Showing 354001 words to 357000 words out of 432432 words

Chapter 119 - Abban Sojoji Book 2 Hausa Novel Complete

haka ne?kin takurawa rayuwata Hosana,A haka kikeso na"?
  Turo baki tayi tana ɗan satar kallonshi,
  "Baki son farin cikina,kullum burinki ki addabi rayuwata kib hanani sakat,Zunubin me na akaita maki ne,"
   Ashagwa6e tace"Bakomai,"
  "Kinfi so ki ga hawaye na ko,"
Girgiza mashi kai tayi alamar,A'a,
Hannu yasa ya rufe fuskarshi yana raira mata kukan ƙarya,
  Nan fa hankalinta ya tashi,tabi ta ruɗe,
  "Ya Omar bazan ƙara zuwa ba,dan Allah kadaina kukan,yanzu zan tafi na barka,"jiki na rawa ta sauka daga saman gadon tana ja da baya baya tana faɗin"ka gani ko?tafiya zanyi,bazan ƙara dawowa ba,dan Allah ka daina kukan toh,"
  Ƙasa ƙasa ya dinga dariya batare da taji shi ba,har sai da ta fuce daga ɗakin sannan ya zame hannunshi aranshi yace"fitinanna,Allah yasa Daddy ya dawo cikin week ɗinnan zansa a ɗaura mana aure,At first night,zan koya maki hankali,duk wani hauka da kike ji asaman kanki saina sauke maki shi,"
  Yana maganar yana dariya,a yayin da yake saukowa daga saman gadon,jallabiya ce ajikinshi,toilet ya wuce,

Wuraren karfe 8,Sehrish ta farka da wata irin matsananciyar Yunwa,a gaggauce ta miƙe,ta ɗauko jallabiya ta zura a jikinta,kitchen ta wuce,batare da 6ata lokaci ba,ta ɗaura girki,bazata iya jure dafa abu mai wuyar dafuwa ba,Shiyasa ta ɗaura Indomie shaf shaf ta kammala dafuwarta,A cikin plate ta kwasota ta fito daga cikin kitchen ɗin,ta zauna a palour tana ci,sai lokacin ta shiga tunanin ko'ina su Uncle suka tafi?daga fita sallar Asuba har yanzu basu dawo gidan ba,yanke shawarar kiransu tayi idan ta kammala cin taliyar,asaman table tabar plate din da sauran taliyar,ta koma kitchen ta haɗo kakkauran Tea wanda yaji madara da bournvita,dawowa tayi falon ta zauna tana kur6arshi a hankali,

