Showing 156001 words to 159000 words out of 255288 words

Chapter 53 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1379

IDRIS MAKAWA,

IYYA,KA NA,ABBUD WA,IYYAKA, NA,STA,INN

BAZAN IYA MAN,TAWA DA KE BA YAR UWA MASOYIYA, (ANTYN NICE,)


Wanan wayar da sukayi yakawo karshen nauyi da kunyar da kowan su ke faman dako a cikin zuciyar shi,
Da sannu suka dan fara sakewa da junar su kamar yadda suke a da, indan yai waya da kowan su, zai gaisai,
Wanan shigowar ba karamin shigowa yusuf yayi ba don yashigo da shirin auren Naimat,
Sosai jama,a ke murna da zuwan shi saboda irin yadda mutane ke a cikin matsuwa,
Baida wani hutu atare da shi kasan cewar shine uban amarya da ango gaba daya,
Gida na musan man ya sai masu inda ya mallakawa Ibrahim shi a kyata,
Anty Dije ita ce uwar amarya don itace komai na amarya,
Sosai take gyaran amarya irin gyaran mutanen kasar kwantagora na asali bawai na zamani ba,
Don ita da kanta tasa a samo mata ganye don yin hadin da kanta,
Kamar yadda ko wace amarya yar asali take zama yayin zaman lalai haka itama Naimat ta koma inda tasha wankan lalai da turare sai sheki takeyi,
Su maryam da safiya da wata sister din mijin anty sune a matsayin abokan amarya,,
Sai zirga zirga sukeyi akan duk wani abin da ya dace suyi,
Shigar wasu shadda maryam tayi masu ruwan pink colour,
Sai wani farin lece da akai mai ado dashi kamar flower,
Farin gyale ne tadan yafa a kan,ta da takalmi farare masu dan tsini a baya,
Daga gurin sayen kayan da zasu rabawa friends din su da suka gaiyata suke tare da safiya amma safiya tadan tsaya sayen wasu kayan
A gajiye ta shigo falon hankalin ta a kwance tana mai cewa wassshhh wallahi anty nagaji ga mai manshin din da na hau yana ta tsula gudu da,,,,,
Makalewa maganar tai mata don ganin Yusuf wanda ke zaune,a falon su biyu zaune shi da Anty Dije
Sam bata tsan manci ganin shi ba a folon don motar shi bata gurin balle tagane cewa yana cikin gidan
Daganin ya na yin zaman su ,kasan cewa magana sukeyi mai muhinman ci ,
A tsakanin su don Naimat ma bata gurin alokacin,
Tun bayan wancan rikicin, sai yau sukayi ido biyu da junar su shi, da ita,
Kamar ta juya baya ta koma amma sai ta daure, kawai tasa kai ta shiga,
A sanyaye ta yi sallama ta shigo falon idanun ta sunyi, wani lub da su saboda kwaliyar da tayi,
Fuskanta babu yabo babu fallasa, ta,gaishe su a cikin girmamawa,
Yusuf ne ke cewa daga ina take haka take cewa ana gudu da ita a mashin,
Maryam ba kyaji ko ?
Har yanzu baki bar hawan mashin ba ko a dinga wulwulaku a titi,
Yakarasa zancen shi a cikin nuna bacin rai
Juyawa yayi inda anty take yana mai facing din ta ya ce,
Anty ku koyi tukin mota mana pls a , aje maku mota a gida yafi hakan ?
Dariya ma maganar shi ya ba Anty a lokacin irin yadda ya hakikance yana faman fada,
To Yusuf in banda abinka abinda mutum bai,dashi ai sai ya yi hakkuri,
Maryam na jin yadda yake ta faman sababi sai kawai ta juya, zuwa dakin su,
