Showing 36001 words to 39000 words out of 255288 words

Chapter 13 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1360

kasa da shi,
Gaskiya duk abinda zaiyi wanan karo saidai ayi ta don dai shi yayi niyar tallafawa Abdullmalik din,
Da wanan tunanen a zuciyar shi ya kwanta barci sai juyi yakeyi a tafkeken gadon nashi,

Aisha wace tai shawaran zuwa Lagos gurin Joseph
Don dai tagane cewa idan ta cin mai can tafi samun kudi, bisaga in yazo nan garin
Don anan mutane sunayi mai yawa ga bukatun yau da kullun,,,
Saidai tayi rashin saa yace mata aranan ya wuto zuwa kaduna don halartan wani taro da zasuyi akan karin farashin da,suke son yi
Bata hakkura ba don haka kaduna tasamay shi
Saidai yana gurin meeting a lokacin don haka driver ya tura yadauko daga tasha zuwa inda yai masauki,,
Sai gab da magriba yadawo yace ta shirya su, wuce zuwa Abuja yanada uzuri kala,kala acan don haka ba zai samu damar tsayawa kaduna din ba,,,
Waya yakeyi alokacin don haka sai yaga kawai Aisha tana kokarin har hada kayan ta,
Yana gama wayan yakai kallon shi gareta yace, sai naga kamar lokacin sallah yayi ko,?
Bazakiyi sallah ba kafin mutafi, inafa zai fi maki don sai dare nasan zamu karasa,
Tana wani jan kafa kamar bata son yin sallah a lokacin,
Har ta idar yana zaune sai dan,ne danen wayar shu kawai yakeyi,
Duk da bawai yasan ya ake sallah ba yadai fahinci cewa batai wani dadewa ba a gurin yin sallah,
Don haka da mamaki yake ce mata har kin gama ko,??
Don haka mikewa yayi yadauki duk wani belongings na shi dake daki zuwa waje,
Sai cikin dare suka samu isah don haka masaukin shi ya wuce direct, don KB yasan da zuwan shi,
Yasa an gyara komai duk da dai dama gidan kullun acikin gyara yake,
Shikan Joseph suna isa a cikin daren nan fita yayi zuwa gurin wani mutum da yake son gani,
Aisha tun tana jiran shi tana yar tsuki, har barci ya dauke ta, bada sanin ta ba,
Kodo Joseph yadawo yasamu tayi barci don haja ko take away din da ya zo masu dashi batasamu ci ba,
Kiran sallah da akeyi daga wani unguwa wanda da alama ba nisa daga gidan Joseph din shi yata da Joseph din a lokacin wanda dama al,adanshine haka duk wani Christian mai rikon addini yana tashi daidai wanan lokacin,
Don yin morning prayers din su kullun,
Aisha tana kwace shemay shamay saman gado, tana barcinta abinta,
Yar rigar barcin da tasa don daukar hankalin Joseph, har barci ya kwashe ta yadan kware gefen ciyar ta a fili,
Don haka yana fitowa yin burshe, ya isa har bakin gadon inda ake kwance ko motsawa batayi ba,
Yana mamakin wanan irin barci haka ace mutum bai tashi ya yi morning prayer, haka,
Hannu yakara kaimata yana dan dukar cinyar ta data dan kware wurin barci,
Yana cewa baki tashi kiyi salkah kadafa time ya wuce ki,
Sai wani mika takeyi shiko sai kallon mamaki yake mata alokacin
Yaga cewa ai Assalam yarone amma duk yake tare dasu akai kiran sallah
Zakaga yaron na kokarin tashi zuwa yin sallah,
Amma ita gata da girma ta yaga bata damu da ta tashi yi ba,,,
Kallon inda yake tayi ido tafa da kwana, tace mai kabari kawai inda na tashi ai zanyi,
Wani irin mamaki ya kama shi azuciyar shi yana mai cewa O God help me with dis ,
Aisha sallah ma bazaki tashi kiyi ba sai kinga dama,
Haba kiwa kanki fada mana ai dis is bad wlh, abindan lokaci kadan,,
Tai wani mika badon taso ba ta tashi buguzun,bugunzun zuwa cikin bathroom, ko minti nawa bata kai ba saigata tafito wani dan yalalon gyale ta yafa
Joseph wanda yai daidai da gama addu,an shi ya na kokarin rufe Bible din shi ya kalle ta yana mai kada kai cikin mamaki don ganin gyaken da ta yafa wai zatai sallah, dashi,
Kwanciya ya yi rigingine ya kallon yadda take dangwara goshi kamar wace keda wani uzuri ,a gaban ta,
Ba,afi mintuna ba ta sallamay tafado mai saman gado gaba dayan ta,
Kokari takeyi ta fara romancing din shi sai yai dabara yadan jaye ta daga jikin shi yana nai ce mata zan dan fita jugging ne yanzu kafin gari ya haska,
Yajaye daga jikin shi yana mai kojarin daga wa don ya sauka saman gadon,
Sunan shi takira cikin wani irin muryan yaudara idon ta ya canza kalla a lokacin, tana mai ce mai
Wai may yasa kake min haka ne pls ta ya zan bata time dina zuwa gare ja amma kai kullun sai ka kawo min uzurin da baikai yakawo ba,
Tana kokarin kara jawo shi zuwa gareta yai saurin karasa mikewa daga saman gadon
Yana maice mata ki tambaya kiji ni Joseph ba irin wa yan nan mazan bane da kike tsan mani,
Wanan ma da kikaga ina maki just don kada kiga kamar banda,time dinki ne,
Amma tunda kinga hakan ma bai isheki ba
Ya nakai kofa yace pls ki daina zuwa don hakan ma na itmya jamin matsala,
Mamaki da tsoro kalaman shi suka jefata ita Aisha,da mutum nawa ke kokarin kawa gareta ne yau har wani ke fada mata haka,
Inbadon tasan cewa tana moriya dashi ba ko a haka da yagane cewa tawuce wanan kalamin gareta,,,,
Bayanshi tabi da kalllo har yabar dakin cikin shirin zuwa dan motsa jiki,
Hmmm Aisha bata san waye Joseph ba da batai tunanen hakaba daga gare shi,,,,,,,