Tana cikin shan tea ɗin nan,taji dirar motarsu acikin gidan,Uncle Abusufyan ne ya fara shigowa cikin gidan,Miƙewa tayi da sauri tana fadin"Daddy,sannu da dawowa,"
  A gaggauce ya amsa mata"Yawwa Daughter,ɗaukko mayafinki mu tafi,dattijon nan ya kira ni a waya,badajimawa ba,"
  Jin haka yasa ta ajiye cup din hannunta asaman table ɗin gabanta,Jiki na rawa ta wuce ɗakin,jimm kaɗan ta dawo sanye da mayafi tayi rolling ɗinshi,hannunta ruƙe da wayarta,
  Shigowa cikin palourn tayi batare da 6ata lokaci ba,Abusufyan ya ruƙo hannunta suka fito waje wurin motarshi,Security ta gani suna tsaron gidan,tana ganinsu ta gane cewa mutanen babban yaya ne,
   buɗe motar tayi ta shiga,Abusufyan ya shiga ya zauna a mazaunin driver,tashin motar yayi tare da yin reverse ya karya kwana,da gudun gaske ya fuce daga cikin gidan,Kai tsaye suka haura saman titi,hannunshi har kerma yake yi saboda saurin da yake yi,burinshi kawai su ƙarasa cikin unguwar,
   "Daddy,ina yaya Rafayet ɗin?naga banganshi ba,"
  "Nabarshi a hotel,tun bayan da muka kammala sallar Asuba,Ni kuma na wuce gidan wani Old friend ɗina dake anan,Na jima acan,ina kan hanyar dawowa Dattijon ya kira wayata,Yake sanar dani cewa Malam Nura ya dawo"ya ƙarasa maganar adai dai lokacin da yake ƙoƙarin juya sitiyarin motar,Cikin unguwar suka shiga,a bakin bishiyar bedi yayi parking ɗin Motar cikin layin,tun kafin su fito daga cikin Motar suka hango ƙopar gidan a buɗe,bayan sun fito daga cikin Motar,Abusufyan ya daga hannunshi sama tare da cewa"Ya Allah kasa muji alkhairi!"
  Sehrish ta amsa mashi"Ameeen Daddy,"
  A ƙopar gidan suka tsaya,Abusufyan ya kwaɗa sallama,cikin sa'a suka ji an amsa masu sallamar tasu,Jimm kaɗan sai ga wani matashin saurayi dogo siriri ya fito daga cikin gidan,jikinshi na sanye da yadi,
  Miƙa ma Abusufyan hannu yayi suka gaisa,kafin yace"baƙi mukayi ne,"Abusufyan yace"Eh,baƙine,muna neman Malam nura ne,Allah yasa yana nan,"
  Tunda saurayin ya fito idonshi na akan sehrish,kallon sani yake yi ma fuskarta,ita kanta kallon nashi takeyi,kamar taso ta gane shi,da alama tasan shi tun yana da ƙuruciyarshi,Ranta ne ya bata cewar kodai Sadeeq ne ɗansu ya girma haka"!?
  "Da ace kun ƙara minti Biyar baku zo ba,da kun rasa shi,don kuwa yanzu yake shirin komawa Islamiyya,"
  Wani irin farin cikine ya lullu6e Abusufyan"taimaka kayi mana sallama dashi,".
  "Toh,"ya amsa tare da juyawa ya shige cikin gidan,after some minutes ya dawo hannunshi ɗauke da tabarma,A cikin zauren gidan ya shimfiɗa masu ita,
   "Ku shigo daga ciki ku zauna,yanzun nan zai fito,"
  "Yawwa mun gode ƙwarai,"Abusufyan ne yayi maganar tare da ruƙo hannun Sehrish suka shiga zauren,A saman tabarmar suka zauna,Suna jiran tsammanin ganinshi,
  Wayar Abusufyan dake acikin aljihunshi ce ta soma ringing,da sauri ya zaro wayar,yana duba mai kiran nashi Sunan My first in~law ne,Amsa kiran yayi tare da kara wayar a kunanshi,
  "Uncle,A ina zan same ku"?Rafayet ne yayi maganar,
   Abusufyan yace"muna a hotoro,Amma kaɗan jira kaɗan zan tura maka da address ɗin gidan,Sai kazo,"
  Sgr yace"okey,I will be waiting,"
Rejecting call ɗin yayi,yana ƙoƙarin mayar da wayar cikin aljihunshi,Wani babban mutun ya shigo cikin zauren,bakinshi dauke da sallama"Assalamu Alaikum,"atare suka amsa mashi sallamar,yayin da suka bi shi da kallo,
  Daga ganin mutumin ya kwana biyu a duniya,ya manyanta sosai ya fara tsufa,Jikinshi na sanye da shiga ta musulunci,ta waɗanda suka amsa sunansu malamai,hannunshi na ruƙe da cazbaha,kanshi kuwa rawanine,A mutuncen shi yazo,
  Kamar yadda suke kallonshi shima haka yake kallonsu,yanayin kallon dayake yi masu kamar kallon sani ne,wuri ya samu agefen tabarmar ya zauna suna fuskantar juna,Shi dasu,
  Da sauri Abusufyan ya shiga gaisar dashi"ina kwana baba,mun same ku lafiya,"
  Fuskarshi asake ya amsashi lafiya lou,Alhamdulillah"
  Gaba daya hankalinshi na akan fuskar Sehrish,kallon ƙurulla ya shiga yi mata,nasan gano a ina yasan fuskar yarinyar,Sunnar da kanta ƙasa tayi tana wasa da yatsun hannunta,
   ɗauke idanuwanshi yayi daga kan sehrish ya mayar dasu kan Abusufyan yace"Ince dai lafiya ko?naji kunyi shiru baku gabatarmun da kanku ba,Gashi ni bansan ku ba,"
  Murmushi Abusufyan ya ɗan yi tare da gyara zamanshi,Atsanake ya soma kora mashi jawabi,
