Showing 195001 words to 198000 words out of 255288 words

Chapter 66 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1373

sakon ,
Sai kuma ta jawo nata wayan takirashi take sheda mai cewa itace ta tura mai sakon ,
Tagani ne acikin wayan maryam shine ta ce bari ta turo mai,
Da sauri kuma tagoge kada maryam ta fahinci cewa, tayi amfani da wayan,
Ba,a dauki wani lokaci ba da maryam tadawo dakin dauke da kulolin abinci a hannun ta, ta dire su a gaban Naimat,
Sosai Naimat taci abincin don abincin yai mata dadi a baki,
Ta dade rabon da taci wani abinci irin haka kamar yadda ta ci shimkafa da waken,
Tana ci suna zuba hira da maryam kamar a bin hadin baki saiga, Safiya ta shigo gidan,
Gaba dayan su suka sa ihun murna a lokaci guda ,
Maryam wace tasan da,zancen korafi a kanta a bakin safiya ,
Ta,sheko da guda ta,rugumay ta ta baya itama dai ture ta tayi tana cewa anya kuwa maryam idan kin yi aure zakiyi zumunci, kuwa?
Bari har inyi auren kiga yadda zanyi ta zumunci da ku sai kun ce na i,she ku,
A lokaci guda suka sa tsaki a tsakanin su don jin abinda maryam tace,
Au to ku bari ku gani sai kun sha mamaki na tafada cikin tsigar zolaya,
Safiyace bayan ta zauna take cewa tare da daga kai takalli maryam,
A,A ya bugo maki waya ne maryam,?
A lokaci guda fuskan Maryam ya sauya daga fara,a zuwa bakin ciki
Batare da ta iya bada ansa ba tace, idon ta sun dan ciciko da hawaye kamar za su zubo, tace,
Safiya pls kada ki kawo min zancen wanan mara mutuncin pls,
Cikin mamaki suke kallon ta don jin cewa yau maryam ce da bakin ta take kiran A,A da wanan sunar,
Safiya tadan gyara zama daga kan kushin din da take tace hmmm,
Ji min ,fa A,A din nan dan wullakancin mutum kawai jiya yakirani da waya
Yadinga surfa min zagi ta inda yake shiga ba nan yake fita ba,
Wai mu makwadaita, macuta munyi mai butulci a kan kudi,
Ba son Allah da Annabi kike mai ba tun farko don da,son gaskiya ne da baki canza ra,ayinki ba akan shi,
Ke tun ina cewa ya tsaya in mai bayanin yadda zancen yake y
Fam yaki yarda da zance na in fada maki har takai ni ma nafara mayar mai da bakaken maganganu,
Naimat ce tace may ki,kacewa dan iska ke kuma,?
Ta tambaya a cikin fushi da harshen hausan ta dake da surki da na kabila,
Safiya tace haba ke ko nice fa,
Har zaki tambayeni may nace mai,
Ai saida ya shiga cewa kin gane ne safiya ki tsaya ki saurare ni ma wallahi,,,
Tace kawai sai na kashe waya din ban son jin komai daga bakin dan iska kawai,
Kawai ba,su ankara ba sai she,shekan kukan Maryam wace ke gefen su suka ji,
Lokaci guda duk suka kai mata kallo a cikin mamaki,
Da farko safiya tana zaton don tayi wa A,A cin mutunci maryam ke kuka,
Amma sai suka ji muryan ta a cikin kuka tana cewa,
Ban taba zaton cewa malam zai iya min irin wanan cin fuskan ba,
Ida da har ina kwadayin dukiya ne ai da shine mutun na farko da zai fara shedan haka,
Amma yafadi mana duk zamana dashi na taba rokon shi ya bani koda kwandala ne,,
Nan dai suka shiga bata mussalai, masu ma,ana har ta dan kwantar da hankalin ta,,,,

