe baki tayi sai dai nuna masu hanyar bedroom ɗinshi da tayi duk tabi ta ruɗe,da gudun gaske Abusufyan ya nufi ɗakin tare da abu,suna shiga ciki dama ƙopar toilet ɗin abuɗe Mommy tabarta,nan suka sameshi cikin mawuyacin hali,sunyi matuƙar girgiza,Cuccuboshi Abusufyan yayi ya fito dashi daga cikin toilet ɗin,Ya janyoshi zuwa saman gadon ya kwantar dashi,jiki na rawa Ya curo wayarshi saboda ruɗu daƙyar ya iya lalubo Layin Sgr ya danna mashi Kira,Sai daya bi kowannansu Ya sanar dashi halin da Mahaifinsu ke ciki,
A lokacin dasu Sehrish suka faɗo falon Ya yi dai dai da shigowar Omar da Sgr,da gudun gaske suka shigo kaitsaye suka nufi bedroom ɗin Abbansu,wucewarsu keda wuya Kanal yousouf ya faɗo falon da gudu shima Ya wuce part ɗin,gaba ɗaya sai da matasan gidan suka hallara a ɗakin,wasu tuni sun fara zubar da hawaye,tsoransu kada su rasa mahaifinsu a wannan halin da suke ciki,sae faman ambaton innalillahi wa'inna ilaihirraji'un suke yi,
Fawan dasu twins kuwa tuni sun fara kuka kamar wasu ƙananun yara,
"Addu'a zakuyi mashi ba kuka ba,in sha Allah zai samu lafiya,"acewar Abusufyan shi kanshi dauriya kawai yake yi,don kada suga rauninshi,hakan zai ƙara tayar masu da hankali,
yanke shawarar kaishi Asibiti suka yi,Sgr ne ya ɗauke shi asaman kafaɗarshi,Sauran suka bi bayanshi,
Suna fitowa entry hall ɗin gidan,da gudun gaske armstrong ya buɗe mashi mota ya kwantar da Abbansu aciki,Sannan ya bude mashi front seat ya zauna,Jan motar yayi da gudun gaske motar Marshal tabi bayansu,Motocinsu Kanal yousouf suka rufa masu baya,hada Oummansu Sehrish aka tafi asibitin a motar fawan ta zauna tare da Jahad da Hosana,Mommynsu Junaid kuwa tana a motarsu Abusufyan sai lallashinta Yake yi,duk ta shiga damuwa alokacin motocinsu suka fita daga babban gate ɗin gidan,mutun uku aka bari a gidan Aunty Azmee dake kumshe a ɗakinta,Sae Haroon dake kulle a medical room dinsu,
Sehrish bata samu tabisu ba,daga komawa ta ɗauko mayafinta sai dai tajiyo tashin motocinsu,kamar tayi hauka lokacin da ta fito waje bata samu motar ɗaya daga cikinsu ba,anan ta zuƙunna gaban ƙopar palourn tana kuka,ga tsoron shiga gidan da takeyi,
Da wata irin jiniya motocinsu suka hau saman titi a jere,Lokacin da suka ƙaraso Katafaren Asibitin Sgr,Sai suka tsaida jiniyar,a hanzarce bayan sunyi parking ɗin motocin nasu,Sgr ya fito Ya ɗauki Abbansu,sauran ma suka fito gaba ɗaya suka wuce cikin asibitin,Zo kaga taron nurses da likitoci,Ai tunda suka ji isowar Sgr kuma suka ji cewa Mahaifinshi ne baida lafiya,nan fa sukayi dandazo domin duba lafiyarshi,
A wani katafaren ɗaki suka kwantar dashi,kusan likitoci shida ne akanshi daga cikinsu hada Doctor Emran,
Sgr baisamu shiga ba,saboda a halin da yake ciki a yanzu bazai iya duba Abbansu ba,yana cikin matsananciyar damuwa saboda yasan dalilin ciwon Abban nasu,dama yace su fara ƙirgen kwanakin mutuwarshi,in har basu dawo mashi da yaronshi ba,
A saman waiting seat suka zazzauna suna jiran tsammani,Omar da Sgr suna a tsaye,Kowa ka kalli fuskarshi gwanin ban tausayi,
"I can't forgive my self,idan har Daddy ya mutu silar 6oye mashi mutuwar Junaid da mu kayi,"Ya ƙarasa maganar yayin da idanuwanshi suka cicciko tab da hawaye,
Ruƙo hannunshi Omar yayi"bakai kaɗai ba Rafayet,nima bazan yafewa kaina ba,in har muka rasa shi,wlh i ave regretted already,Da mun sani tunfarko mun sanar dashi gaskiya kawae tunda dama gudun hakan yasa muka 6oye mashi,"gaba ɗaya duk sun sha jinin jikinsu,
"Dan Allah kukan ya isa haka,twins,fawan da irfan,in na sake jin shessheƙar kukan wani acikinku wlh zaku koma gida ne,"kanal yousouf ne keyi masu faɗa,.