  "Ni sunana Abusufyan,Wannan kuma ƴa tace,Sunanta Sehrish,'
  Gabanshi ne ya faɗi rass,aɗan tuɗe ya maimaita sunan"Sehrish"kamar irin ya ta6a jin sunan,
  Cigaba da magana Abusufyan yayi"nasan baka gane ta ba,saboda sanin da kayi mata tun na ƙuruciya ne,Amma nasan ba zaka iya mantawa ba,Da ZAINABU ABU BUZUWA MATAR MAKWABCINKA YA SAYYADI,"
  Saboda tsabar kiɗima Malam Nura ya zabura tare da miƙewa tsaye yana kallonsu hankalinshi aɗan tashe yace"dan Allah kuyi mun bayanin su wanene ku?menene alaƙarku da zainabu abu da kuma sayyadi"?
  Miƙewa Abusufyan yayi yana ƙoƙarin kwantar mashi da hankali yace"pls baba,dan Allah ka koma ka zauna muyi magana atsanake,"
  Rai a6ace malam Nura yace"Idan maganar wannan fasiƙin mutumince ta kawoku to ku tattara kubarmin gidana!Banason ganinku,banason ganin duk wani abu daya shafe shi,ku fuce kawai tun kafin ranku ya 6aci a wurin nan "yana magana jikinshi na kerma saboda tsabar 6acin rai,
  Ganin yana ƙokarin korarsu yasa sehrish miƙewa tsaye cikin sanyin murya tace"Baban sadeeq,Ka manta da ƴan ukun zainabu abu da ta haifa"?
  Mayar da hankalinshi yayi sosai akanta yana kallonta,
  "Ni ɗaya ce daga cikinsu,nasan baka manta damu ba,Nice Sehrish ƴar uwarsu Jahad da Hosana"
   Cike da mamaki Malam nura ke kallonta,hannunshi na kerma ya nunata da ɗan yatsanshi daƙyar ya iya furta cewa"kek..ke..ƴar wurin zainabu abuce?
  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,tace"Ni ce SEHRISH Baban sadeeq,su jahad ma suna nan araye,"
  Wasu irin zafafan hawaye ne suka soma sauka akan fuskar malam nura,ruƙo hannunta yayi yana kallonta,la66ansa sae kerma sukeyi,yayi matuƙar mamaki ganin yarinyar,bai ta6a tsammanin cewa yaran zasu rayu ba,abun yayi matukar daure mashi kai,
  Cikin shessheƙar kuka yace"Allahu akhbar!Wai dagaske ƴa'ƴan abu suna araye a doron duniyar nan?Dagaske ne abunda idona suke gane mun kuma suke jiyomun!Ya Allah kasa ba mafarki nake yi ba,"kuka sosai ya fashe dashi,duk yabi ya ruɗe bawan Allah,
  Kama hanyar shiga cikin gidan yayi,yana kwaɗama maman sadeeq kira"Murja!!murjanatu!kina inane kizo dan Allah,Ki ganemun wannan abun al'ajabin,Yau gani ga jinin zainabu abu har cikin gidana,Abun da muka daɗe muna jira,yau Allah ya amsa addu'armu"
  Jin wannan maganar ta Baban sadeeq yasa Maman sadeeq ta miƙe zumbur daga zaunen da take saman sallaya,buguzun buguzun ta faɗo cikin zauren,turus ta tsaya abakin zauren tana ƙarewa Abusufyan da Sehrish Kallo,
  Malam nura yace"kin gani ko?Yaran nan sun rayu,Wahala batasa sun mutu ba,dama nasha faɗa maki cewa Allah yana tare dasu a duk inda suke,Allah shi zai kula da abunshi,Yau dai maganata ta tabbata,kalli ki gani wannan yarinyar ƴar wurin zainabu abu ce fa,Sehrish ce"yayi maganar yana nuna mata sehrish,
  Hannu murja tasa ta daki ƙirjinta tare da Ambaton sunan Sehrish da ƙarfin gaske,
  Da gudu sehrish ta ƙarasa wurinta suka rungume juna,tare da fashewa da wani irin matsanancin kuka,kamar ransu zai fita,
  Tuni idanuwan Abusufyan sun cicciko da kwalla,shi kanshi baisan lokacin da hawaye suka wanke mashi fuskarshi ba,
  Gaba dayansu sun shiga cikin wani irin yanayi na ban tausayi,kowa da abunda yake tunawa acikin ranshi,
  Cikin shessheƙar kuka Maman Sadeeq ta dafa kafaɗun Sehrish tana faɗin"Ashe rai kanga rai!Rishi kece kika girma haka?lallai Allah Al musawwir ne,Kalli yadda rayuwa ta sauyaki,Ban manta lokacin da kuke rayuwa a wulakance ko takalma babu a kafafuwanki,Ya Allah na gode maka daka nuna mun wannan ranar,Yau gani ga ƴa'ƴan aminiyata zainabu abu,Wayyo Allah farin ciki,"zubewa ƙasa tayi ta fuskanci gabas tayi sujjada tana kuka tana godewa Allah,hakan ba ƙaramin ta6a masu zuciya yayi ba,
  Sun ɗauki tsawon lokaci suna wannan koke koken,kafin daga bisani komai ya lafa,Saman tabarmar suka koma suka zauna,cike da jimami,kowa yayi shiru na ɗan wani lokaci,
Kafin Abusufyan ya soma magana"Baba waɗannan ƴaran ƴa'ƴana ne,bana sayyadi ba,Ya yaudaremu ne gaba ɗayanmu ya auri abu da cikina,batare da saninmu ba,Wannan shine silar duk wani abu daya faru a rayuwarsu...."
