Showing 186001 words to 189000 words out of 255288 words

Chapter 63 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1392

rabo da ya sata a idon shi tun ranan da suka dawo unguwa a tare,
Cikin ladabi ta gaida shi ruwa ya ke tsiyayawa amma sai da mamakin gaisuwar da tai mai ya kama ta,
A nutse ya karba mata don zaka ce ai ba shi ba ne take gayar wa,
Sanin halin maryam da safiya tayi yasa ta fitowa ita ma daga dakin cikin fara,ar ta,
Tana gashe shi da shigowa tana kuma kokarin samun gurin da zata zauna a daya daga cikin kujerun falon,
Maryam wace duk a ta kure take saboda tana ganin cewa duk step din da tayi kamar a idon Yusuf yake,
Kitchen ta nufa gurin da Anty ke kokarin shirya mai a bincin shi,
Karban aikin tayi a hannun anty taci gaba da zuba mai,
A falon su ukune zaune a ciki Yusuf kewa Anty Dije, bayani akan tafiyar mahaifin su kasa mai tsarki,
Magana yake wa Anty dije a zahiri amma acikin zuciyar shi tunanen yakeyi maryam ce yake kallo a lokacin wace ke tafe ,
Ba komai yasa yake son yarinyar nan ba sai zaman ta irin macen da yake burin aure a rayuwar shi,
Kunya natsuwa, kamun kai, rikon Addini tarbiya da kuma sanin darajan mutane,
Itako maryam zancen da taji na tafiyan su baba shine ya ja hankalin ta,
Badon komai ba sai saboda adduan mahaifin su ke nan a kullun shi dai yatafi makka ya gano kabarin Annabi da Abubakar da nana fatima,
Duk addua sai kaji yasako wanan addu,an yau gashi Allah ya nufe shi da zuwa wanan shekaran,
Allah sarki baba ashe Yusuf ne mutumin da,zai yi sanadin sauke faralin ka
Tire din da ta dauko na abincin shi ta dire mai a gaban shi tare da kokarin jawo mai table din a gaban shi,
Nagode maryam ya ce a takaice tare da cigaba da zancen shi,
Wanan hali irin na godiyan Yusuf komai kamai kan,kantar abinda kai mai sai yayi ma godiya,
Muryan maryam ce ya dakatar da shi daga bayanin da yake wa anty, ta
A zuba ma ne ko ba yanzun zaka ci ba ta tanbaya cikin dukar da kai kasa,
No, barshi kawai na gode ya ce yana mai daga mata hannu,
Ta mike a hankali ta juya zuwa kitchen don ta rufo kofan da tabari a bude,
Ido Yusuf ya kara binta da shi yana kara mata kallo azuciyar shi ya na,addua Allah yasa haduwar su ya, zama alheri a rayuwar su da haka yadan lumshe idon shi,
Safiya wace ke gefe kuma tana nazarin duk halin da Yusuf din ke ciki ta dan murmusa daga gefe, batare da,sanin kowa ba,
Maryam wace a lokacin tadawo cikin falon tana kokarin shigewa daki safiya ce ta dan jawo ta da fira,
Tace maryam wayan nan naki ko yana yi yanzu ya daina hooking din da yake yi,
Tafida hakan cikin rashin nuna wani abu a fuskanta,
Sam mutum zai dauka cewa bada wani manufa tayi zancen, ba,
Wanan maganar na safiya yadan sa maryam din dawo wa falon
Gurin da safiya take a zaune ta nufa tana mai cewa cikinnmuryan nan na ta tankar ansa ta magana,dole ne,
Kinsan yanzu kira kawai nakeyi da shi sai kuma received din called, kawai,
Anty Dije ta mike a hankali tana cewa barin dan shiga cikin gida kafin ka gama yanzu zan dawo zan tura yaro can gidan mu gurin babane,
Anty dije tana fita gidan sai Safiya tace au na fa manta da cewa za,a kirani nabar waya daki cikin sauri ta mike zuwa dakin,
Tafiyan safiya yasa akabar su su biyu sai dan shiru ya ziyarci gurin abincin shi yake ci hankali kwance abinshi,
Jin shiru ya dan ratsa gurin yasa lokaci guda Yusuf ya juyo yana fuskantar ta,
Ba tare da yakalleta ba yana mai ci gaba da cin abincin shi yace,
Maryam kwana biyu lafiya kike ko ?
A bazata maryam taji maganar a lokacin hankalinta nagurin wayar ta da ke a hannun ta,
A hankali tadago kanta sai taga cewa ai su kadai ne agurin kawai,
Ko bakya magana ne kina tsoron kada na gudu dake tunda ba ki san koni waye ba ko, ?
Ita dai maryam murmushi kawai ta dan sake wanda iyakar shi iya fuska, batare da tayi magana ba,
Shima Yusuf di kamar yadda tai murmushin hakan ya yi nashi,
Dukawa yayi yaci gaba da,cin abincin shi a hankali kamar yadda yake yi tun farko,
Sai da ya kurba ruwa yadan jawo tissue yadan goge bakin shi ,
Sanan yace maryam nasan cewa kina mai jin zafin abinda A,A dinki yai maki ,
Maryam duk abinda babba zai hango yaro ba zai taba hango shi ba,.
Don haka kibar wa Allah al,amarinki gare shi yafi duk wani tashin hankali da zaki saka kan ki a cikki,