Zaune yake saman kujera yana karanta text din sai kawai yaji cewa bazai iya karasawa,ba,
Don haka ya aje wayan saman table din glass din da ke a gaban shi cikin bacin rai,
Wani irin abu yake ji a zuciyar shi takar idon shi zai rufe, alokacin,
Ji Yusuf yi bai ma san may ya ke ciki ba a lokacin,
Don haka sai ya ji tankar numfashin shi yana shirin daukewa a lokacin,
Da kyar ya iya nemo natsuwa ya ya furta a hankali yayin da yake dafe da kan shi dake mai ciwo tankar ya tsage,
Yace,
Innalillahi Wa, Inna, Ilaihim, Raji,un
Ya jima shiru dafe da hoshin shi da hannun shi guda a hakan yana nanata wanan addu,an,
Sannu a hankalo yadan dinga jin zuciyar shi na walwalewa a hankali daga kuncin da yake a ciki da farko,
Mikewa yayi zuwa bakin window falon shi,,yadan furzar da iskan kamar yadda yake yi, idan yana cikin yanayi,
A,A ya ambata a hankali insha Allah zan gwada, maka cewa wani dan furen jujin yafi dan furen gida mutunci,
Zan gwada maka cewa imani da biyayya suna da amfani ga dam adam ,
Daga haka yaji wani irin tukuki ya taso mai don haka bai iya cewa komai sai kalman innalillahi da yake ta nanatawa a cikin ranshi,
A hankali ya tako zuwa dakin shi yana mai tunan cewa lalai A, A zan gwada maka cewa,
Ni Yusuf nagaji sunan kwarai da ga mai sunan ,, ni Namijin Gwarozo ne acikin mazaje,
Ba dan akuya ma ciyi amanan diyan mutane da abokan azarki ba,
Daga haka yaja kafar shi da kyat har ya isa bedroom din shi,,
A rigingine yakwanta yadinga tasbihi ga Allah ubangijin shi, tare da neman a fuwan shi,
Yasan cewa wanan irin gorin shigar shi cikin addinin, musulunci da mutane ke masa,
Ya ringa yin addua akan Allah ya bashi ikon cin wanan jerabawan da ya ke acikin sa, daga kuma neman rinjaye akan masifun da yake fuskanta,
A haka ya dinga juyi a kan gadon shi yana tuna irin kalaman da ya ke fuskanta daga mutane da dama akan musuluntar shi,
Jikin shi yana jin shi tankar anyi mai duka idon shi sun kada sunyi jajir, rayuwa gaba daya yafita ran shi,
Allah gafurur Rahimun, yana, nan cikin wanan halin, ne barcci ya dauko shi,
Ya jima sosai yana barcin bai farka ba har zuwa lokacin da nauran da ya saita masu tayar dashi daidai lokacin sallah,
Tabbas yaji dadin wanan baccin da ya samu yayi ,, don yaji saukin
Don da bai yi barcin nan na a haka zai wuni cikin bakin ciki da kunci,,
Wanka ya fada yana fitowa ya wuce massallaci,
Bayan yadawo ne yaji shi wani wasai da shi duk wani bakin ciki da kuncin da yake, ji ya daina jin su,gaba daya,
Dining table ya nufa inda yasamu hamza ya hada mai abincin shi, haka ya dinga cusawa a cikin shi, har sai da yaji yayi dam,
Komawa yayi saman two sitter yadan kwanta kamar mai yin barcci, hannun shi rike da goshin shi,
Tunane yake yi don sai yanzu yasan ko may ye so,
Tabbas bai taba sanin cewa ana son mutum irin yadda yake jin Maryam a,rayuwar shi a halin yanzu,

Kusan kwana biyu yana cikin wanan damuwar idan kaga walwalar Yusuf sai idan yana tare da,Sonny ko Jibrin
Lokacin da Sonny ya gama abinda yakeyi a garin su,
Don haka sai suka fara shirin tafiya kwantagora ganin kayan al,adu kamar yadda,Sonny din yaji labarin su daga bakin Jibrin abokin hiran shi da yawo,
Shiri na sosai sukayi saboda irin shigar da zasuyi yana bukatan kudade, da sauran abubuwa,
Ba su wani dade a hanya ba ko da suka taso,
Saboda irin gudun da sukeyi ga kuma motocin su lafiyyayu ne so sai,
Sun iso lafiya garin sai dai wanan karon bai wuce direct gida Anty nashi ba,
Sosai tun a hanya Yusuf ke kallon tsarin kasan hausaw yana mai yabawa da irin abin da yake gani,
Shigowan su garin yakara sa Sonny rudewa sosai don gani yadda garin ya tsaru tsab,

