Showing 204001 words to 207000 words out of 255288 words

Chapter 69 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1396

mai son gano wani abu a cikin dakin,
A gaskiya yana son musuluntar Sonny do min wani babban jahadi ne a gare shi,
To kuma ya zaiyi da dakon son maryam da yakeji tun tana yar ficiciyar ta,,
Wanda sai a yanzu ne ya gane cewa So ne yake mata shi yasa yake kin duk wani al,amari na,ta a wancan lokacin,,
Idon shi yadago ya bude inda yaci gaba da nazarin shi akan abinda ke damun shi,
Ya san halin Sonny sosai yana daga cikkin ire iren mutane yan son rayuwa wa yanda sam sukan manta da akwai mutuwa,
Gashi kuma matashi ajin farko masu fada aji a kowani, kasa,
Duk inda suka kyalla ido suka ga mace har sukaji suna son ta tofa sai sun lasa suke iya kyale ta,
Wani irin kishi ne mai karfi ya tukako zuciyar Yusuf saboda tuna kowa ye Sonny din da yayi,
Maryam din ce ta bashi tausayi a yadda yake ganin cewa duk laifin shine da ya kawo shi inda take,
Inda zuciyae shi tai dan sayi shine tunawa da yayi da kowace ce maryam din,
Shi kadai ya murmusa don sanin kowace maryam din dayayi da sanin halaiyanta,
Maryam yarinya ce da tasan ciwon kanta, wace abin duniya bai taba tsone mata ido,
Ga tada kau da kai ga abin mutum don shi duk iya sanin da yai mata bata taba cewa tana son wani abu agurin shi ba,
Ire iren wanan tunanen yai tayi kala kala inda daga karshe ya yanke shawaran, abinda ya dace yayi akai,
Jiki ba kwari haka ya mike daga gurin da yake zaune saboda shawaran da ya ke ganin itace kawai mashi mafita,
Ya hana shi sukuni a zuciyar shi don haka wanka ya fada ko da zai ji sanyi a zuciyar shi,
Ga abinci a gaban shi amma sam yakasa koda spoon guda, ne saboda irin yadda yake ji, a zuciyar shi,
Dan tsohon da ya taimakane ya fado mai a rai saboda yana da bukatan yayi ko ya jikin nashi
Kira na biyu aka daga wayan da sallama bayan ya karba ne,
Yagabatar da kan shi a gare su nan da nan suka sheda shi,.
Godiya suke mai shikuma yana kokarin tambayar su lafiyan tsohon su,
Nan dai yai masu alkawarin cewa zai dawo ya ziyarce su zuwa gobe idan ya rarage abinda yakeyi,

Maryam tana zaune duk tunanen rashin jin muryan Yusuf kwana biyu da batayi yana daga cikin abinda ke dan damun ta,
Bata san may yasa ba yanzu take yawan jin shi a jikin ta fiye da tsan manin ta,
Muryan Anty Dije ce taji a kan ya tana tambayar ta Maryam lafiya dai ko ?
Bakomai tace wa yar nata,
Bakomai nagan ki haka a zaune cikin damuwa maryam,?
Yar mursmuhin mai kama da yake ta sake kawai,
Kodai Yusuf kike tunane tunda naga jikin ki dai kin ji sauki yau,
Mamaki ya cika maryam din don jin abinda yar nata tafadi,
Kai tagirgiza tace haba dai Anty may zan yi tunane gare shi,
Anty dije wace bawai ta yarda bane tace bam san may yasa wayoyin shi suke a rufe ba,
Duk layin shi nakira akashe suke tun jiya da safe,
Don haka nima ina tunanen ko lafiya yake amma barin kira Jibrin muji,
Jibrin din ne ke sheda ma su cewa yatafi kano gurin wani meeting ne amna zuwa gobe zai dawo Insha Allah,,
Sai alokacin maryam tai dan ajiyan zuciya har yar nata taji,
Amma sai bata ce mata komai ba wucewa kawai tayi zuwa cikin gida abin ta,
Gurin da take zaune tadan kai kwance anan barci ya dan kwashe ta, batare da tasani ba,
Anty Dije wace ke kitchen tana tuka tuwo muryan maryam dake barci a falon ya katse ta daga tukin tuwon da takeyi,
Wani irin kakakari da shure, shure takeyi kamar wace ake zarewa rayuwar ta,
Sosai Anty Dije ta razana saboda ganin yanayin maryam din, a lokacim,,,


ZEEE MAKAWA YELW@
[4/28, 5:40 PM] β€ͺ+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
8⃣2⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI

