Showing 45001 words to 48000 words out of 255288 words

Chapter 16 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1350

kyau, don wata rana zasu iya canza ka Joseph,,
Sai kuma inda Mr Ema ke cewa kadaina yawo da yaran hausaw don basu da tabbas,
Cikin wani irin yanayi ya aje wayan kamar mai tsoron wayar, na shi alokacin,,,
Da kyat ya iya mikewa zuwa cikin bedroom din shi jikin shi,duk ba kwari,
Duk da ya kwanta da ya runtse idon shi ba abinda yake gani sai wanan sakon na wayar shi,
Come to the light of life, islam,,,
Rintse idon shi ya karayi kamar wanda bai son tunawa da sakon,
,,,,,,
Maryam wace ke zaune bakin dan matsakaicin gadon su ita da Issalam,
Takai wani lokaci tana jiran replay din shi saidai taji shiru ba wani alamar da wani sako tafe,
Haka ta hakkure ta kwanta tare da tunane kasadar da tayi na tura mai wanan irin sakon duk da tasan cewa ba wai zai gane cewa ita bace,
Amma dai tasan cewa kasada ne haka din, don ina ruwan ta da addinin shi,
Tsuki tayi gami da juyawa tana may ganin laifin kanta, dayin katsalandar da shiga harkan da ba nataba,
Sim din tacire a hankali ta samu wani guri inda tasan cewa, ba mai taba ganin shi gurin, taboye
A hankali taja bargon ta dake gefe aje, tai rufe jikinta da shi ta,na mai lumshe idon ta,
Sai dai sam barci yaki daukar ta don tana tunane akan sakon da ta tura,
May ye,wai, amfani abokan shi su jibrin da KB da bazasu iya fadakar da shi gaskiya ba,
Tsuki tayi gami da kara juyawa ta wani gefe tanamai cewa
Ina zasu iya fada mai gaskiya tunda suna samu kudin agurin shi a kai a kai,
Wai may yasa mutane kudi ya rufe masu ido ne haka da yawa,
Kudiba fa, ba kunya yadda suke rawan kafa akan ARNE, wanda suke darajawa da kiman,tawa saboda kudi,,,
Shin wai basu san cewa shi kanshi yasan cewa sun fi shi daraja ba da kima mutunci, saboda hasken addinin su, yafi na shi,,,,
Amma saboda kwadayi duk sun zubar da damar tasu,
Kara jan bargon ta tayi ta lullube lif daga haka barci mai nauyi ya dauke ta, zuwa wata, nahiyar,,,,,

A,A masuga ne zaune a office din shi yai tagumi da hannun shi, guda ,
Ba komai yake tunane ba sai wanan yariyar da yafara ji a, cikin zuciyar shi,
Watau Maryam wace duk wani tsari da kuma diri da yake bukata ga mace tana dasu,,
Kafin ya kai karshen tunanen shi yaji an turo kofan office din nashi,
A hankali yadago kai da idon shi da suka dan sauya yanayi yana mai kallon kofar ,
Da sallamar ta ta,shigo office din cikin shigar atamfa, da dan hijabin ta mai kara mata kyau ko yaushe,
A nutse take kamar kullun yau madai kamar ba sabo a tsakanin su har yanzu,
A mutunce ta dan durkusa ta gaishe shi, sannan ta dan samu kujera guda ta zauna,
Sai a lokacin A,A yadago ido ya zuba mata su kamar na yan mintina,
A kunyace maryam ta kauda kanta daga kallon shi, saboda bazata iya jure kallon namiji ido da ido ba,
Yar murmushi yayi har fararen hakoran shi suka dan baiyana fili,
Magana yake yi mai kama da rada,maryam kina kokarin ki min illa a wani part na jikina,
Cikin dan razana da dago idon ta,akaro nabiyu suka kara yin arba da juna,
A,A yace yes, ba wai, ba gaskiya ce nafada, saboda duk second ina ganin ki a zuciya ta Maryam
Cikin mamaki maryam tace mai malam ni kuma ? ta fadi cikin sanyin murya,,
Kai yakada mata a hankali, yace akwai wata maryam ne nan a tare da ni,
Ido ta dan kura mai sai kuma tai saurin kawar wa , azuciyar tako tace ban taba tsan manin cuta da ga gare ka ba malam,
Ansar da yaba tane yasa ta gane cewa zancen zuci ya fito fili,
Don ji tayi yace har abinda yafi haka zaki iya ji daga gare ni ai,
Zan cena sam babu maganar cuta ko yaudara acikin ta,
Gaba daya suka kurawa juna ido cikin dan mintina,
Maryam ce tai saurin kawar da na ta idon again
Saboda in badon a zaune take ba da zata iya faduwa don kaduwa,
Sannu a hankali A,A masuga yaciga bada kafa gwaunatin shi a zuciyar maryam,
Cikin jin kunya da kuma nauyi Maryam tai mai sallama daniyar wucewa yau ita kadai,, don dai wani irin nauyin malam din take ji yau,,,,
Tafe suke ya na,takara kafa gwaunatin shi gare ta, ita ko har yanzu ta kasa gaskan ta zancen nashi a cikin ranta,,,,


