Showing 12001 words to 15000 words out of 255288 words

Chapter 5 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1336

gida ne gurin sauri,
KB ne ya waiga inda Joseph ke tsaye yana kallon ya ce,
Man wanan taimakon ka ne, pls
Cikin nuna rashin ganewa yake kara tambayar su, komai zai mata nan dai KB yakara mai bayani,
Kafadar shi dan daga alamar ba damuwa ai,
Shigowan su a cikin dakin taron ya haskaka so sai don mai MC yai announcement din shigowar su kamar yadda idan wasu sun shigo ake cewa ga yan kungiyar kaza nan sun iso,
Kallo ya koma gare sai kuma dan kus kus yatashi a gurin kamar yadda aka saba, inda anga kirstan na shiga cikin musullumai adinga a queuzing din su ta hanyar da bai dace ba,
Wanda yin haka najawo ma su sanyin gwiwa, so sai,
Mafi yawan mutane sai mamakin Aisha sanda sukeyi a cikin su ke don sanin cewa sunan ta na cikin fitattun yamatan da ke tashe agari,
Kuma gashi kayan ta sundanyi shigen kala da na jikin Joseph din wanda shi bai ko dago da hakan ba,
Zaman su bada wani dadewa aka fara program din bukin,
Ana aka fara gudanar da abubuwan da aka tsara a gurin,
Zaune Joseph yake yadan tokare habar shi da hannayen shi dukka biyu,
Yana kallon yadda ake guda nar da bukin abokin su, wanda yai aure,,,
Wani can wanda Joseph din bai sani ba yazo ya ja KB da hira har suka bar kujerar,
Jibrin dake gefe a zaune wayar shi taikara bayajin may ake cewa don haka ya tashi yadan koma can ta waje kadan ko zai ji kiran,,,
Yanzu,daga Aisha sai Joseph ke zaune, a inda aka tanadar masu, suke zaune,
Daga inda KB yake suna magana ya jiyo muryan MC na cewa ana bukata Joseph da Aisha su fito su taya ango farin ciki,
Saida KB ya dafe kai don yasan cewa da wuya Joseph din ya fito tunda baida masaniyar hakan,,
MC nata nata abinda akace text kb yayo mai cewa yafirmta dashi da yari yar nan suyi rawa,
Kamar kada ya tashi sai yatuna cewa bazai kyautawa angon ba inda har bai fita ba don haka ya fara mikewa batare da ya kalleta ba yace mata sai ki tashi mu fita ko,
Ba wani rawa sukayi ba sosai amma anji dadin fitar nasu don Joseph ya nuna kulawar shi ga ango,,
Wasu yan mata dake ge fe zaune suna kallon yadda ake ta
Su ka fara yan suraitai kamar haka,
Au dama wanan ba musullumi bane ke inji wa ya fada maki,
Dayar tace bakiji lokacin da ake cewa ana son Yusuf Joseph yafito tare da,Aisha sanda
Sai gudan tace kai amma anyi harasa wallahi guy kamar wanan kuma bai sallah,
Dayar tace gaskiya ni saima kawai naji haushin shi ya kamani wallahi, ita kuma Aisha don kwadai sai wani shige mai take ta yi,
Wace ita ce cikon ta hudun masu hiran da tun da suka fara zance bata ce kala ba,
Tace kai ku dai na daukar wa kan ku wahala ma,
Iyaka,ku da shi kuyi mashi fatan alherin shiga cikin islama indan har yana da rabon shiryuwa, Allah yasa yagane gaskiya yadawo hanya,
Sai ta farkon tai caraf ta ce a haka ?
Wanan ai yai nisa baya jin kira, in bashi ba ai tun yana yaro da ya musulunta, ko,,,,,
Ita dai wace bata maganar sai cewa ta yi ai abin daga Allah ne kawai, in Allah ya nufe shi da shiryuwa saiko ya shiru, yadawo hanya,
Haka dai kusan ko wani kujera suke ta zancen su kamar yadda gurin buki ya tana da
Kai kana kallon wani wani yana kallon ka,
Ganin cewa dare ya fara yasa Joseph yai su KB magana akan cewa su zo su tafi don shi baya yin dare sosai a waje,
Don duk haka tarbiyar yaran IBO suke duk ganin kada su basu yarda,su kai karfe takwas na dare waje,
Wana na daga cikin irin tarbiyar da suke wa yaran su,
Idan kuma sana,a ce bakin karfe shidda andawo gida ke nan daga gurin sana,a,
Saidai kuma tun karfe bakwai na safe anbar gida ke nan zuwa gurin bidar kude, (Allah ya kyauta)
Wanan haduwar da Joseph yayi da Aisha itace silar haduwar su,
Don tun a gurin da ta ce ya ara mata waya takira kawar ta don su wuce tasamu nobar shi,,,
Da zai tafi ma lake mai tayi akan ya bata lift zuwa gida saboda dare yayi a cewar ta,
Anan yabar su KB daga shi sai Aish sanda suka kamo hanyar zuwa gida,
Da kwatance tai ta yi mai har suka iso gidan su, Aisha din,
Koda ya Parker motar shi bai ce mata komai ba sai jiran yakeyi tafi ta yasamu ya wuce
Ita ta tsaya wani yanga kamar wace bata da lakka ajikin ta
A hankali ta dan waiga inda yake tana cewa nagode fa,sai wani lokaci ke nan kuma ,
Kai ya kada mata yana mai cewa No ba matsala ai ,,
Tana fita yafigi motar shi da karfi yabar uguwar zuwa, gidan su,,,,,,,,