ZEEE MAKAWA
[2/20, 10:18 PM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
1⃣7⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

Alhamdullah jerabawan su maryam yafito yanzu ,yaya I,lliyasu ya samo mata guri bi karatu,a FCE kwantagora, inda zata karanta bio,chemistry,
Maryam taji dadin wanan abin so sai ba maryam ba kawai har baba
Don har gida yazo yai ma Anty Dije da mijin ta godiya akan kula mai da yar shi da,sukeyi tsakani da Allah,
Maryam wandda yanzu girma da wayo yazo mata ta roki Anty ta barta taje gurin mamanta, acan Bobi kafin ta fara karatu,
Anty bata kiya ba saida tace sai ta fadawa baba don kada, yazo yaji daga baya yai fada
Baba bai,yi fada sai fatan adawo lafiya da yai mata yabata dubu daya yace tasai masu tsaraban man shafi da sabulun, wanka,
Cikin kwana biyu akai mata yan shirye,shiryen tafiya,
Duk da bawai maryan ta saba da mamanta bane amma dai tai ta zumudin zuwa kauyen,don tagane su,,,
Ranan da zata tafi tunda safe ta hana idon ta barci don zumudi,
Har saida Anty ta kasa kan,newa tai mata, magana
Maryam wai,dama dai ashe kin dade kina son yin wanan tafin ne ko,
Yar kunya taji da kuma nauyin Anty nata, saita dan sune kanta tace ,aa anty kawai dai ina son zuwa ne inga yadda garin yake wallahi,
Har inda zata shiga mota Anty ta rakata tare da yaran su,,
Inda yaran ke kuka sai sun bi little mummy su inda zata,
Shiru take zaune cikin mota sai tunane takeyi yadda zata riski mahaifiyar ta ,
Don dai tasan cewa zaman kauye na maida mutum iri, sai tausayin mahaifiyar ta ya,kamata
Tace Allah sarki mama ita kuma nan Allah yai nufin zaman rayuwan ta,
Haka tai ta tunane azuciyar ta har suka isa garin kamfanin,Bobi, saidai tai mamakin ganin garin a saman babban titin zuwa minna da kwantagora,
Tana sauka idon wa yanda ke zaune a bakin titi yayo kanta caaaaa
Wani yaro tagani ya tafiya sai,tai mai sallama nan take tambayar shi gidan liman hamza,nan yaron yai mata kwatace akan tabi wani dan lungu, zata ga wani gida mai katon icce a kofar gidan tashiga nan ne gidan, tana bi kuwa sai gata a kofar gidan,,
Da sallamar ta tashiga mata uku tafara gani su guda tana daka guda kuma tana duke tana wanki dayar kuma tana wanke wanken kwanoni,
Duk kan su daurin zani agaba, ga yara manya da kanani nan jagwal da su, wasu majina ahanci wasu kuma kunu ya bushe masu a baki har hanci,,,
Sun karba mata sallama cikin mamare ki wace don ganin tada sukayi da kaya a tare da ita,
A cikin ladabi ta durkusa har kasa tana gaishe su ,
Abin mamaki sai ganin mata takeyi suna bulowa daga wani dan lungu, ashe ganin tsoro taiwa gidan matane, ciki fam kusan su goma,
A cikin sanyi muryan nan nata take cewa, don Allah mama Rukaiyan saleh nake nema,
Wata mata wace ke daure da wani zani blue mai photo barewa ce tace taufa gani nan,
Sai wata wace ke gefe tsaye tun shigowar shin kodai Mamuce,,
Maryam tace maryam ce sai salati suka hau alokaci guda,
Suna murna da farin cikin ganin ta, cikin sauri suka fara kwasan kayan ta zuwa ciki dashi,
Maman ta tace a kai ta, dakin abokiyar zaman ta, wace suke cewa Ladi,
Anan akai mata masauki ita, da kayanta, kafin wani lokaci har an kewaye ta da abinci kala kala,
Da yake kauye ne duk sunyi abin sanar su tasayarwa,
Kwarai mahaifiyar Maryam taji dadin ganin Maryam, da kuma wanan ziyarar da takawo masu,
Bayan kowa ya watse akabar Maryam da mahaifiyar ta, a hankali maryam ta dago kan ta takalli mahaifiyar ta wace ke tsugunne a gefen dan gadon ta,,
Tace mun samay ku lafiya mama, cikin kariyar murya take maganar kamar wacce zatai kuka alokacin,
Mahaifiyar tace takauda kukan da cewa yasu wajen yayan naki ina fatan duk kuna lafiya ?
Kikara rike yar uwar ki da amana kin daiga yadda itama tarike ki amana,
Ba maicewa ga yadda kuke da ita ,don ko da nake nan ina jin irin zaman da kukeyi da ita
Duk wani abinda ta hore ki dashi kiyi kokarin rike shi,
Allah ne kawai zai iya saka mata da alherin sa,,
Saidan hiran sauran jamar su da sukayi inda take tambayar ta ko kwana nawa zatai masu ta sheda mata sati guda zatayi ta koma,
Daga karshe ta gabatar mata da tsaraban da tazo masu dashi
Nan mama tai filla,filka da kayan saida ta,tabatar dakowa na gidan yasamu tsaraban,
Maryam taji dadin zama tare da mahaifiyar ta duk da a kauye suke sam bata nuna masu kyama ko nuna wayewa,
Dan zamanta har da karatun addini suka dan samu daga gareta,
Duk safe za,a kawo mata abin kari daga ko wani shiya nagidan hakama da rana ko dare kowa da kwanon shi da zai aiko mata,
Ana gobe zata koma har daga makwabta aka dinga kawo mata tsaraba irin na kauye,
Badon sun so ba washegari tabar su takamo hanya dawowa ita kadai,
Tunda motar ta tashi sai taji zuciyar ta duk ba dadi ya cushe mata guri guda ji take kamar kada su rabu da su,,
Hannu tas tadan share hawayen ta da taji yadan gangaro mata,
Sannu a hankali sai gasu Allah ya kawo su cikin gari lafiya,