  Tunkan ya ƙarasa maganar Baban sadeeq yace"Dama najima ina zargin cewa,ƴan ukun nan bana shi bane ashe dagaske ne,Ya Allah kayi mana maganin Fasiƙin mutumin nan,Ka kawo mana ƙarshen shi,Mugu azzalumi ya jima yana cutar rayuwar yaran nan,In sha Allah ƙarshen shi bazaiyi kyau ba,"ranshi a 6ace yake yin maganar,
  "Sehrish ina Hosana take baiwar Allah"Maman sadeeq ce tayi maganar har lokacin hawaye ne ke shararowa akan fuskarta,
  "Duk suna nan lafiyarsu ƙalou muna atare dasu cikin danginmu,"
Murmushi Maman sadeeq ta saki tare da cewa"Allah sarki,rayuwa kenan,"
  "Baba ko kuna da labarin Abu"?Abusufyan ya jefo masu tambayar,
Gabansu ne ya faɗi atare suka kalli juna jin tambayar da Abusufyan yayi masu,
  Hakan ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba,tun daga kan irin kallon da yaga sunyi ma juna yasa shi shan jinin jikinshi,. 
  Hankalin Sehrish a matuƙar tashe tace"Dan allah,ku faɗamana a ina Oummanmu take?nasan kuna da masaniya akai,"
  Shiru sukayi batare da sun basu amsa ba,nan take Sehrish ta fashe da kuka tana cewa"dama nasani,zai yi wuya mu sameta araye,innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,"
  Ƙiriss ya rage zuciyar Abusufyan ta buga,zumbur ya miƙe yana ƙoƙarin barin wurin,hannunshi dafe da saitin zuciyarshi,
    Muryar Baban sadeeq ce ta katse mashi hanzarinshi,
   "ABU TANA RAYE,"
jin wannan maganar yasa,Abusufyan komawa dirshan ya zauna,muryarshi har shaƙewa take yi wurin cewa"dagaske abuna tana araye?dan Allah ku faɗamin gaskiya,abu tana raye?tana ina?a ina zan ganta?"
  A natse baban sadeeq ya soma kora masu jawabi,
  "Tun bayan lokacin da Hosana tayi jinya a asibiti sakamakon Buguwar da kanta yayi harta samu ta6in hankali,nasan kunji labarin nan a wurinsu Sehrish,"ya ɗan dakata dayin maganar yana kallon fuskokinsu,
  "Hakane,munji komai a wurinsu,"a ƙagare Abusufyan yayi maganar,jikinshi sae tsuma yake yi,ita kanta sehrish ta ƙosa taji abunda zaice,
   "Tun bayan da aka kwantar da Hosana gadon asibiti,lokacin ana ƙoƙarin tattara kuɗin da za'ayi mata aiki,kwatsamm aka nemi mahaifiyarsu aka rasa ƙasa ko sama,tun bayan da ta sanar masu cewa zata je gida ta sanar da sayyadi halin da yarinyar take ciki don tunda aka kwantar da ita bai leko asibitin ba da tunanin ko asamu wani abu daga wurinshi,Don acika ayima yarinyar aiki,tunda ta haura ƙafa tabar asibitin bamu ƙara jin ɗuriyarta ba,"
  Shiru ya ɗan yi yana sauke ajiyar zuciya kafin ya daura da cewa"A lokacin Hankalin mu ba ƙaramin tashi yayi ba,ga yarinya ba lafiya kwance gadon asibiti rai hannun Allah,Ga sauran ƴan uwanta dake a cikin ƙuncin rayuwa na rashin ganin mahaifiyarsu da basu yi ba har tsawon kwanaki,wannan yasa muka bazama neman abu acikin unguwar nan,Saƙo da lungu ba'a sameta ba,Gashi gidansu a garkame da kwaɗo,har muka fara tunanin cewa kodai Abu ta gudu ne tabar yaranta,wata'ƙil damuwace tayi mata yawa,shiyasa ta ta tafi tabarsu,Jinyar hosana ta koma hannun Maman sadeeq itace taci gaba da kula dasu a asibiti,"
  Dakatawa ya ɗan yi da jawabin,na wani lokaci kafin yaci gaba da cewa"Ana haka,wata rana na dawo daga masallaci,ina ƙoƙarin shiga gidana,sae ga wani yaro nan,Umari ɗan wurin makwabcinmu ne shima,Yana tsaron shagon mahaifinshi abakin hanya,shi ya tare ni yayi mun sallama,Na juya na amsa mashi sallamar,yace mun malam inason magana dakai,game da Matar mutumin nan makwabcinka,Ya sayyadi,koda naji ya ambaci hakan sai na mayar da hankali sosai akanshi nace mashi"ina sauraronka,Anan ne yake sanar dani cewa,Ya gamu da abu akan hanya tana hauka babu takalma a kafafunta babu mayafi a jikinta,tana kuka tana sambatu tana fadin cewa Ya kashe mun babana,Ya rabani da mijina!kuma zai kashe mun ƴa'ƴana,'lokacin da Umari ya sanar dani wannan maganar hankalina ba ƙaramun tashi yayi ba,tun kafin ma ya ƙarasa maganar,jiki na rawa na hau babur ɗina na koma asibiti,a gaggauce na tattara yaran nan,nasa aka kaisu katsina wurin kishiyar babata,bakomai yasa nayi hakan ba,sai don gudun kada kalaman Zainabu abu su tabbata da gaske,Saboda a nazarin da nayi,wannan sambatun da akace tana yi yana da alaƙa da haukanta,Tabbas ya sayyadi shine yayi silar mutuwar mahaifinta,shiyasa har abun ya tsaya mata aranta,kuma ya ta6a mata zuciya har ta samu ta6in hankali,wannan dalilin yasa na ɗauke yaran gaba ɗaya na mayar dasu can,saboda inajin tsoran Ya sayyadi ya halakar dasu,"