Ina rokon Allah ya nuna mu na, wanan Watan mai Albarka da Darajja, Ni,ima Gafara da Rahama,
Ya Allah ka sa damu da Albarkokinan na shi, lafiya RAMADAN KAREEMπŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘
AMEEN YA ALLAHπŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘


A gajiye yake taka matakal ginan ya na saye da rigar shadda mai ruwan makuba
Dinki rigar iya cinyar shi kawai da yar gutunwar hannu daidai gwiwar hannu,
Saboda zaman da yasha gurin meeting din starching rigan yadan takure , takure,
Kan shi babu hula sai sheki da yakeyi yaji oil ga kamshi,
Hannun shi guda yana a cikin aljihun shi da sauri sauri yanzu yake tafiya don ya isa gurin motar shi,
Tundaga nesa ya bude motar yana isowa yashiga,
Fuskan shi ya shafo da hannushi yakara mayar wa har zuwa wuyar shi wani iska yafurza tare da fadin Ya Allah,
Yana daukar waya kiran anty dije yana shigowa mashi,
Sai a lokacin ya dan yi ajiyar zuciya a irin yadda yake ji, a zuciyar shi,
Sallamu Alaikum Anty Sorry zan kira ki dan anjima kadan pls, ina saman hanya ne,
Bata aje wayan sai fada data haushi dashi cewa zai kashe waya haka har kwana biyu,
Murmush mai sauti ne yadan sake saboda yasan cewa shi mai laifi ne sosai,
Don haka yace gwiwa na a kasa Anty aimin afuwan pls,
Kwanar asibitin da yanufa don diba tsoho ya karya batare da wani dogon tafiya ba ya isa asibitin,
Tsohon yana kwance saida hannun shi guda yana daure da ruwa ana mai kari,
Dan tsohon najin muryan Yusuf ya yunkura da niyar tashi,
Gaba daya har Yusuf din suna hada baki gurin cewa ,a, a, a baba ka kwanta da ruwa a hannun ka,
Tsohon yakoma ya kwanta yana cewa to, to, yana mai gyara kwanciyar shi,
Yusuf ya matso gab da tson inda suka sa mai kujera ya zauna suna fuskantar juna da tsohon,
Alokacin Yusuf yaji a zuciyar shi dama ace wanan tsohon shine mahaifin shi
Dayafi kowa morewa, mahaifi a rayuwa da ba zai iya gusawa nan da can ba a wanan halin da zai tsaya ya kula da,duk wani motsi na shi,
Yana zaunawa wanan tsohon yafara zuka mai albarka ya na mai fatan gamawa da duniya lafiya,
Wani abu ne yazo mai a makoshin shi ya tokare mai yakama jin wani irin tukuki a zuciyar shi,
Da kyat ya samu,ya hade wasu miyau masu daci, da yauki
Sai yar dariyar yake yake yi a fuskan shi tankar ya kai mai ciki,
Kai mutumin wani gari ne ?
Tambayar da tsohon yajefo shi da ita ke nan a lokacin da yake cikin tunanen shi,
Forgigit ya tuna cewa ko shi waye,
Inda har za,a tambaye shi ba zai gushe da fada masu gaskiyan ba kamar yadda ya saba fada cewa Asalin shi FUREN KAN JUJI NE,
Dayan yaron tsohon ne ke cewa ana tambayar ka ko kai mutumin wani gari ne wai,?
Kwantagora ya ba da, ansa, a ta kaice ,,,,
Wai, wai, akwai nisa gaskiya a cikin wani jaha garin yake dayan mutumin ke tambaya,,
A can cikin jahar Niger garin yake, yankin yamma,
Allahu akbar inji tsohon ya fadi lokacin da yake dan gyara kwanciyar shi,
Saida muma zamane yakai mu can asali mu yan jahar,Benue ne,
Gaba dayan su suka juyo da kallon su inda yake cikin mamaki,
Yace musulunta nayi bada dadewan nan ba saboda fahintar musulunci itace hanyar gaskiya,,
Gaba dayan su a lokaci guda sukace Allahu Akbar,
Kan shi ya sunkuya kasa don abinda yake ji, a jikin shi tun jiya,
Babu abin dake a zuciyar shi duk yinin yau kamar yadda zai furta hukunci da ya yanke a kan su,
Dan tsohon nan na kwace cikin cijewa irin ta mai jin jiki,
Tsohon yai ta bashi labarin ko shi waye da kuma yadda ciwon ya samay shi ,
Nan ne Yusuf gane cewa dan tsohon irin malaman nan na zaure ne masu tara almajirai da yawa agidan su,