Zaune yake a kofar gidan su Anty dije Assalam na rike a hannu shi yana yar wasan lilo da hannu Joseph din,
Mai mashin din da ta hau ne yazo har kusa da inda suke zaune,
Ido yabita dashi har lokacin da ta sauka ta mikawa mai mashin kudi,
A,lokacin mai mashin din ya sauke mata wani buhu,da ke shake da kayan tsaraba da tazo dashi,,,
Joseph ya sauke hannun Assalam a hankali shiko Assalam naganin ta yaje ya kankamay ta ya,na, ihun da murnan ganin ta,
Suna can suna murna basu san lokacin da Joseph ya dauki buhun kayan da kuma yar trolley din ta zuwa cikin gida,
Saida suka gama ihun su koda zasu diba basuga kayanta ba ,kuma basuga Joseph ba
Sai ganin shi sukayi ya na fitowa da ga cikin gida, yana kakabe hannun shi, da handcarchef, din shi,,
Da mamaki take kallon shi don sam,batai tsanmanin cewa zai iya daukar mata kaya dakamshi zuwa cikin gida
Juyawa tayi daidai lokacin da ya iso inda suke tsaye, cikin yar karamar murya tace ta gode duk da tasan cewa bawai dole bane ya amsa masu,
Tadawo da sati tafara shiga makaranta daukan lectures,
Maryam yarinyace mai hazaka ga karatu dama duk kowani famni ba,abarta a baya ba, tana kokartawa,
San,nu,a hankali kanta yafara wayewa kamar kowace budurwa da ke makarantar,
Yau ma kamar kullun shiri takeyi don gudun makara,,saboda tasan cewa suna da lecture din wani bakon malami da zai dauke su,
Gashi sun samu labarin cewa baida wasa ga aikin shi duk wanda yazo bayan shi bazai shiga ma aji ba alokacin kuma, dole kowa yasai handout din shi,
Yau har da break fast anty tayi da ita ta tsaya tasha amma maryam sauri take yi tace idan taje can zata samu dan abinda taci,
Ta dade a bakin titi kafin ta samu abin hawan da zai kaita amma sai suce bazasu je har can ba yanzu da safen nan, sai da kyat tasamu wani yace zai kaita a dari biyu tace ba komai,su tafi,,
Hakan ya jawo mata makar har time din da za,a fara lecture din yadan gwauta da minti biyu kacal,
Amma jin cewa da tayi ance baida sauki lecturer din wurin rashin nasiha,
Yasa taja baya kawai tasamu wani mota ta dan kwanta saman motar, kadan
Rayuwar ta yai matukar baci sosai da rashin samun wanan lecture din da batayi,
Tana tir da halin rashin imani,ko, nasiha nawa su, mutane,
Tsaye yake kanta yana magana amma Maryam batasan cewa, da mutum yana mata magana ba, alokacin,
Motsin da taji ne kamar kusa da ita shi yasanya ta dago kai da sauri don gani kowaye gurin,
Wani black, handsome guy ne tsaye agaban ta,sajen fuskan shi yah karawa fuskan shi wani daraje,da girmamawa,
