Showing 123001 words to 126000 words out of 255288 words

Chapter 42 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1397

magana ba sai shiru da tai masu sai kace bada ita suke ba,
Anty dije ce tace hummmm maryam halinki sai ke wallahi,
Ba,a sukar aure fa inda ba zaka gyara ba to kayi shiru akai
Sai a,lokacin tai magana tana mai mikewa tana kakabar zanin ta da wani kyale,
Tace ai ni gaskiya na fada anty don sam ba suyi matching ba da ita,
Anty Dije wace taji haushin zancen kaunar nata tace,
Aisai ki samo mashi wace sukai machin dashi ina ga zaifi wanan jayayar taki,
Daki tashige abinta tana turo baki gaba don dai ita tafadi ba kuma yadda za,aiyi da ita,

Duk da dare ne ya,kamata a ce yai barci by now
Amma sam barci yaki zuwa mai sai ma maganar maryam dake kokarin yi mai yawo a kwakwalwan shi,
Maganar maryam din gaskiya ne duk da ya fahinci acikin gatse tai mashi su,
Amma shi kanshi yasan cewa sam basu dace ba tun farko ,
Saboda Jibrin kawai yadaure har haka tafaru a tsakanin su,
Tunda Jibrin din ya nuna yana son wanan abin shikuma bai iya,watsa mai kasa a ido,,
Juyawa yayi dayan ban garen yana mai kara rintse idanun shi stil maganar ce ke mai yawo akai,har yanzu,,,,,,,,,

πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘
Dan Allah kuyi hakkuri masu cewa wai basu gane abinda nake rubutawa, wai bani rubutu da kyau ku yi min afuwan pls banda enough time ne da zantayin editing

ZEEE. MAKAWA
[3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
5⃣2⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA,,,


Assalamu A,laikum yan uwa musulmai, fatan alheri agare ku ko dayau she,
Wanan daren Alhamis din son in amfani dashi gurin mika gaisuwata tare da fatan alheri, ga duk masoya wanan novel na furen juji da,nakeyi,
Kaunar novel din ku na nuna kaunar ku zuwa ga addinin mu ta musulunci maidaraja,
Ubangiji Allah ya kara haskaka maku rayuwan ku, Allah yakara rufa asiri nagade,,,,,,



Zaune yake saman table din dake cikin office din shi yana duban wasu takardu,
Sai laptop din shi dake a saman table din gefe guda ajiye,
Yana rike da biru sai ticking din wasu daga cikin abinda yake diba a cikin takardun yake yi,
Kada kanshi cikin mamaki yakeyi don sam bai taba tsamanin cewa abin ya kai haka ba,
Biron dake hannun shi da pepper ya aje saman table din,
Komawa yayi da sauri saman kujerar da yake zaune da farko,cikin sauri ya fara dan,na computer,
Hannun shi guda da sauri yake sarrafa computer din shi don son ya tabbatar da abin da ya ke gani, a rubuce,
Bakomai bane face zunturu tun ribar kudi da company shi ta samu,
Sau uku yana furta Subbahanallah Wallahamdullah Wa,lah,illaha,illah, Allahu Akbar,
Sai kuma yadora da fadar Hamdallah,
Komawa yayi ya dafe kanshi da hannun shi duk biyu kamar mai jin wani ciwo ko tunane,
Zubur ya mike yana mai daukar makulin motar shi,
Yanufi hanyar da zai sada shi elevator, don ya yi saurin sauka,
Tuki yakeyi a hankali sai tune yakeyi yanayi yana kallon gaban sa,
Gidan wani limamin massalacin da yake yawan bi sallah ya tsaya,
Zaune yake gaban malam cikin ladabi yakewa malam bayanin irin riban da ya samu a cikin wanan lokacin,
Saida malam yai gyaran murya sannan ya fara magana acikin kwanciyar hankali yadda Yusuf din zai fahince shi,
Komai na gamay da zakka da kuma sadaka fissabilliha malam yai mai karin haske akai,,
Godiya yaiwa malam yakawo alheri mai yawa yabawa malam din,
Bai koma office ba saboda yana da abubuwan da yake da bukatar yi kafin dare,
Ga fahintar shi ga bayanin da malam yai mai, shine, cewa zaka bayar da ita ga wanda ke a cikin bukata yafi,
Ko kuma ka taimaki wani ta yadda mai,shi zai iya mikewa,
Ba kamar yadda yaga cewa akasarin madu kudi suna rabon zakkah a yanzu ba,
Da za ace sai tallaka yabi layi adinga bawa kowa dari biyar biyar ko yan dubu guda guda,
Inda zaka ga mutane suna ta tururuwa zuwa karban zakkah gidan masu kudi,
Inda har ko kawa akeyi a gurin taron maza da mata akan zakkan naira dari biyar,