ZEEE. MAKAWA
[2/20, 10:28 PM] β€ͺ+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
2⃣0⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA

Masoya novel din furen juji ina maku fatan alheri aduk inda kuke ina kara maku fatan gamawa da duniya lafiya ,
Rahama ,daukaka azurta,dacewa da alheri ubanginji Allah ya hada ku dashi,
Don nasan cewa bawai novel din kuke kauna ba kishin addinin mu ta isalama yasa kuke kaunar novel din, fatan alheri gare ku ko yau sheπŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘



Tsaye yake a cikin dakin shi yana daura agogon a hannun shi wanda ke mai masifar kyau aduk lokacin da ya makala agogo a hannun shi,
Jerked din shi yadan aza saman wuyan shi, hannun shiguda ya rarimi yar Case din shi, da ita,
A cikin sauri yake kokarin yin komai hakan kawai zai sa mutum yagane cewa yana da wani abu mai muhinmanci yau agaban shi,
Da dan sauri sauri yake saukowa daga step din yana kokarin gyara tie din dake makale a wuyar shi,
Tun bai karasa sauko wa ba Ejoma dake tsaye a bakin dinning table take mai wani irin kallo,
Kofa yanufa don yau baiko tsaya zuwa gurin kakar shi ba,
Brother, abinda Ejoma ta furta ke nan kamar yadda take kiran shi, where, are u going
Your break fast is ready now,
Tafada cikin yar shagwaba kamar yadda yan kabilar su keyi wa yayyen su,
Dan tsayawa yayi, cak, Agogon shi yadiba ya dan ya mutsa fuskan shi kadan yace mata,
Cikin dan sakin fuska sorry sister, i don't have time for dat pls,,
Kai Ejoma ta kara dan langabewa tadauki cup tea ta,nufi inda yake tsaye har a lokacin yana kokarin gyara nicktie, din shi,
Cup din tea din dake hannun ta tamika, mai tana cewa brother i beg drink dis ,even small now,
O my god, Ejoma iam telling ,u now, dat iam, late,
Ba yadda ya ita dole ya karba ya dan kurba tsa,tsaye, kadan kadan,
Yamika mata cup din cikin sauri yabar falon don gudun kada Ejoma ta jawo mai wata matsalar kuma
Yana fita Ejoma dake tsaye tadan bi bayan shi da kallo tana dan girgiza kanta,, Busy man ta furta,
Ba laifi don yasa bakin nasu basu karaso ba, gurin da za ai taron,
Wasu yan kasan Cameron da Guinea ne zasuyi wani dan meetings da su ta yadda zasu dinga tura masu mai acikin farashi mai sauki,
Sai kuma kada watau ( Cotton) zasu yi harkan business din shi dasu,
Sosai Joseph din ke jin dadin meeting din tare da bakin nasu saboda akwai abubuwan da ya fahinta so sai a fan,nin kasashen biyu,,,
Tsawon wani lokaci suna wanan, taron har zuwa daidai da lokacin sallah a zuhur,
Kawai sai mutum guda daga cikin su baki,ne so sai wulk da shi,wanda ke cikin shigar bakaken coth
Tare da wani daya wanda shiko wasu kanan kaya yasa sun bala,in yi mashi kyau sosai,
Mutumin farkon ne yafara daga hannun shi yadan kalli agogon hannu, wanda ke nuna karfe, daya da wani abu na rana,
Mikewa yayi zubur yana mai ce ma sauran abokan meeting din I want to pray,
Joseph da a,lokacin yake kokarin diba wasu takardun dake a gaban shi yai sauri daga kai ya kalli mutumin
Wanda shi azaton shi tun farkon shigowar su yadauka dan bishon ne,
Wai a,she muslumi ne, diban shi yakara konawa ga gudan da ke kojarin sance agogon hannun shi
Kamar yadda yaga su KB na yawan yi idan zasu yi, alwala,
Duk a cikin mamaki yadinga kallon su a zuciyar shi kuma cewa yayi,
Ashe shi musulumi bawai dole ta kam ki wani hali zaka iya sheda shi ba ke nan kamar yadda yaga sauran, musullumai suna rike tasbaha ko kuma rawani ko sa tufafi mai nuna sheda,
Kafin ya farga yana a cikin tunanen sai gani wa yan nan biyu dake gefen shi sun mike suma zuwa yin sallah,
Ya kai wani lokaci yana ta al,ajabin wanan abin da yagani a tare da wa yan nan baki nasu, sosai,
Wayar shi tai kara don haka yafita tadan waje kadan daga dakin taron,don,yar karba call din,
Abakin wani daki dake gefen inda,suke taron yaga takalma mutane agurin,
Sautin ladani sallah yaji har inda yake yana fadar Allahu,Akbar, Sami,al,llahu limal,hamd
Kamar ance ya waiga hango su yayi still suna cikin shigar tufafin da Joseph ke tunanen zasu hanasu yin sallah,
Can karshe yanufa ya ci gaba da maganar da yake yi,
Har zuwa dawowar shi sun rarage sallah sun idar suna zaune suna lazimi,
Ya zauna bada wani jimawa ba saiga su Aoudullah sun shigo duk kan su fuskan su cikin fara,a,
Nan suka fara mikawa mutane hannu suna musabi,a da duk wanda ke gurin,
Sau guda yadan daga kai ya kalle su yai saurin kawar da kan shi,
Sai dai haka kawai ya kalli yan uwan shi Christian dake ta harkokin su cikin rashin damuwa,,,,,,