"Sai kace ba musulmai ba!maimakon ku tayashi da addu'a amma kun dage sai kuka kukeyi,"ya ƙarasa maganar tare da jan guntun tsoki,idanuwanshi cike tab da kwalla,
Abu kuwa sai faman lallashin Mommy takeyi,ganin yadda take ta shar6ar kuka,
Abusufyan ne yace"don Allah Aunty kidaina,kina ƙara tayar masu da hankalinsu,keda yakamata ace kina lallashinsu,"hannu tasa tana share hawayen fuskarta,juriyarce bazata iya ba,ita kaɗai tasan yarda take ji acikin zuciyarta,
Fitowa Doctor emran yayi daga cikin ɗakin da aka kwantar da Abbansu,Aikuwa da sauri suka tunkareshi,kowa yana tambayar ya jikin nashi,
"Ku kwantar da hankalinku,Yana samun sauƙi,Addu'ar ku kawai yake buƙata,"yakai ƙarshen maganar tare da aza idanuwanshi kansu Sgr da Marshal"ina son ganinku a office,"
Tunda suka ji haka sai jikinsu ya ƙara yin lakwas,gaba Dr emran Yayi suka bi bayanshi,har izuwa Office ɗinshi,Wuri ya samu ya zauna,kafin suma suka zauna suna fuskantarshi,
A tsanake ya soma yi masu bayani"nasan kunsan meke damun mahaifinku,damuwa ce akan rashin Junaid,Yanzu haka dana baro ɗakin,Sambatu yake yi yana ambaton sunan shi,"dakatawa ya ɗan yi da bayani yana kallonsu,jikinsu sai tsuma Yake yi,
"Jinin shi ne ya hau sosae,Ga kuma Ciwon zuciya dake barazanar kamashi..."