Yusuf ne ya dan sulale zuwa gidan Anty nashi don ya sanar masu da zuwan Sonny,
Ya iso kofan gidan su Anty Dije din inda yaga samarin dake fira kamar kullun
Sun mike sukayo kan shi cikin murna danuna jin dafin zuwan shi,,
Wanda hakan ba karamin dadi yaiwa Yusuf din ba, a cikin ran shi,
Don ko ba komai sun nana mai kulawan su gare shi,
Nan suka,shiga jiddan kayan tsaraba zuwa cikk cikin jin dadi,
Anty Dije ce ya riske a kofan kitchen tana kokarin dauko plate a mazaunin shi,
Tana ganin Yusuf da jin sallamar shi ta mike da fara,an ta tana mai sannu da zuwa da bakin da babu sanarwa,
Ya yai dariya duk da yau kawai sai ya tsinci kan shi da jin kunya da nauyin anty din,
Yakaraso gaban ta yadan rusunna, yace Anty barka da gida,
Cikin dan hararan wasa tace gaskiya Yusuf kana son muyi fada yanzu,
Dariya yakara yace tuba nake Anty na tafiyan bazata yazo min,
Shiru Anty tayi cike da mamaki, jin abinda yace batare da taga wani alamar waaa a fuskan shi ba,
Sai kuma batayi magana ba tace to sannun ku da zuwa,
Ya amsa da cewa yauwa Anty mun samay ku lafiya,
Sai dan satan kallon ko ina yakeyi ko zai hango maryam da idon shi,
Ya dan fuskan ci anty din yace wanan karon fa sa bako nazo anty,
Gaba daya hankalinta ta mayar gareshi don jin abinda yace,
Falin suka shiga a lokacin,sanan yakara cewa wa qn a bokin nawa dake South Korea shine mukazo dashi don yaga gari,
Zama yayi yana mata bayanin makasudin zuwan Sonny kwantagora,
Maryam wace kamshin Yusuf kawai ya isar mata isowar shi gidan daga gurin da ta idar da,sallah ta kwanta,
Zubur tamike daga saman abin sallah da take kwance tafito daga dan wajen window inda zata ita hango Yusuf din,
Daga inda take tadan daga labule tana hangen shi,
Yana saye cikin wasu kanan kaya da suka kara mai kyau suka fitar mai da kurciyar shi da,wayewar shi fili,
Hannayen shi suna zube a cikin aljihun wandon, shi,
Wani irin lumshe idon ta tayi lokacin da hancin ta ya shakan mata kamshin shi,
Jikin shi ne yabashi cewa ana kallon shi don haka yadaga ifon shi, zuwa kallon gurin da take,
Daidai lokacin da ta bude lumsasun idanun ta suka hada ido da Yusuf din,
Cikin sauri maryam din ta sake labulen tayo baya tana mai dafe kirjin ta tankar wace taji tsoro ko taga abin tsoro,
Wani irin lalausar Murmushi ya sake a lokaci guda,
Son Maryam din ne yaji yakara shigan shi a lokaci guda,, bai taba jin yana son mace haka ba sai wanan karon,
Muryan Γ€nty ce ya katse show din itace ke kiran maryam din,
Sai da ta sa wani dan karamin hijabin ta baki a saman kayan dake a jikin ta sannan tafito cikin tako guda guda,
Kanta a kasa ta karaso gaban su saboda kunya, duk ya rufe ta,
A hankali tace mai sannu da zuwa uncle ya hanya,?
Tafadi a hankali kamar wace bakin ta ke ciwon magana cikin wani irin taushin murya,
Daga Yusuf har anty yanayin maryam ya basu tausayi , sai dai duk suka share,
Ta juya zata wuce ne anty tace cikin murya maikama da rauni,
Tsaya mana maryan ku gasi zan dan shiga gidan lami in samo kankara ne,
Bayan wucewan anty ne makwabta Yusuf wanda ke zaune dan nesa kadan daga gurin da take tsaye kamar kwance saman bayan kujera,
Kanshi yadago yadan kalle ta cikin wani irin yanayi mai rikitar wa,
Da sauri maryam takara dukar da kanta kasa tana wasa da yan yatsun ta,
Batayi aune ba sai ganin mutum tayi a gaban ta tsaye yana mata wani shu,umin murmushi,
Murya kasa kasa yace baki yi murna da gani na ba ke nan ko ?
Jin hakan yadan sata saurin dago kai suka kara yin ido biyu karo na biyu da shigowan shi,
Ido ya kashe mata wanda hakan yasa maryam din duk ta wani rude a lokaci guda, ta dago idon ta cikin rudewa da razanar
Nan da nan gangan jikinta yadauki rawa don jin numfashin Yusuf din gab da ita,
Ganin irin yadda maryam din ta rude a lokaci guda yasa shi tsayawa yana mata wani irin kallo cikj. So da kauna,
Ji yake a lokacin tamkar ya rungumay maryam din da gagawa,
Amma yin hakan haramun hakan bazai yiyu a garesu ba,
Dole ya tillasta kan shi da dan ja da baya daga kusan tan junan da sukayi suna fuskan tar junan su,
Maryam yakira sunan ta cikin wani kasalalen murya tankar wanda ya tashi daga barci,
Yace may yasa kika ki bugo min waya tun daga wancan ranan da kika kirani,?
Idan kuma nakira baki picking, Why maryam,? why ?,
Yafada tankar wanda zaiyi kuka alokacin don wani irin abu da yaji yana fusgan shi,
Tabbas komai yana iya faruwa a irin yadda yake ji akan ta
Da gagawa ya juya zuwa gurin da yatashi da farko ya zauna,
Lemon da Anty Dije ta aje mai saman table ya tsiya a cup,
Sai lokacin maryam tadan saita kanta daga ruduwar da Yusuf yasakata a ciki cikin yan dakikoki,
Muryan shi taji yana cew ina da bako maryam,
Ina son ki shirya muje ki gaida shi,
Da sauri tadago kan ta takaima gurin da yake kallo,
Kai ya gyda mata yace yes zuwa gobe zan zo in dauke ku keda,su Assalam mutafi,
Sai alokacin maryam tai wani irin ajiyar zuciya har Yusuf din yaji ta daga inda yake,
Kallon ta yakara yi kawai cikin wani shu,umin murmushi sai kuma ya mike tsaye batare da yakara kallon ta ba saboda ba zai iya jurewa ba a irin yadda yake ji,
Don maryam din yaga takara mai wani kyau da girma ga kuma haske da tadan kara, akan bakin tada ke shining,
Daidai zaifitane yace sai ki shirya zuwa gobe din zan kiraki in fada maki time,,,,,,,,