Yau kusan kwanan su biyu ba su komai da shi da ibrahim sai kasafi akan yadda ya kamata sukeyi,
Ibrahim yai mamaki kwarai ga yadda ya fahinci cewa Yusuf din yana kokarin ya kawo sallon bada zakkah shi,
Ance yawan tambaya ko sa ido yana kowa zubewar mutunci,
Don hakane Ibrahim ke yawan yin taka tsantsan ga al,amuran Yusuf daya ke gani,

Da marance ya shirya cikin shigar matafiya, inda yadauki jakar shi tankar mai tafiya,
Hanyar garin Suleja ya nufa saida yai ta yawo so sai a garin,
Inda ya kula da unguwar da yaga talkawa sunyi yawa sosai,
Wani massalaci yagani mai irin ginar laka, yadiba da kyau ya dubi yanayin gurin,
Komawa yayi yasamu wani hotel yakama don ya kwana,
Washegari tun da safe yabar wanan gari na Suleja yaiwa garin kwantagora tsinke,
Bayan tafiyar shi waye war gari sai ga jama,a dattawan unguwa sun taru suna, kallon damin kudin da aka aje a, cikin wani katon leda da akai raping din shi ,a cikin massalaci
Da farko tsoro sukaji amma daga baya sai akace kodai kudin wani matafiyi ne ya manta dasu a gurin,
Sai sukace a kirga sai asamu wanda aka ba ya kai koda banki ne ya aje masu har zuwa lokacin da mai shi zai bullo, su bashi abin shi,
Wata yar farar takarda ce tafado daga cikin ledar, da aka fara warwarewa,
ZAKKAH
A,karubuta da manyar haruffa gabadayan su sai wanan ya kalli wanan wancan ya kalli wancan, gurin yai tsit,
Mutun guda daga cikin sune yace ALLAHU AKBAR da karfi sai sauran suka karba mai,
a lokaci guda gaba dayan su,,,,
Na suka shiga yiwa mai wanan halin adu,an fatan alheri da gamawa da duniya lafiya,
A garin kwantagora ma irin haka yadiga rabawa mutane zakka batare da ansan cewa daga gurin shi bane kudin ke zuwa,
Jama,a sai zancen ake ta yadawa iri,iri, wasu harda kari sukeyi a,kai cewa, wai ai wani ne kuma sukara yawan kudin da mai shi ya samu,
Tunda yaiwa garin shigar dare baya fita ko ina don haka ba kowane yasan cewa yana garin ba,
Sai wa yan da yake sallah jam i tare da su a massalaci, suka sani,