Gudu yake shararawa a motar shi tanyar ta zuwa kudu, don kirar da yasa na gagawa daga abokan sanar shi saboda meeting din da zasu yi don kara wa mai farashi saboda harajin da gwaunati ta saka masu,
Shi kadai ne a cikin motar sai kidar da ya sa nawakar wani dan yaren su inda yake wa egwaii of Benin kirara,
Wayar shi dake gefen shi tai babirashon, hannu ya mija yadauko wayar hankali shi na saman titin kadan don yafara jin kamshin okene,
Ganin bakuwar noba yayi acikin wayar shi dan mamaki ya baiyana a fuskan shi kadan,
Don gani bakuwar nobar kuma yasan cewa wanan wayar sai special mutanen sa ke kiran shi da ita,
Kamar ya aje saidai ya dauka yana mai karata a kunen shi,
Muryan mace yaji tana mai sallama a cikin hausa,
Cire wayar yayi yadaga yana kallo don shi a bin ya bashi mamaki so sai wallahi,
Sai kuma yace kila wrong noba ce,
Karakara wayar yayi a kunen shi don yace is wrong noba,
Saida abin mamaki daidai lokacin da ya kara wayar akunen shi a lokacin ne, yaji mai maganar tana cewa
Yakake Joseph ?
Mamaki karara a fuskan shi ya ansa mata da lafiya,
Wake magana ya ke tambaya cikin mamaki, saida tai yar murmushi har yana jinta daga inda yake
Tace kana magana da Aisha Sanda ce,
Aisha Sanda ?
Joseph ya kara nanata sunan cikin mamaki a fili
Tace mai eh
Wace kuka hadu a wurin dinner din hamza har ka kaini gida,
Ok ok yace nagane ya kuke ta amsa mai da lafiya lau,
Yau nake tambayar KB kai yace min ka wuce sai tadan shake muryan ta kamar mai shirin kuka,
Tace shine bakazo munyi sallama ba katafi, ?
Maganar ta ba shi mamaki sosai don dai ya san cewa bawai wani sanin juna sukayi ba ko sabawa,
Amma sai kawai yadake duk da cikin mamakinta yake , ya ce , mata just sorry,
Kamar ta na ganin shi kai kawai ta gyada mai kamar yana ganin ta a fili,,
Wani irin ajiyar zuciya yayi yana mamakin maganar ta acikin zuciyar shi,,,
Ita ko Aisha wani irin shu,umin murmushi tayi bayan sun aje wayan azuciyar ta tana kiyasta abinda, take planing akai,,,,