ZEEE MAKAWA YALWA
[4/28, 5:38 PM] β€ͺ+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
7⃣9⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI

Anty Saffena, Anty Nafessa harzami, Anty Hafsat Yusuf, Maman Farida, Anty Bintu katsina, Maman Walid, lovely Daughter na Jamila Safiyanu,
Tare da duk wacce ban samu ambatar sunan ta ba aciki da fatan zaku yafe min rashin sa sunan ku a jerin sunayen da nazano,,
Allah ubangiji yakara dauka da bude da rahamansa agare mu baki daya, nagode kwarai yan uwa da irin kulawar da kuke bani a kullun tare da fatan zaku dinga hakkuri dani a koda yaushe,
πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘


Saye take cikin,wani dogon riga, mai ruwan Jan colour,,, duwatsun jikin rigar ,farare, ne,
Dinkin dogon hannu ke a jikin rigar ,
Sai gyalen rigar tadan yi roling din kanta dashi,
Sai yar karaman, jaka fara da ta rika a hannun ta, shima yana da wasu stones farare,
Assalam da Issalam suna sanye cikin shigar English wear, masu kyau da daukan ido,
Safiya ma tana saye cikin wani dogon riga light, green, mai kyau dinki shi kamar ta banga, rigar ya karbe ta,
Wanan karon Jibrin ne ya zo da su, daga gidan Anty Dije zuwa gidan Yusuf inda su kaiwa Sonny masauki,
Abincin lunching ne suka dauko daga gurin big Anty din nasu,

Waje suke zazaune saman fararen kujeran roba, suna shan iska, shi da Sonny,
Motar da ta stsaya daga dan nesa dasu kadan hankalin su ya kai garesu,
A hankali suka sako kafan su daga wajen motar, kafan maryam dake saye cikin wasu fararen takalma masu wasu belts a bayan su,
Sonny wanda hankalin shi na gurin motan don ganin cewa a kwai mata a cikin motar shiko dama mayen matane,,
Maryam wace kafar ta kawai ke a waje, ita bata fito ba tukun,
Yaran ne suka fito da murnan su don hango uncle da sukayi zaune daga nesa saboda basu san cewa yazo garin ba,
Sai safiya ce tafito a gaban motar tare da Jibrin din,
Yusuf wanda ke rugumay da yaran ajikin shi yana masu magana hankalin shi ya koma gurin da ya hango ta fitowa daga cikin motar,,
A hankali tafito daga cikin motar yayin da take dan gyara rigan ta a hankali,
Daidai lokacin Safiya ta zagayo ta iso gurin da maryam din take tsaye,
Sonny dake masu kallon kurulla kamar yana son ya, ga,no munin mutum daya daga cikin su,.
Tafiya sukeyi jikin su na wani rausayawa kamar kifi,,
Sonnu wanda numfashin shi yai kamar zai dauke saboda ganin wa yan, nan zukakkan yan matan dake tafe in suke,
Kuma wai duk a cikin wanan garin da yake ma daukan kauye a idon shi,
Wani irin kyaune ga wanan yariyar dake baya saye da Jan riga haka,?
A cikin wanan takon nasu na natsuwa har suka karaso inda su ke zaune,
Idon Sonny din har zuwa lokacin da suka karaso gurin nasu kyam a kan su,
Maryam wace wanan kallon da yake masu duk ya takura ta ji take kamar ta shake shi,
Kujeru suka basu suka nuna masu gurin zama inda Yusuf din yai masu nuni da su zauna,
Ko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login