Yau jumma,a acikin shigar farar shadda dikin tazarce, sai wata fular daya sa wa kan shi mai ruwan Assh colour,
Gidan Anty Dije ya nufa musalin sha biyun rana , ba komai ya sa shi ya nufi can ba sai dan ya dauki Assalam su tafi mosque tare,
Anty a gida ita daya sai Abubakar tai mamaki kwarai da fa ganshi a lokacin,
Baiko kai ga zama ba sai ga yaran sun shigo gida da gudun su don ganin motar uncle Yusuf a kofar gida,,
Bayan yagama rungumay yaran dake mai Oyo,yo yadan dago kai yana kallon Anty Dije,
Wace ta ke tsaye ta kura mai ido cikin mamaki take kallon shi,
Yaushe ka shigo garin nan Yusuf ?
Tambaya acikin mamaki take mashi ita shiko sai murmushi yakeyi yana kokarin cirewa Assalam bottiry din rigar shi,
Amsa yaba ta a takaice da cewa shigar dare nayi shiyasa, ban fada wakowa cewa zan shigo ba,
Dago kai yayi ya kalli Anty yace mata, Sallah Jumma,a nake son mutafi kada mu makara ,
Daga haka Anty tashiga shiriya Assalam din da,yake jirah,
Da sallamar ta tashigo gidan a gajiye don tafiyad ta kawai ya isa ya sanar da mai kallon ta cewa ta gaji,
Dakin ta, ta,fada tana kokarin cire, rolling din dake a kanta,
A hankali ta sabule abayan da ta aza saman kayan jikin ta, wanda yanzu haka nauyin shi yakai mata ko ina,
Cikin shigar da tayi tunda safe, ta,fito, tana sayen da wani shocking material, mai laushi,
Cikin kayan da yaya iliya yai mazu ne na sallah,yadin grey colour mai dan adon jan flower, cikin sa da kasan shi,
Direct gutin fridge ta nufa don ta dauki ruwan sha, kamshin da taji yasa ta dan dagowa da mamaki
Kamar tai magana ko tai tambaya saidai kuma ta shere kawai,
Sallah maryam ta gabatar tadan kai wani lokaci a zaune ta lazumi sai ta mike, inda suke aje abinci ta nufa,
Abinci ta debo a cikin plate sai kayan garnish din da ta zuba a sama,
Zaman ta yai daidai,da shigowar su gidan daga dawo,wa gurin sallah jumma,a
Gaban tane ya bada wani , sautin kara don dai gaskiya ,
A,lokaci guda suka hada ido inda yai sauri kawar da idon shi,
Amma zuciyar ta sai wani bugawa yake kamar wace taga abin tsoro, a,lokacin,
A hankali ta furta mai kalman sannu da zuwa, ta mai sune kanta kasa,batare da ta kara dagawa ba,
Cikin falo ya,shiga tare da Assalam a hannun shi sai carpet din sallah, da ya rika,
Sai bayan shigar shi ciki sanan tadan samu sukin fara cin abincin ta ,
A hankali take cin abinci amma karan plate din ta yana kaiwa a inda suke,
Anty Dije wace, ta fito tana kokarin hadawa Yusuf abinci, take,ce wa Maryam,
Nasan cewa Baba zai shigo yanzu tunda an sauko daga jumma,a
Maryam tace aikuwa tun fada nashigo nake son fada maki cewa, ashe,
Wai abokin ya din nan na kan wuri wai yasamu zakkah daga wani bawan Allah,
Wanda ba ,a san kowaye ba yai ta bi massalataiya yana bada sadaka saboda Allah da Annabi,
Anty Dije tace da, zun fa Almajirin nan ke min labari wai sun tsaya kallon wani mutum ne da ya bude gidan shi sai yaga kudi a kofa cikin ledar an rubuta Zakkah,
Yusuf wanda tunda suka fara hira yake sauraron su sai murmushi kawai yayi
A lokacin Antyn nashi ta shigo dauke da dan tiren da ta hado mai abinci aciki,
Annan take cewa muna can muna maganar wai wani ya tsunci zakkah a kofar shi ashe ma ba mutun guda bane,
Masha Allah yace alokacin da yake kokarin bude plate don zuba abinci,
Muryan Babane ke gaisawa da Maryam a kofa,
Maryam din ke cewa Baba Oyo,yo, cikin tsigar shagwaba,
Baba yace ja,ira yau ina diyan naki suke suka barki da taro,
But yaran suka fara fitowa da,gudu suna taron Baba wanda ya shigo masu da yar ledar tsaraba,
Suna karban ledar suka fara kokarin budewa maryam ce takarba don ta bude masu,
Tadan zauna saman gefen simintin su, zaman ta yai daidai da fitowar Yusuf,
Har kasa ya tsugun na kamar yadda yaga hausawa na gaida mahaifar su ya gaida Baba,
A,a to Bawan Allah ka shigo garin ne, ?
Sannu ka kaji ya aiki ya jama,a da kuma ko kari yau da kullun,
Allah yai maku albarka kaji, Allah ya taimaka ya rufa Asiri,
Ameen Ameen Yusuf ke ta fada kawai, kanshi a duke
Ita,ko Maryam sai kokatin bude ledar tsarabar baba takeyi wa yaran daje tsa, tsaye a kanta,
Dankali ne soyayye da Awara mai yaji da salad ya sayo masu, kanta aduke tace su dauko plate a sa masu,
Alokacin taji muryan Yusuf yana cewa Baba za,a kaika ka dauki photo
Ina son bana kashiga cikin masu tafiya zuwa Makkah insha Allah,
Da sauri Maryam tadago kai tana kallon shi, sai dai kwarjin shi bai bari ta kai,wani lokaci tana kallon nashi,
Baba daje a zaune bai san lokacin da yakai zaune ba a saman dan simintin da Maryam ke zaune gefe,
Yaro may kace ? inji Baba, ,,
Anty Dije tafito da goro manya farare a cikin leda tana kokarin mikawa baba,
Maryam tace, yau baba bazaici goro ba Anty don kin ga ya kasa magana,
Da kuwa ya sakar mata yana maicewa karbi nan yan nema,
Abinda Yusuf wanda ke kokarin komawa cikin falon ya fada maryam da su Assalam ke fadawa Antyn,
Da sauri ta kalli Yusuf tace O, O ni Hadiza, Yusuf ban san may zan saka maka dashi ba wallahi, aduniyar nan,
Kafin suyi magana sai muryan baba sukaji kawai yasa kuka wi,wi,
Yanata zabga addu,a acikin kukan,
Bai iya kara cewa komai ba ya mike kawai yabar gidan,
YUSUF yabi bayan shi da sauri tare da jarban goro. A hannun Anty yabishi da shi,
Nan yabar su Anty da maryam suna ta famar sadudar maganan,
Bai,wani dadewa ba yadawo tare da Assalam wanda ya,bishi da baya,
Sai a lokacin Yusuf ya dawo yadan tsaya ta waje yace tare nake son su tafi da, Baba Abdullsamad,
Insha Allah, da Ibrahim wanda zai raka su,
Ita dai Anty dije sai mamaki zancen kawai takeyi,
Ta kalli, yusuf din tace mai wallahi ban san may zance ma ba, gaskiya,
Saikuma takama hawaye kawai da dan karfi Yusuf, yace Subbahanallah,
Ganin maryam yayi tana goge fuskan ta wanda hakan yasa hankalin shi ya kada tashi,
Falo ya koma inda Anty take zaune tana faman share kwallan dake ta faman silalowa daga idon ta,
Guri ya samu yana cewa anty haba, haba dai Anty pls ki daina don girman, Allah
Yi,wa irin su Baba irin haka tankar taki ne a rayuwar mutum,saboda neman albarka duniya da lahir,