Ganin ya dakata da yin maganar yasa Abusufyan saurin cewa"Yanzu a wani hali abu take ciki?kun samu nasarar gano inda take,"
Miƙewa Maman sadeeq tayi tare da shigewa cikin gidan,Jim kaɗan ta dawo hannunta ɗauke da tray,ruwa ta ɗebo masu acikin Jug,sae ƴan kofuna guda uku,Ajiyewa tayi agabansu,tare da tsiyaya ruwan ta miƙa ma Baban Sadeeq,hannu yasa ya kar6a tare da kai kofin bakinshi yana sha,
Ƙara zuba ruwan tayi a sauran kofunan ta dauka ta miƙa ma Abusufyan,girgiza mata kai yayi tare da cewa"Bazan iya shan komai ba,in har banji a wani hali abu take ciki ba,"sam babu kwanciyar hankali atattare dashi,
Miƙa ma Sehrish ruwan tayi,"kar6i kisha ƴata,"hannun sehrish na kerma ta kar6i kofin takai ruwan abakinta tana sha,

💋Boss Bature💋*



Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*

*Father of soldiers*

*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*

💫💥💫💥💫💥💫💥💫💥💫

*_ALBISHIRINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE , SHAHARARRAR KUMA KASAITACCIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WADDA KUKAFI SANI MAMAN YUSUF YAR SOKOTO TANA YI MAKU ALBISHIR DA CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE CIKIN FADIN NIGERIA DA NIGER KARKU MANTA MACE MAI KYARA KANTA BATA BORANCI_* 💃💃💃💃💃💃💃 07069711327

_Akwai zafafan kayan Mata masu kyau da arha cikin sauki da rahusa Kuma duk inda kike zamu aika maki kayanki cikin aminci da yardar Allah ba cuta ba cutarwa don a Dade anayi sai gaskiya uwargida da amarya ku garzayo Kar abaku labari_

Munada kalolin Kaya kamar haka💥💫💥💫💥💫👇🏻👇🏻

Maganin sanyi sahihi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata

Maganin gyaran nono domin dawo da martaban nononki hadin gargajiya da bashida illah ajiki