Tunkan emran yakai ƙarshen maganar,Omar ya dafe kai jikinshi na kerma,jikinsu Ya gama mutuwa,
"Yanzu ya zamuyi kenan?menene solution"?Sgr ne yayi tambayar,
"Akwai matsala fa,saboda ya ƙwallafa ranshi akan son yaron,Idan har ba ganinshi Yayi ba,tofa sai dai abishi da addu'a,"
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"miƙewa Sgr yayi da sauri ya fice daga Office ɗin,gaba ɗaya sun rasa inda zasu tsoma ransu suji daɗi,
Miƙewa Sehrish tayi daga zuƙunnan da take abakin ƙopar palourn,Hannu ta zura acikin aljihun rigarta,ta curo wayarta don ta kira Jahad taji Ya jikin Abban nasu,
Tana kunna wayar,ta shiga Call log anan ta samu missed calls da baƙuwar number,har kusan sau 10 aka kira,Batasan number ɗin wanene ba,Har jaraba kiran Layin tayi wayar nata ringing ba'a ɗaga ba,
Bayan kiran ya katse ne,ta lura da message ɗin da aka turo mata,Da sauri ta buɗe saƙon ta soma karanta shi kamar haka,
__Sehrish na kira layinki baki ɗaga ba,Amrish ce inason magana dake game da ɗan uwan nan naki,dan Allah idan kinga saƙon nan ki kira ni_
Abun ya ɗaure mata kai,tunani ta shiga yi wani ɗan uwanta ne Amrish ke magana akai,sake kiran Layin tayi wayar ta dinga ringing amma ba'a ɗaga ba,
Katse kiran tayi,tana ƙoƙarin juyawa ta koma cikin gidan kira ya shigo layinta da baƙuwar number,da sauri ta ɗaga kiran tare da kara wayar a kunnanta,tunkafin tayi sallama muryar Amrish ta katse mata hanzarinta,
"Sehrish kina ina ne!ina ta kiran Layin wayarki amma baki ɗaga ba,magana ce akan Junaid na tura maki Address ta message,kibar komai kikeyi kizo ki same mu"tana kai ƙarshen maganar ta katse kiran,
Wani irin faɗuwar gaba Sehrish taji,Abun ya matukar ɗaure mata kai,musamman data ambaci sunan Junaid,
Hannunta na kerma ta shiga duba message ɗin da aka turo mata,kwatancen inda zata same su ne,
Tarasa ya zatayi,ita dai ba mota gareta ba,gashi babu wanda ya rage acikin gidan balle ya kaita,kama hanya tayi ta miƙi titin da zai sadaka da babban gate ɗin gidan,Sae faman zumbula sauri take yi,Sai da tasha wahalar zuwa babban gate ɗin,Sojojin dake tsaron gidan suka hanata fita,kamar ta fashe da kuka,
A dole ta shiga kiran layin matasan gidan,Duk wanda ta kira bai ɗagawa,har Abusufyan ta kira shima bai ɗaga kiran ba,
Sai da ƙyar ta samu Hosana ta ɗaga kiranta,da sauri ta kara wayar a kunnanta,
"Hosana Ya jikin Abban"?
"Nima bansani ba,Sun shiga dashi ciki,"
"Dan Allah idan akwai wani kusa ki bashi wayar,"
"To"ta amsa mata,jim kaɗan taji muryar Kanal yousouf,
Sai da ta fara tambayarshi jikin Abban nasu,Ya sanar da ita cewa da sauki,tukunna tace"Gani nan zan fito gida an hanani,dan Allah ka taimaka kasa su barni na fita,nima asibitin zanzo,"
"Ki basu wayar,"Cire wayar tayi daga kunnanta ta miƙa ma ɗaya daga cikin sojojin,ya kar6a su kayi magana dashi sannan ya miƙa mata wayar,"Zaki iya tafiya,amma yace kada abarki ki fita ke kaɗai,don haka wani daga cikinmu zai ɗaukeki a mota ku fita,"
Ba ƙaramin daɗi taji ba,dama ƙarfin hali ne kawai,ko kuɗin abun hawa bata dashi,
Anan ta tsaya,wani sergeant ya ɗauko mota ta buɗe ta shiga ciki ya tashi motar,saida suka hau saman titi sannan yace"Madam ina zuwa"?
Karanto mashi Address ɗin wurin tayi kamar yadda Amrish ta rubuto mata a saƙon,
Wani private hospital ne suka shiga,sojan ya fito ya buɗe mata ƙopa ta fito daga ciki,a bakin ƙopar shiga ciki ta samu Amrish a tsaye hannunta ruƙe da waya,wani irin farin ciki ne ya lullu6e Sehrish da gudun gaske ta nufeta,rungume juna sukayi nan take Amrish ta fashe da kuka,
Ɗago da ita Sehrish tayi tana tambayarta lafiya,
"Amrish dama kina nan?layinki kona kira bana samu,meya sameki ne?me kike yi a asibitin nan ne"?