Duk sauran zancen da sukeyi a kai maryam wace ke ta ciki tana jin su duk ranta abace,
Don dai ko A,A wanda zai aure ta ai ba zai zake yana mata irin wanan masifan ba,
Shigowar safiya a dakin ita agajiye yasa ta dan sakewa ta daina kumburin da takeyi,
Sosai suka baje kayan da suka sayo don na su irin sha,anin suna dibawa, gaba dayan su har anty,
Muryan Anty ce maryam taji tana kiran ta bayan sun gama kallon kayan da arranging din komai,
Da sauri maryam din tace naam Anty,
Bata kara cewa komai ba sai kuma tai shiru tana mai kurawa kaunar naya ido,
Kamar mai tunanen wani abu can sai tace, wa maryam din,
May yasa dazun Yusuf yana maki fadan hawa mashin kika wuce ki ka barshi batare da kin tsaya ba,
Wani irin tsoro ne ya lullube maryam din don jin an anbaci sunan Yusuf wai kuma tai mashi laifi,
A hankali maryam ta janye hannunta asaman wani kwalin sweet da tadora akai,
Kanta ta dukar kasa tana dan wasa da yatsun ta a saman ties,
Karo na biyu takara kiran su nan ta tace, kina jina kuwa,
Maryam sam bana son ki nunawa Yusuf wani mugun tsana wanda har zai zaci ko kyamar,shi kike ji kamar yadda yake zato,
Dan juyawa Anty ta yi inda Safiya take tana mai,cewa don Allah dai safiya idan mutum,
Ya nuna cewa ya damu da kai a matsayin dan uwa ko kuma wani nashi can,?
May ya kamata kai kayi mashi a lokacin,
Safiya tace kai ma kabashi kulawa mana fiye da yadda ya nuna ma,
Masha Allah, inji Anty amma ita kinga sam bata gane hakan ba a rayuwar ta,
Kin gani yadda ki kayi dazun sam wallahi bai yi daidai ba
Hakan zai iya fusata shi yadauki zancen da baba yayi akan ku bilhakki da gaskiya,
Kin ko san cewa baba zai iya yin komai ba tare da amincewar ki ba,
Tagumi maryam tayi tana sauraron Antyn nata acikin natsuwa,
Inda Anty da safiya sukaci gaba da kawo mata musalai kala,kala akan zama da mutane
A sake murya a raunane tace yanzu yaya zanyi anty in kaucewa gudun magana,
?
Abinda anty ke son ji ke nan dama sai tadan gyara zaman ta tace,
Ki nuna mai cewa ke yanzu baki da dan uwan da ya wuce shi,
Shawaran ki, ki dinga sanar da shi don jin ra,ayin shi
Kissa dai irin ta mata zaki dinga gwada mai tankar ba komai a tare da zuciyar ki,
Kinga koda baba zai kara waiwayan zance shi Yusuf din da kanshi zai nuna wa baba rashin dacewar hakan a tsakanin ku,
Cikin sauri maryam ta daga kai takalli anty dije tace,
Amma anty baki ganin idan baba yaga haka zai zaci cewa ko na yarda ne,
Murmushi anty dije takarayi tace, ai shi Yusuf din sam bazai yarda har hakan yafaru ba,
Ke wayo fa za muimasu shi da baba din , ke dai iyaka kiyi kokarin nuna mai cewa ba komai na jin kyama a tsakanin ku,
A sanyaye maryam tai ajiyan zuciya tace nagode anty,
Wallahi har naji wani sanyi a zuciya ta
Anan sukaci gaba da hiran duniya saiko ga Naimat wace ta shiga family house din su mijin Anty ta shigo gida,
Duk hiran da sukeyi ita maryam hankalinta na can tana tunanen yadda zata fara bullowa Yusuf din,,,