Cikin shigar dinkin shadda yake,dinkin wanda ya tsaya mai,daidai ciyar shi sai guntun hannu, da a,kaiwa dinkin,
Yana saye da wani farin glass wanda bazata iya tamtace, ko na magani ne ko fashion ne kawai,
Duk da indon shi nada glass bai hanata,gani kwayar idon shi ba da kuma kallon mamakin da yake mata,
Batasan lokacin da taisauri ta mike ba daga kwanciyar da tai, a saman motar mutane,
Yana tsaye hannayen shi rungumay a kirjin rungumay
Ganin ta tashi yasa yai saurin kokarin wuce wa,
Saida kuma yaji ta saki wani dogon tsaki, tare da yin kwafa,
Dawowa yayi yana ce mata lafiya dai ko naganki a haka, ko kina son wani taimako ne,
Dan tsaki taja tana kokari gyara jarkar dake rataye a kafadar ta,
Wani mugun malami ne yabata min rai don yaga Allah yabashi baiwa ya,manta cewa wani dama ne ubangiji yabashi
Saiga shi ,shi yana amfani da damar yana cutawa diyan mutane, da, damar ta shi
Tadan daga kai a karo na faron tunda tafara mai magana cikin bacin rai, tace ,,
Wai ace duk samakon danayi don kada in makara, shiga,lecture din shi, saboda ance shi mugune in,,, in an, makara bai bari mutun yashiga,
Sai ga shi,,abin hawa yabani matsala wallahi,
Amma abin haushi wai minti biyu kacal na dora a saman lokacin da ya,fara lecture,
Sai,gashi wai ya rufe ba mai shiga kuma,,Abin haushi ance bai yiwa Allah don mugganci, shi,
Tun da tafara fuskan shi na a,kanta,
Fuskanshi dauke da murmushi yace too bad,
Is alright, may sunan guy din ne wai,,,
Ido ta,dan zaro waje tace kai may ye, zakai mai wa yanda ma suka dade tare dashi sun yaba shi da mugun hali ,,,
Fadamin sunan shi kawai ko zan iya taimaka maki akai,
Taidan wani far da ido taba alamar tunane, can tace,
Hmmm wai,ko A,A, MASUGA suke ce mashi ba, ko wa ma something like dat dai,
Ya na kokarin bude motar shi, yakalle ta ido cikin ido, yace mata,,
Ok ki,samay ni a block C idan kin,je office na uku daga daman ki, ,ki shi ga zaki samay ni, ciki,zan yi kokari in gani, may za,ayi akai,
Bawani jin darrr ko kuma tunane, wani abu dakaje yadawo, gareta, sai cewa tayi, to kawai ta amsa mashi alokacin, har yashiga motarshi yana kokarin tayar wa,
Sai bayan ya wuce ne tai dan ajiyan zuciya cikin bacin rai tace shikuma wanan din ma kowa ye a makarantar da zaice, zai tunkari, AA Masuga,
Tunda duk sakkon datayi tun da farar safiya ya hana yashiga ciki,
Next lecture tashige abinta batare da ta damu da zuwa gurin da ake jiranta ba,,,
Don ita a ganin ta mugun malamin ya riga ya cuce ta ko,,
Zaune yake yana aikin tura sako a cikin system

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login