Tsaye yake a cikin wani ma,aikatar tatan man petroleum, da ke kudu, yana son idon shi ya tabbatar mai da ko mota nawa daga con n motocin su , suka shigo,
Wayar shi tai kara noba ce ya gani babu suna don haka bai san mai wanan nobar ba,
Yadauka yana mai cewa hello,
Aka ansa mai adayar bangaren, jin muryan mace kuma ba hausa tana cewa
Hello mun wuni lafiya ya kwana biyu ?
Hello wake magana yace
Mamaki ne ya kama Aisha jin cewa har yanzu ashe bata shiga ba,
Ansa mai tayi da cewa Aisha ce daga KG,
Dan shiru ya biyo baya kadan sai can yake ce mata ok nagane
Pls ki bani dan lokaci zan kira ina aiki yanzu pls
Ba matsala race tana mai aje wayar cikin jin takai ci,
Amina wace ke kwance gefen ta har tagama wayar ta numfasa tace wallahi Aisha kina bani mamaki
Cikin dan jingina bayan ta da bangon dakin da suke zaune tace agani ki ko,
Amina tace a ganin kowa ma,
Kin fasan cewa ba musulmi bane wanan guy din don may zaki nace a kan shi dole sai kinyi halak da shi,
Daidai lokacin ta dauko wani abin gyara kumba daga cikin jakar ta,
Tafara dan kankare kumbar hannunta da abin sai can kamar bazatai magana ba tace
Kina nufin don ba musullumi bane bazan yagi rabo na ba ke nan,
Cikin mamaki kawar nata ke kallon ta don Aishan ta ba ta mamaki kwarai ta ya zatai mu,amula da wanda ba musullumi ba,
Gaskiya ita bazata iya ba, iyakar harkan ta ga musulumai yan uwanta,,,
Saboda yawan matsin da take mai dole yafara dan sakin jikin shi da ita har suna dan hira jefi jefi a waya,

Tafe take ciki uniform din su na girls day secondary school, sauri takeyi don ta isa gida, saboda ta samu ta shirya da wuri zuwa islamiya,
Don a kwaita da tsoron bugu bata son abinda ya tabi lafiyan jikin ta sam
Wasu "yan matane mutum biyu cikin shiga ta isa da nuna lokaci ke tafiya,
Tafiyar ta takeyi cikin sauri yasa sukayi kusan yin karo da daya daga cikin yan matan ne tai karfin halin cewa haba malam wani irin tafiya ne kikeyi babu ko tsari balle ki nuna ajin cewa ke ma mace ce,
Maryam wace duk saurin da takeyi bai hana ta tsaya wa guri guda ba cak,,,,
A hankali ta juya inda suke tadan kalle su murya a raunane tana mai cewa kuyi hakuri pls ban san cewa gurin ba zai muna bane,
Daga haka ta juya batare da ta kara cewa uffan bata ci gaba da tafiya sai dai maganar na kona mata zuciya,
Don may zasu ce ita bata da aji kodon batasa bujen da ya manne mata jiki bane, shine rashin wayewar da suke hange a gareta,


ZEEE MAKAWA
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
7⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA


Kusan duk wanda ke cikin wurin yana saye da rigar coat ce a jikin shi sai yan kali lqn ne ke da shiga irin ta hausan arewa ko su basu mutum uku ba daga cikin su,,,
Daga ni meetings suke yi kuma meeting ne ma tsauri don duk kan su fuskan su babu wallawa a ciki,
Kadan kadan hayaniya ke dan biyo baya musan man idan an fadi wani abinda ba,a yarda da shi ba agurin,
A wajen harabar gurin kuma maza ne kaitai majiya karfi kashi, kashi, da alamar security ne su
Sai wasu irin manyan motoci da sai inda idon ka ya tsaya,,,
Kowani kusurwa na wajen an zuba jamian tsaro birjik
Sunan mutum uku ne yanzun haka ake muhawara akai,
Mr Inok ,Ishaya noma sai Joseph,Emanuele,
Daya daga cikin su ake son ajewa a matsayin sectarianism din su na matasa masu harkan man petrol,
Daga karshen zaben ya fada akan Joseph wanda akasari mutane ba,su so hakan ba ,,,,
Wani dan Jos suka so Ishaya Noma,
Wanan mukamin ya jawo mai ci gaba sosai tare da duk wani wanda ke kusa da shi,
Abokan shi dana sanar shi sun hada mai party samun cigaba,
Mutanen kwantagora sun zo mai murna, don kusan duk, yan abokan su sun zo,
Wanan zuwan ya tayar masu da hankali so sai fiye da tsab manin su,
Don duk daukan da suke mai ashe yafi da haka a fili,
Sai bayan sun wuce ne Aisha ta samu wanan labarin kuma har an tafi, don haka ta lalashi Amina har ta yarda suka shiga motar kasuwa suka tafi har can,
Bayan sun isa ne, takira nobar KB take sheda mai cewa gasu sun iso garin,
KB yai mamakin jin wai ga su sun shigo cikin garin
Inda Joseph yake cikin abokan harkan shi KB ya rutsa yaje har cikin kunnen shi yai mai rada yaba sheda mai zuwan su Aisha
Sai da Joseph yadan nuna kaduwa don bai taba tsan manin zuwan su ba,
Wani yaron shi yakira yai mai nuni da KB yace su je tare azo da, su masauki
Su kan su sun yi mamaki kwarai da irin masaukin da suka samu,,