Zaune take saman kujera mai zaman mutun biyu,
Hannunta rike da waya tana cewa safiya tazo mata da, wani mango drink datake yawan son sha,
Safiyan na cewa ita bazata koma baya ba tunda ta wuto gurin ko,
Tsuki taja tana cewa macuyiya don kawai kimin keta kin san ban shan duk irin da kika,sayo zaki ce bazaki sayo min ba,
Muryan shi taji daidai saitin bayan ta yana cewa kedawa ke fada haka maryam ?
Da sauri ta juya bayanta cikin dan tsorata don sam batasan ya shigo gidan ba a lokacin,
Bayan ta ta juya sai ta gan shi tsaye cikin wasu kaya masu shigen na indiyan musulmai,
Maganar su Anty Dije ne yafado mata arai cikin dan kankanin lokaci
Sai cewa tayi cikin dan wani murya kamar mai shagwaba,
Wallahi yaya safiya ce muguwa Anty ta aiketa sayen drink shine nace mata, tasayo min irin wanda nake so
Amma wai sai ce min tayi wai ita ai ta riga tabar shagon sayarwa ko kuma bazata koma ba,
A hankalo ya isa gurin dayan kujerar dake facin din wanda take zaune akai,
Cikin mamakin yadda yau ta sake jiki tana mai magana cikin mutunci da nuna kulawa,
A dan matse fuska yace ina Assalam da Issi suzo mutafi in kai ku ku sayo,
Wani iri maryam taji a cikin ranta na yadda zasu fita a tare gudun kada wani ya gan su ya zaci wani abu,
Amma sai gargadin Anty Dije da Safiya ya fado mata a rai,
Murmushi tayi a fili tace uncle kada na wahal da kai da abarshi kawai zai fi,
Kallo mai kamar harara yai mata yace ku sa may ni a mota pls
Kanta kawai ta gyada alamar to,
English wear ke ta cikin jikin ta don haka sai ta dauko wani katon hijab din ta , ta feshe shi tsab da kamshi ta zumbuda saman kayan nata,
Da ita da yaran suka fita bayan ta shedawa anty inda zasu da uncle din,
A can dan nisa kadan da kofar gidan ya parker motar shi,
Wata bakar Jeep ce mai kama da wani siffan abin ruwa,
Da karasowan su ya bude motar ta yadda zasu shiga ciki dukkan su,
Assalam wanda yasaba idan zasu fita ya shige gaba tare da shi
Yanzun ma kokarin shiga gaban motar yaron kayi
Amma sai Yusuf din yake ce mai, ya koma baya tare da Issi su zauna yabarwa little Mum gaba,
Suna barin gurin anty dije wace ke tsaye bayan labule tana leken su tai wani yar ajiyar zuciya,
Kira,an shek Ahmad suleman kano ke tashi a cikjn motar a cikin surar Al,imran ,
Maryam din wace itama bin karatun takeyi a hankali,
Inda Yusuf din ke ta sharara gudu a saman titin,
Cikin yan mintina kadan sai gasu a bakin wani store wanda akai wa rubutu da manyan haruffa 212 plaza,
Shagon yakai shago a wurin girma don haka suna tsayawa a wanan store din,
Maryam ta daga kai tun shigowar su motar,ta kalle shi,
Yagane may take nufi don haka yadan juya inda su Assalam suke ya ce,
Mufita mu zagaya kowa ya dauki abinda yake so kunji,
Cikkn zumudi suka firfito zuwa cikkn shagon inda yake rike da hannayen yaran,
Itama maryam din dole tabi bayan su badon ranta yaso ba,
Sosai suke ta sayayyan su shi da yaran inda yake biye wa duk wani shirmay nasu yana taya su jidan kayan da suke so, agurin,
A, baya baya maryam ke bin su wace har zuwa yanzu ko tsinke bata dauka ba,
Ganim bata da niyar zuwa yin abinda ya kawo su yasa shi ce mata,
Kinfasa sayen drinks din ne ko ?
Kai ta gyada mai alamar ,a,a don haka atare gaba dayan su suka tafi gurin,fani abin shaye shaye da yan tonde, tonde,
Sai kuma ya wuce zuwa gurin su man gyaran gashi da kayan kamshi dana wanka,
Juyowa yayi inda take yace sun ishe, ki ko a kara wasu,
Da sauri maryam ta kada kai alamar sun isheta,
Gurin biyan kudaden kayan da suka lodo ya nufa inda yabiya su makudan kudi a ka kai masu har cikin motar su,
Wanan karon a hankali yake tafiya ba kamar lokacin da zasu zo ba,
Sai can daga bisani ya dan karkato kanshi inda take yace,
Maryam ina saurayin ki naga tun da nazo ban gan shi yazo ba,
Kamar maganar bai soke ta ba tace, kai yaya Yusuf, har da yar kaunar taka kakesawa ido,
Surukin kane fa , yaya yusuf takare zancen a cikin zolaya,
Tsaki ya ja yana mai yar hararan ta yace, Allah dai ya kiyaye ni surikina mai mutunci ne,
Duk da ansar ya bata mata rai amma sai ta cije tace mai cikin dan sasauta murya,
Kai ya Yusuf duk wanan biyayya da girmamawan da yake maka, zakace mai hakan ?
Tsuki yaja cikin dan sasauta murya, yace, to be Frank maryam wanan guy din wallahi bai dace dake ba sam,
Gaban tane ya fafi dammm saboda jin abin da yace,
Muryan yaran dake bayane suna kokarin bude wani kwalin biscuit sai fada ga kaure a tsakanin su,
Sosai yanzu ya lula a saman titin cikin yan mintina ya iso kofar gidan nasu
Tun daga nesa kafin su karasa kofan gidan maryam ta hango motar A,A a tsaye amma yana acikk zaune,
Gab da motar shi uncle ya tsaya da tashi motar a gefe guda,
Cikin kidimaywa da nuna tsoro maryam ta bakina rawa take cewa malam tun yaushe kazo, shine baka kirani ba,
Hararanta yayi cikin daure fuska yace daga motar wa kike maryam,
A lokacin Yusuf dake kokarin kwasan kayan da suka,sayo yana jin su,
Dukar da kan ta tayi kasa tai shiru, sai daya kara dan dago fuskan shi acikin bacin rai yace,
Maryam ban fa fahince ki ba tambayar ki nakeyi fa,
Cikin gagawa yake azaman bude kofar motar shi,
Ya nunata da yatsan shi yace kada ki raina min wayo ki mai da i ban san abinda nakeyi ba fa pls
Nan da nan idon shi ya canza yai wani jajajir tsatsan bacin rai duk ya baiyana a fuskan shi,
Sosai rayuwan ta yai mata daci akan irin yadda yake mata agaban mutane,
Idanu a runtse tana jin wani irin zafi da bacin rai tace,
Dakata malam kadaina fada min irin wanan kalaman,kamar wata yar cikin ka,,,
Cike da mamaki A,A ya ware ido yake kallon ta don ta bashi mamaki irin yadda tarufe ido tana bashi ansa,
Juyawa tayi kawai zuwa cikin gida batare da takara koda second a gurin ba,,,,,