A gajiye tafito daga dakin daukar lectures din din su yar jakar ta na sabale a kafadar ta,
Tasan cewa A,A yana aji a lokacin don haka bata wahal da rayuwar ta zuwa office din shi,
Saboda yanzu ma duk ta rage yawan zuwa gurin shi don guje wa shedan,
A,kwai wani dan korido wanda zai sadaka da wata department namasu yin computer science,
Iccen da ke gurin andan kawata shi da wasu kuherun kasa da akayi wa farin penti,
Can ta nufa da niyar zuwa ta zauna, kafin lokacin shigar ta lecture yayi,
Wata matashiryar buduwar ce zata dan girmay ma maryam kadan,
Zaune take ta hada kai da gwiwa alamar a cikin tashin hankali ,take,don tayi zaune tayi tagumi,
Gefen ta maryam ta zauna tare da fadin Bissimillahi,
Hannu tasa acikin yar jakar ta tadauko wani dan bunch din digestive, biscuit, da wani dan lemon kwali,
Gefen da yariyar data tarar a zaune tadan kalla karo na farko tunzuwan ta tazauna gurin,
Mikawa yarinyar ledar biscuit din tayi tana mai mata Bissimillah,
A hankali yariyar tadaga kai da idon ta da sukayi jawur, a lokacin, ta,dan girgiza wa Maryam kai alamar a,a, tafurta nagode,
Sau guda maryam ta dan tauna biscuit din sai taji kawai bataji dadin yadda ta lura da cewa yarinyar na kokarin share hawayen ta da gefen gyalenta,
Lafiya dai ko Maryam tai katsalandar din tambayar yarinyar,
Wani kuka tasake lokaci guda tace wallahi yar uwa matsalar malam nan ne ke damuna ace mutane yan uwanka musullumai su dinga maka sheri,
A hankali Maryam ta aje kwalin lemon da tafara dan zuka a lokacin ta mai da hanjalinta gun yarinyar,
Yarinyar tace ni sabuwar zuwa ce a wanan school din, gashi na kusa kamalla duk wani abin da yakamata inyi amma gashi HOD din mu yaki samun hannu a takarda na wai bai yarda da results dina ba,
Wani irin mugun tausayi yarinyar taba Maryam jin bakinta kawai tayi yana tambayar yarinyar wani department ne,
Tace computer science, zubur Maryam ta mike ta kokarin gyara gyalen da tai rolling din kanta dashi,
Shigar shi office ke nan yana kokarin dauko ruwa acikin dan karamin Fridge din dake office din,
Da sallamar ta shigo office din sam bai zaci zuwanta yanzu ba don yasan cewa sai ta gama abin da takeyi takan zo su wuce gida, watarana ma sam baya ganin ta saidai suyi tayin waya,
Ganin ta yanzu yasa yasan da matsala fuskanta ya dan kalla yaga damuwa fal acikinta,
Daidai lokacin da yake zama yake cewa lafiya kuwa Maryam,
Ido tadan tsura mai yau babu ko kiftawa, yai mamakin hakan sosai a, ranshi don yasan cewa ba halinta bane hakan,
Zai yi magana sai yaji muryan tana cikin rauni tana magana,a hankali,
Malam banaso sam, sunan ka, ya dinga fitowa daga cikin azzaluman malam makarantar nan,
Masu kokarin kayarda ditan mutane, daga cigaban su,
Kafin taci gaba yadaga mata hannu alamar ta tsayar da zancen ta hakana,
Cikin mamaki yake tambayar ta komay ke faruwa da har tazo mai a haka,?
Nan ta kwashe yarda sukayi da wanan yariyar ta fada mai,
A, cikin mamaki yake tambayar cewa yaushe akai haka da shi,sam bai ma san zancen ba
Can yace ina ita yarinya tana daga waje inji Maryam,
Da sallama maryam suka dawo tare da wanan yarinya,,,
Cikin ladabi tagaida malam din wanda ke dan rubutu a wani dan pepper,,
Yadago kai yakali inda suke yana mai mika mata hannu alamar takawo takardun ta, dake hannun ta,
Ba,bata lokaci taciro su daga cikin handabag din ta, ta mika mashi su, jiki na rawa, kamar zata fadi don tsoro,
Tai mamaki kwarai da taga yasa mata hannu batare da bata lokacin komai ba cikin yan mintuna
Ita ko yanzu kusan wata daya da rabi ke nan tana ta faman bin, ai, mata wanan aikin abu ya faskara,
Sai gashi yau Allah yakawo mata shi a cikin sauki ta samu an mata,
Yana gamawa yadago ido ya kalli yariyar yace mata kin taba gani na akan wanan takardan,
Tace duk lokacin da nazo sai messenger ya ce min baka nan komaya yace ance bazan samu ba karshe ma sai ce min yayi ance takarduna basa yi wai,,,,,,