Washegari ne zaa ,gudanar da taron tayar murnan samun cigaban da su Joseph suka samu,
Inda taro yai taro don duk bakon daya zo dana kusa dana nisa Joseph yasa an karama shi da wada tacen abinci da na sha daidai gwargwado,
Fili na musan man yasa aka bawa abokan kurciyan shi a ce war shi, inda suka fito cikin musulunci tare da hasken musulunci a fuskan,
Sai mamaki su akeyi yadda sukazo taya,shi murna haka da yawa,
Anyi yan wasan ni da kuma raha kamar yadda akanyi inda wani abokin kasuwan cin shi da Lagos ya ba shi shawaran yai aure, hakana tunda Allah ya,wadata shi da arziki tun yana yaro,,,
A haka taro ya,watse , wa yanda suka zo daga nisa suka fara niyar komawa gida,
Sai, a lokacin Joseph yasamu kebewa da su Aisha cikin yar sakin fuska yake masu maganan,,,
Inda yai mata godiya sosai da kuma bata, appointment, nan da two weeks zasu hadu,
Aisha taji dadin wanan tafiyar da sukayi saboda irin guzurin da suka dawo dashi,
Tun wanan lokacin ya rage samun lokaci kamar da, yanzu ya kwana biyu baizo kwantagora ba duk da aiken da mahaifin shi Mr Emanuel ke mai na cewar church members na son ganin shi,
Aiki yakawo shi Abuja don haka yai amfani da wanan damar ya iso amsa kiran mahaifin shi,
Yan church din sun gudar da,addu,an su gare shi tare da fatan alheri zuwa gare shi,
Yaji dadin wanan adduan da akai mai don haka yaba gagarumin gudun mawa a church din nasu,
Tun jiya Sunday da suka dawo church din bai kara fita duk da yawan wayan da friends din shi keyi don jin cewa yana gari,
Bai samu fitowa sai bayan karfe biyu inda yace ma KB yazo su fita,
Don motar shi ta na bukatar, wanki sosai, don haka, yabar ta kanin sa ya fita mai da ita gurin wanki,,
A,saman mashin din KB suka fita, fitan da yasa mutane suka san cewa Joseph yazo gari,
Hmmm Dan Adam da kudi, kafin wani lokaci har yan kai koke sun isa gurin da suka san cewa zasu ganshi su yi maula,
Mutanen mu ho, idan zuciya ta mutu koma mutum na iya yi don kawai ya samu kudi,
Sai bayan sun gama maula ne sai a koma gefe ace ai dan kafirin nan yazo
Ai yanzu ba asan sanar da yake yi ba sai dai kudi ake ganin shi da shi ba a san ida yake samun su ba,
Wasu kuma, cewa suke yi ai Joseph mafiya yake yi yanzu sosai, irin na ya birni wanda ba,a gane akidar mutum,,,

Maryam tana tsaye a gaban mirrow tana gyaran hijab din dake a wuyan ta,
Issalam tazo ta bayan ta ta rugumay ta ,
Issalam kada fa ki sa in fadi kasa wqnan rikon da kikai min,,,
Yar wasan kokuwa suka fara yi da Issalam din kama ba zasu makaranta ba,
Anty Dije ce ta leko dakin jin su shiru da tayi dakin,
Cikin mamaki anty Dije tace, amma dai, maryam anyi uwar banza
Yanzu ku shirya ku wuce shine zaki buge da wasan kokuwa da Issalam,
Maryam na dariya daidai lokacin da Issalam ta kara kai mata damka ta na ko karin wai sai ta kayar da maryam a kasa,
Daidai tana fadawa kan katifa, tace ma yar nata ai yanzu zamu wuce insha Allah,,
Anty Dije na tsuki ta sake labulen dakin tace ai ku ,za,a daka a makarantan,
Har ta kai kofa ta tuna Assalam baya dakin kira ta kwada mai,
Daga bayi ya karba mata mama gani nan ina wanka,
Cikin mamaki jin cewa yana cikin bayi har yanzu yasa anty mamaki
Hanyar bayin ta nufa don ganin may yake yi a ciki har yanzu,
Sabulu yasa a fuskan shi dumu dumu, bai ko san shigowar uwar tashi ba ciki,
Sai lokacin da yaji hannun ta a jikin shi ta danko shi,
Wani irin ra,zananen ihu, yasa wa uwar don yana ganin kamar zata buge shi, yasa yaron yaka ihu,
Daga, maryam

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login