Zaune take cikin wani yellow material dinkin buje da riga masu kyau,
Dan kwanlishi ba daurawa tayi ba just ta aza shi saman kan tane,
Wayan ta yana a hannun ta tana dan yin game da shi,,
Kirane ya shigo mata sai dai bata gane ko waye mai nombar ba,
Da sallama ta dauki wayan muryan mace ce ke magana a layin,
Maryam taji an anbaci sunan ta, batare da ta ansa ba taci gaba da sauraren mai maganan,
Sai kuma mai maganar bata kara cewa komai ba dan shiru ne ya biyo baya,
Tace baki sanni ba amma dai da zaki gan ni zaki sanni,
Kiran da nai maki shine akan nasaban ki da Yusuf watau Joseph dan gidan Ema mai manja,
Gaban maryam ne a lokacin yabada wani dam haka kawai batare da tasan ko may ye za,a fada mata, ba a lokacin,
Wani,tsoro ne ya lullube ta da sauri tadan kama waigawa ko zataga Anty ta da ido, a kitchen ta hango ta, tana kada miya,
Karo na biyu mai maganar ta kara ambatar sunan maryam din wanan katon kamar mai rada tai maganan
Daidai lokacin da maryam din ta iso gurin da yar na ta take ,
Kada kiji tsoro maryam ki saurare ni da kyau kiji may zance maki, da kyau,
Gaskiya ni bazan iya cutar da mutum dan uwana ba shi yasa naga ya dace in fito fili in fada maki abin da ke gudana akan ki,
Wayan suka zuba wa ido daga ita har yar ta suna sauraron mai magana,
A kofar shiga gidan ku an rufe wani abu wanda daga ke har Yusuf din indan kun taka kun rabu kenan har abada,
Sannan kuma ba zai kara kula koda Anty kiba bale wani naki,
Ke kuma ance a sakar maki ciwo mai kama da ta hauka ko batar hankali,
Don kowa yazaci baki da lafiya ne shi yasa zai guje ki,
Tagumi sukayi suna sauraro sai innalillahi suke ambatawa kawai,
Inda taci gaba da masu kwatancen gurin da aka binzine masu abubuwa akofar gida,
Anty ce ta tambaya cikin saurin jin datayi kamar mai shi tana kokarin rufe wayan ta, da cewa,
A sake cikin sauti mai karfi tace yanzu may abin yi yar uwa,
Mai maganar tace don girman Allah ku rufamin asiri kada ku bari agane cewa nice na fada maki wanan zancen,
Tambayar ta Anty Dije takara yi akan cewa may ye mafitan zancen,
Sai cewa tayi aje daidai gurin da aka bizzine abin a tone tun gudan su bai bi gurin ba,
Don tun daren kwana hudu daya wuce, aka rufe abin agurin,
Kuma wanda akaba kudi don yadiba koda maryam din tabi gurin yace har yau baiga fitan ta daga gidan ba,
Kinga ke nan abin bai fara aiki ba ke nan ko tace cikin nuna kulawa,
A sanyaye Anty Dije takewa mai wayan godiya sosai inda take cewa ai babu komai don duk ciwon musulumi na musulmi ne,
Inda tace insha Allah idan taji wani abu zata kira su ta sheda masu da wuri, wuri,, don su dauki mataki,
Maryam wace tun fara zancen idonta yaciciko da kwalla,
Take,hawaye yafara mata sintiri a idanun ta take dan she,shekan kuka,,
Anty don Allah ku taimaka ku jaye zancen nan tun ba,a halakani ba,
Zan hakkura da Yusuf din don dama nasan cewa ba sa,an yina bane
Kawai dai biyayyane nayi har na takai na fara jin shi a jikina,
A haka ta dinga share hawaye da bayan hannun ta,
Fuska a daure don jin abinda maryam din tace Anty Dije take kallon ta, tace wa yar uwan nata,
Yanzu maryam ina imanin ki da tauhidin ki ya shiga da har zakiyi believed da wanan maganan,
Kiyi imani da cewa duk abinda ya samay ki daga Allah ne maryam ,
Tunda har Allah yasa munji abinda ake yi akan ku kin ga sai kawai mu roki Allah ya kare muna ke,
Da sauri maryam tadan kalli yar,uwar nata tana kada mata kai tace, cikin muryan kuka,
Anty kawai dai a fasa wanan abin ni bazan iya ba gaskiya tun yanzu ace har an fara yiwayiwa mutun irin wanan sherin,,
Tana kokarin share hawayen ta, sheshekan kukanta na tashi cikin tashin hankali,
Murmushi Anty Dije ta yi ta girgiza kai, kaiyya maryam ai idan kince haka sun samu galaba akanki ke nan,
A sanyaye maryam tace cikin muryan kuka, Anty to ya za,ayi,
Anty Dije tace barin kira baba in sheda mashi abinda ke faruwa kafin abu yai nisa,
Daga haka suka bar wajen cikin tashin hankali saboda duk sun shiga rudani,