SEENABU MAKAWA,,
H🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
6⃣5⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA


IYAKA, NA,ABBUDU WA,IYAKKA NAS,TA INN,,,


Har kulun addu,a na,gare ku da fatan alheri ga duk masoya novel din furen juji, Allah yasa a gama da duniya lafiya Allah,sa mu, dace da rahaman Ubangijin mu,,,,
πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘


Shigowar Maryam ya yi dai dai da fitan Yusuf da ga cikin gidan,
Dan gefe ta samu ta dan bashi hanya, tankar baisan cewa da ita a gurin ba ya sa kai zuwa waje abinshi batare da ya ko kalle ta ba,
Duk da rayuwan Maryam bai mata dadi ba soboda irn yadda ya nuna mata,
A kofar, gida Yusuf ya hango motar Yusuf din yana kokarin barin unguwar,
Sau,guda yadan kalli gefen da ya hango motar A ,A din yai wani saurin kauda kan shi, batare tankar A,A yasan da shi a gurin,
Sai bayan yaga shigewar shi daga kwanar
Yai wani irin dogon tsuki kamar wanda ya ga wani abin ki, ko tsana,

A hankali Maryam, takarasa shiga cikin gidan nasu inda ta,samu Anty Dije wace, ke zaune da yaranta duk sun zagaye ta,suna son a bude ledar da sweet din su ke a ciki don su sha,
Jiki kamar mai jin kasala ta zube a saman wani kujera da gefen wanda yar ta ke zaune a kai
Anty Dije ta dogo kai a hankali ta kalle ta nan take ta fahinci kaunar nata na a cikin yanayi,
Gaban ta ya ba da sautin faduwar gaba tana tunanen indai ba wani abin bane ya hada maryam din da Yusuf din ta,
Amma to ai shi Yusuf lafiya ya bar su yan inda ma yake sheda masu tana waje tukun,
Sai kawai tai saurin kawar da wanan zarkin da zuciyar ta ke kokarin fada mata,
Ledojin da yaran ke ta kokarin son ta bude tace wa Assalam ya kwasa ya kai wa maryam,
Muryan Sadiya,ce ta suka ji a bayan su tana cewa
"Eh" an dawo bari muga abinda aka siyo ma, manyan mata,
Sai a lokacin maryam ta maka mata wata hararn "mind you, a cikin wasa,
Sadiya din ce takaraso gurin itace ta karbi ledan tafara budewa,
Kayan da ta gani fam a ciki da kuma Price's din su ya sa tai saurin dago kai ta kalli inda maryam take zaune,
Maryam wacce hankalin ta,bai gurin a lokacin tana kokarin diban wayar da taji sako ya shigo,
Muryan sadiya ce, dake kokarin cewa maryam ki ce barna kikayo wa Bros yau,
Sai a lokacin idon maryam ya kai a kayan da Sadiya ta zazzage a saman ties kasa,
Ba karamin kaduwa tayi ba don ganin irin yawan kayan da Sadiya ta ware cewa, duk nata ne,
Baki ta bude da niyar za tai magana sai kuma maganar ta makale mata yakasa fitowa,
Guda guda ta dinga bin kayan da kallon har idon ta ya sauka asaman wani dan kit, mai adon ruwan silver,
Rashin sani ko may ye a cikin wanan kwalin yasa ta tambaya Sadiya da cewa may ye a cikin kwalin,
A hankali sadiya ta bude kwalin wasu set din turare ne kusan kala hudu a ciki, amma duk na desame product,
Sai su man shafi masu kyauda da,tsada, kafin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login