Bayan fitowar su ne wanan yariyar ta rungumay Maryam tsam a jikin ta tana ta zuba godiya anan take sheda mata cewa sunan ta Safiya,
Tundaga wanan ranan suka kulla friendship mai Γ karfi a tsakanin su har takai in har guda baiga guda ba, bai jin dadi,
Yau tsawon kwana biyu kenan Safiya bata shigo makaranta ba,
Don haka Maryam tashiga cikin damuwa sosai,
Nobar wayan ta takira wanda kwana biyu kenan nobar bata shiga koda takira sai ace is switch off,
Yau kira guda Allah yasa nobar yashiga, batare da wani bata lokaci ba aka dauka a dayan bangaren,
Nan take jin cewa ai safiya mahaifiyar tace bata da lafiya suna asibiti da ita,
Maryam taima safiya alkawarin zuwa dubata, insha Allah,
Sukayi sallama tare da aje wayan cikin nuna tausayi,
Maryam ta fadawa Anty abinda yasamu mahaifiyar safiya,da ke asibiti kwance,
Itama dai anty ta tausayawa safiya da mahaifiyar ta,
Cikin wata raunaniyar murya tace wa anty idan tasamu time weekend zata tafi ta dibo maralafiyan,
Anty Dije tace Allah yasa don dai ke ce da kanki kikayi wanan alkawarin don nasan cewa bazaki tafi ba,
Cikin dan marairaice murya, Maryam tace, insha,Allah zan kokarta in tafi, ai saboda safiya nada kokari wlh,,
Da dare suna zaune a harabar tsakar gidan su suna shan iska
Saboda dauke wutan neper da akayi yau garin yai zafi,
Sallama suka akofar shigowa gida, Maryam wace ke kwance saman wata tabar roba da suka baza tana karatu don tana da test a cikin satin nan,,,,
Cikin mamaki gaba dayan su suke cewa muryan baba ne fa,
Cikin farin cike duk suka mike suna tariyan shi,
Wani tabarma aka dauko wa baba yazauna tare da jawo Isslam da Assalam zuwa jikin shi,,,
Sun gaisa sosai da baba sai shiru yadan biyo baya,
Baba yace wa Anty Dije yazo ne yadibi lafiyan su, da kuma zancen maryam,
Maryam wace ke zaune gefe guda gaban ta yaba da damm,
Nan baba yake tambayar Anty may ake ciki ne da zancen
Anty Dije wace ke dan gefe tsugunne tadan kara gyara zaman ta tace wa baba,
Baba maryam fa karatu takeyi yanzu dan Allah ba ba kayi hakkuri har tadan karasa sai ai zancen auren ta,
Baba ya ce, a,a Dije banaki tanaki bane saidai kin san cewa yanzu mutane ba sui ma baya,
Kin,ga gara tun inada rai muyi mata aure kada in mutu in barki da nauyi ke kadai,
Maganar taso taba anty Dije dariya sai dai ta yar murmusa kawai tace
Insha Allah baba kana da rai maryam zatayi aure kuma kaida kanka zaka aurar da abinka,
Amma zancen cewa zaka tallafa min sa abinda zan aurar da ita don Allah

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login