Yusuf ya kasa wuce saida aka sallami wanan tsoho ya dauke su zuwa, gida,
Badon komai ba sai don ya fidda kan shi a zargin da suka yi mai tun farkon dauko su zuwa asibitin,
Sosai mutanen kauyen sukayi mamakin ganin su tare da mutumin da sukayi zargin cewa dan yankan kaine da farko,
Saboda mugun haduwan da sukaga yayi gashi matashi ga kyau ga kudi kuma,
Nan malam yaroki Yusuf akan don Allah idan an kwana biyu yadawo garin yana da bukatan ganawa da,shi,
Amma kafin ya wuce yasa yaron shi karami yai mai a wani rubutu a ruwa yace yasha,
Yusuf wanda bai, so hakan ba azuciyar shi amma sai ya daure ya sha saboda biyayya kawai,
Da zai tafi yakawo alheri masu yawa yai ma malam da jama,an shi sukayi sallama dashi cikin dadin rai,
Sunkarbi nomban shi don su kirashi a cewar shi idan ya isa,
A hanya ne ya ke tunanen kitan Anty Dije wace yaiwa alkawarin kira tun daren jiya,
Ya so ne da kawai idan ya koma sai ya samu lokaci ya je kwantagora ya fadawa Anty irin shawaran da ya yanke a kan maganar shi da maryam acikin ruwan sanyi,
Duk da yasan cewa akwai rikici a gurin baba don dawuya yadauki yar shi haka kawai yabawa wanda bai san asalin shi ba,
Amma dai shi da kan shi zai fadakar dasu don su fahinta akan Sonny din,
Duk da yasan cewa ko shi don sun san asalin shi dakuma irin cin fuskan da akai mai akan neman mace,
In badon haka ba yasan cewa baza,a bashi ita ba sam saboda su talkawane da suka san mutuncin kan, su,

Zaune take a gurin da tagama sallah isha,i amma tunane duk ya addabe ta azuciyan ta,
Ba komai take tunane ba illa ta yadda za,a bullowa wanan bakon al,amari da yazo mata,
Don dai ita a iya sanin ta batada abokin fada ko kuma hamayya, ako ina,
Amma wai sai gashi kwatsan an wayi gari ana son a cutawa rayuwan ta,
Wayan hannun tane ta daga don ta diba time, tagani, saboda tasan cewa da zaran angama sallah isha,i baba zaizo,
Takwas da rabi taga don haka tamike tafara dan tattara kayan da tai sallah don kada baba yashigo bata a falin su,,

Falon yai shiru, baka jin komai sai muryan Anty Dije kawai da ke koro wa baba da bayani tiryan tiryan,
Kamar babu kowa a falon bayan ita, kowa da irin nazarin da yakeyi, daga baba har aminin nashi da sukazo tare,
Maryam ce a gefe guda tsugune sai hawayen da take zubarwa akai akai,
Baba kan lumshe idon shi yayi saboda mamakin yan Adam daya kama shi,
Yasan cewa Allah ne ya kare mashi yar nashi saboda addu,oin da yake yawaita yi musu, akai akai,
Yarinyar tana bashi tausayi saboda yasan cewa akan shi ce tai biyayya
Wani irin mugun tausayi tabashi da yadan kalle ta da,wutsiyan ido yaga irin yadda take share hawayen dake sintiri a idon ta,
Abokin baba ko ince aminin shi kuma makwabcin su, yai murmushi cikin gyada kai bayan ya gama jin bayanin da Anty tai masu kaf,
Yadan kalli inda baba yake yace, ina kon kwanto, amma ai babu komai idan har sun san wata aibasu san wata ba,
Don kaga Allah ne ya tona masu asiri don ya wargaza masu plan din su,
Amma zasu sha mamaki don ta Allah batasu ba sherin su zai koma masu,
Sallama sukayi wa su maryam din suka tafi tare da kwantar masu da hankali na cewa babu abinda zai faru da yardan Allah,
Hakan yasa hankalin maryam ya da yar uwanta ya dan kwanta amma ba wai gaba daya ba,
Koshi saboda sanin da sukayi wa shi malam na ngaski din ne cewa bakanwar lasa bane shima,,,,,,

Masallacin Jumma,an ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login