Cikin shessheƙar kuka Amrish tace"mu shiga daga ciki ki gane ma idanuwanki,"
Ta ƙarasa maganar tare da janyo hannun Sehrish suka shiga asibitin,A A&E aka kwantar dashi,a bakin ƙopar ɗakin Sukayi kici6us da Ya Mu'allim malamin da take ta nema,
Cike da mamaki ta ambaci sunanshi"Ya mu'allim,"fuskarshi da alamun damuwa atare da ita,Ya amsa mata"Na'am,kina ta nemana ko"?
Jinjina mashi kai tayi alamar eh
"Naga saƙon da kika turomin,idan muka samu natsuwa zamuyi magana,Yanzu dai ga ɗan uwanki can kije ki duba jikinshi,"
Gabanta ne ya faɗi rasss!,kawar da idanuwanta tayi daga kallon fuskar Ya mu'allim ta mayar da idanuwanta kan ƙopar ɗakin,mutun ta hango kwance an sanya mashi oxygen a hancinshi,yayin da hannunshi ke sanye da robar ƙarin jini,zuciyarta na harbawa a haka ta nufi cikin ɗakin,lokacin data ƙarasa gaban gadon tayi arba da fuskar Junaid,Sai ta yanke jiki ta faɗi a sume.......
Shigowa Cikin ɗakin Ya mu'allim yayi tare da Amrish,ruwan dake ajiye saman drawer din dake gefen gadon Ya ɗauka,Ya cire murfin ya tarfa ruwan a tafin hannunshi Ya watsa mata akan fuskarta,Nan take ta farfaɗo tana faman Sauke ajiyar zuciya,Yayin da take ambaton Sunan Junaid abakinta,Miƙawa tayi agaban gadon ta zube saman guiwowinta,kamar a mafarki haka take ganin Junaid,bazata Iya jurewa ba,fashewa tayi da matsanancin kuka yayin da take kallonshi,Dama sai da ranta ya bata cewa Junaid bai mutu ba,Yana araye,Ashe dagaske ne,tasha kuka ta gode ma Allah,Cikin shessheƙar kuka ta soma magana tana kallon Ya mu'alim da amrish dake a tsaye,
"Taya akai junaid daya mutu ya dawo?a ina kuka same shi,A iya saninmu junaid yayi hatsarin mota Ya ƙone ƙurmus"
Jin wannan maganar yasa Ya mu'allim da Amrish suka kalli Junaid,har suna haɗa baki wurin cewa"Junaid Yayi hatsarin mota'?
Jinjina kai Sehrish tayi"Babbar motace tabi takan Motarsu,Wuta ta kamaci,ba'a samu komai daga sassan jikinshi ba,wannan Shi ne abunda muka sani a game dashi....."tana kuka ta Zayyana masu Komai daya faru har 6oye mutuwar junaid dasu Marshal Su kayi,Da kuma Halin da abbansu ke ciki na rashinsa,.
Amrish tasha kuka hada majina,Shi kanshi Ya mu'allim jurewa kawai yake yi,rashin imanin Yayi yawa
"In sha Allah komai Yazo ƙarshe,duk wanda keda sa hannu a wurin cutar da family ɗinku,Zai gane kuskurenshi,don wannan karan da shirina nazo,"Babu wasa a fuskarshi yayi maganar,
"Dan Allah ku faɗamun ya akai kuka samu junaid"?tayi maganar yayin da take share hawayen fuskarta,
Anan Amrish ta kwashe dukkan abunda Ya faru daga farko har ƙarshe
Miƙewa Sehrish tayi tana kuka,Ta rungume amrish tana Yi mata godiya,bawan Allah ashe shine Yake tura mana saƙo da layinki,muka kasa gane wanene,da yake ni ina da numberki,Shiyasa saƙon Ya bayyana da sunanki,nayi tunanin ko kin yada wayarki ne,Ashe junaid ne ya ɗauketa,Bawan Allah,wlh da