Maganin hips Mai tado da hips cikin kankanin lokaci

Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko dai dai misali kiyi kyau kema ki shigo cikin jerin Mata masu aji

Maganin rage kiba da tumbi Wanda zaisa ki sace ki koma Yar dai dai abin alfaharin kowane namiji,

Akwai kalolin gumbuna masu kyau da saukar da ni'ima

Maganin matsi masu ciko da gaba da matseki Kamar Yar budurwa uwa uba zasu Baki dandano Mai gamasar da maigida

Kalolin garrika masu bawa mace niima da jimawa ajiki

Kalolin tsumi Sha yanzu magani yanzu dasa Mai gida ihun Dadi

Zumar mallaka
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Zumar Mai rubutu

Hadin mallaka
Turaren mallaka
Shu'umar humra
Turaren AL'AJABI
Matan gaske
Ak 49
Sirrin tafin k'afa
Turaren fuska
Hatsabibin turare
Kwallin mallaka
Zoben mallaka
Jigidar maida tsohuwa yarinya
Maltinar Mata
Karya gado
Yajin Mata (yajin Mai ciko da mace)
Yajin maza (domin Karin k'arfi)



Muna dahuwar Kaya kamar haka💫💥💫💥👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

Dahuwar zabo (mallaka)
Kazar Yar gata
Yan shila
Ciccibi
Dambu
Zuciya
Yan ciki
Kwai ukku
Tsoka Tara
Kifi
Da sauransu


Akwai sirrika sosai da muke hadawa ga wacce kishiya ta addabeta ko wadda take fama da butsarin namiji ko mafadacin namiji ko namiji Mai yawon dare ko Wanda yake bin Mata insha Allah duk zaku samesu Kuma da yardar Allah za'asamu biyan bukata

Muna bada magani ga yarinyar da tsautsayi ya fad'a Mata ta rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji Kuma insha Allah zaadace da yardar Allah

Abubuwan da yawa gsky Wanda in nace Zan lissafasu sai nakwashi tsawon lokaci maiso tabini PC don ganin kalolin kayan da muke dasu ,

Karku manta mace Mai gyara kanta Bata boranci taku ce maman yusuf Yar mutan sokoto 07069711327
.
Don Allah wadda Bata shirya ba tabari sai ta shirya sannan tayimun magana🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼ngd

07069711327


*Boss Bature✍️*



"Bayan komawarsu hannun kishiyar babata,Sai hankalin mu ya dawo kan tunanin a ina zamu ga uwar yaran nan,Nemanta muka bazama yi acikin unguwar nan ruwa A jallo,duk wasu gidajen masu unguwanni na kewayen mu mun cigita haka ma ofishin yan sanda,tsawon lokaci ana nemanta bamu same ta ba,Hankalinmu ya tashi,Saboda sanin cewa Yarinyar nan bata da kowa,Gashi tabar gida a wani yanayi na ta6in hankali,Ga ƴa'ƴanta dake buƙatarta,hakan yasa bamu yi kasa a gwiwa ba ni da baban umari muka kai cigiya awani gidan Redio amman shiru kake ji ba Abu babu dalilinta Allah kaɗai yasan ina ta nufa don kasan garin kano da faɗi,aƙarshe muka fara zullumin anya Abu na'a garin nan ma kuwa,hakan yasa muka hana idonmu bacci wurin rokon ubangijin sammai da kassai da ya bayyana mana ita cikin aminci ya kareta aduk inda take,tsawon lokaci muna ta rokon Allah ba tare da gajiyawa ba,Ana haka kwatsam wata rana muka samu labarin bayyanar Abu ta hanyar Sanarwa a gidajen radio dana talabijin cewa Ana neman danginta,tare da adireshin asibitin da aka kwantar da ita sakamakon motar wani bawan Allah da ta bugeta a saman titi tana gararanbarta shine ya kaita asibiti ya kuma bada ayi cigiyar danginta,koda sanarwar nan ta isar mana jiki na rawa,Ni da Maman sadeeq tare da yaron nan ɗan wurin makwabcinmu muka kwasa muka tafi asibitin,ba ƙaramin daɗi muka ji ba da muka samu abu zuciyoyinmu suka cika da farinciki,duk da babu hankali atattare da ita,A lokacin likitan dake kula da ita ya buƙaci akawo wani makusancinta,wata'ƙil adace ta dawo cikin hayyacinta idan tayi ido biyu da ƴa'ƴanta da take

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login