ZEEE. MAKAWA
[3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
5⃣3⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA


Masoya Novel din furen juji tare da sauran yan uwa musulmi na duniya,
Ina maku fatan alheri ga wanan safiyar jumma,an da muke a ciki,
Ya ubangiji Allah ka sada mu da alherin dake cikkn wanan ranan,
Sherin dake cikin ta ya Allah ka kare mu kaimuna tsari daga gare shi,
Allah ya karawa Annabi daraja Allah ka kara daukaka musulunci,,,,,
πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘

Gaba daya jikin Anty Dije har Baba da maryam yai sanyi saboda jin wanan albishir da Yusuf yai masu na bazata,
Anty Dije ta daga kai zuwa kallon inda Yusuf yake zaune tare da Assalam don su ci abinci,
Ta, lankwasar da murya tace Yusuf yau na rasa kalar muryan da zanyi ma godiya da shi,
Saboda ban san may zan iya furta ma akai ba, al,amarin ka na daban ne Yusuf
Shigowar ka cikin mu wani babban alheri ne atare da mu,
Gaba daya shigar ka musulunci ta zama ma duk wanda ke rabe dakai alheri,
Duk da zamanka Furen kan Juji da farko ban hango wani sheri atare da kai ba sam har izuwa yanzu da kazama wani haske a cikin al,umma,
Kafin tai magana sai ya rigata farawa da cewa, batare da ya kalle ta ba,.
Narasa albarkan mahaifina na cikina Anty may zai sa bazan bida ga bayin Alkah da suka nuna min kauna ba,
Abinda duk nakewa iyayyen mu ina masu ne saboda neman albarka acikin rayuwa,
A kullun ina rokon Alkah yasa yan uwana su gane gaskiya su,dawo cikin hanya ma,daidaiciya su ma,
Maganar shi taba kowan su tausay da yake fada inda ya ci gaba da cewa,
Abinda ke sa ako,da yaushe nake yawan zuwa nan gurin badon komai bane don in cika wani gibi dana rasa nadaga yan uwana,
Γ€nty Dije baki kyamace ni ba tun ina Joseph dina har zuwa yanzu,
May zai hana in maki duk wani abinda nasan zai iya saki a farin ciki,
A koda yaushe jinku nakeyi tankar yan uwana na ciki daya, saboda irin yadda kike min.
Yar kwalar dake shiri silalowa a idon ta tashare, da gefen hannunta,

Zaune take a bakin gadon ta tana jin lokacin da a,ke ta kiran sallah la,asar daga makwabtar unguwar su,
Amma sai taji yau takasa tashi kamar yadda ta saba yi idan taji kiran sallah,
Sai,da taji fitar su shida Assalam sanan tai yunkurin fita,
A kofa sukaci karo da Anty Dije, wace ke kokarin shiga gurin maryam din,
Suna hada ido da Anty Dije sai ta harare ta ,tace Maryam nikan ban san may Yusuf zai maki wanda har zaki iya mai godiya a duniyar nan ,,,
Nadai ga da mama bata da lafiya irin tai makon da yai muna a gidan Γ±an,
Yanzu Maryam agaban ki fa yau yaiwa baba wanan irin alherin da kowani musulmi ke fata,
Ina sauraron inji kin mai godiya amma sai naga cewa har boyewa ma kikayi don kada ku hadu,
Maryam na in,in niya tace wallahi Anty yanzu nake son in zo in mai godiya amma sai naga yafita,
Bata ce mata komai ba banda hararan da ta kara binta dashi , ta juya takoma inda ta fito,
Azaton maryam yafitane sai ta fita waje tsakar gida,
Da Yusuf suka hada ido yana zaune saman dan dakalin simitin da ke gefe yana alwala,
Idan ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login