Ni har ga Allah idan zancen baba bai maki ba zan iya hakkuri da maganar Allah zai ban wata,
Duk da nasan cewa nadade ina mai rokan Allah akan yaban mata daidai ni ,
Bako wani irin rayuwa nake bukata daga mace ba akwai wasu hallaiya danake son macen da zan aura ta kasance dasu,
Sai ga shi ubangiji ya nufi baba da alkawaranta min
Da na diba sainaga cewa aiduk wanan abin da nake bukata kina dasu har ma kin zarta wanda nake bukatan,
Maryam kafin lokacin da baba zai bukaci jin hukuncin da muka yanke akai
Idan har kinsan cewa bakya sona ko kuma kinada wani still wanda kike so ,
To ki fada min tun zancen baiyi nisa ba saboda ni mutum ne da bani son inwa babba karya ko yaudara,
Dan shiru ne ya kara ziyartan gurin shiko Yusuf yana saurarenta ne ko za tai magana akan tambayar da yai mata,
Amma sai yaga alamar baza tai magana ba ba zata ce wani abu ba sai wasa da wayan hannun ta da takeyi,
Maryam yakara kiran sunan ta cikin wani yanayi da yasa ta rikicewa amma sai tadaure tana mai dago kai ta dan dube shi ,
Yanayin da tagani ga fuskanshi ba wasa aciki a lokacin don haka tai saurin dukar da kanta kasa tana sauraron shi,
Ki daure ki fada min ra,ayinki a ganay dani amna dan girman Allah ina rokon ki da ki fada min gaskiyar abin dake zuciyar ki,
Kada ki duba abinda ke tsakanin mu da baba ko Anty Dije,
Saboda nayi alkawari bazan taba auren macen da bata so na ko wace bana ra,ayina ba,
Ni mutum ne da bani da ra,ayin yin aure ,aure a rayuwa na,
Don haka sai wace nasan cewa tana sona ina son ta zan aura bawai don ra,ayin wani ba can daban,
Pls kada kuma kiji kunyar gaya min gaskiya don nasan ba dadi ka kalli mutun face to face kace mai baka ra,ayin shi,
Amma ni agare ni gara hakan da ka yaudari mutun kafada mai karyan don kawai yaji dadi,
Don haka maryam ina sauraren ki ki fada min ra,ayinki agamay dani pls ?
Maryam wace kanta ke aduke lokacin a cikin zuciyar ta hakika maganganun uncle gaskiyane,
Amma kuma taya zata fada mashi cewa yanzu ta amince dashi kai tsaye ya yarda da ita,
Bayan yana sane da irin yadda akai ta kwasa da ita akan shi,
Dakuma irin yadda son A,A ya ke azuciyar ta har bata iya boye,
Tambayar ta ya karayi sai taga ai kawai tafada maigaskiya zai fi,
Abin mamaki kuma sai taji bakinta yai nauyi ta furta mai ko wani irin kalma,
Saidai kuma i zuwa yanzu karyane tace bataji wani abu akan Yusuf din ba ,
Saidai tana kokarin karyata haka din da takeji a kan shi tun bayan dogon sharhin da safiya ta zaunar da ita tai mata,
Gashi kuma ya tsure ta da idon ta rasa yadda zatai magana har ta fada mai gaskiya,,
Ganin baida niyar kauda idon shi gare ta dole ta daure ta ce ma wani abu saboda tasan yin shirun nata baida mafita,
Kasa,kasa yaji muryan ta tana cewa kasan ai aure nufin Allah ne idan har Allah yakardara ni matar kace kamar yadda mahaifina ke bukata to,,,, sai kuma tai shiru batare da kara cewa komai ba,
Murmushi Yusuf din yayi yadan gyara zaman shi yace Uhum maryam kifitar da duk wani kunya da shakku kiya magana don har yanzu banji kinyi maganar da nake son ji ba
Tabbas maryam nasan aure nufin Allah ne, amma ni abin da nake son in ji shine Yusuf ina sonka ko kuma a, a yusuf bana sonka,
Da sauri tadago kanta dake duke takalle shi shima din ita yake kallo sai yadan daga mata gira yace yes,haka din ne mana gaskiya,
Hmmm kawai tace saine kuma tace, amma dai ai nayi maka bayani ko ?
Tuna dai abin da kikace a baya kawai kince Aure nufin Allah kuma mahaifinki ke bukantan kiyi,
Don haka kenan bake ke bukatan aurena ba har yanzu maganar mahaifinki ne kawai kike bi,
Cikin sauri tadago kanta don jin abindayace tare da saurin cewa Injiwa ?
Amsan da taba shiya dan sa shi dariya dan haka sai ya mike tsaye daga inda yake zaune,
Gurin da take nufa kamar daga sama taji hannunshi acikin nata saikuma taga yakai tsugune agaban ta yace,
Will you marry me ?


ZEE MAKAWA YELWA,,
[4/28, 5:35 PM] β€ͺ+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
7⃣5⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI

Barka da jumma,a yan uwa musulmai masoya novel din furen juji,
Allah ubangiji ya karawa Annabi Mohammad, S,A,W daraja,πŸ‘πŸ‘πŸ‘



Jin hannun shi cikin nata, ya runtse, cikin nashi abinda bai taba faruwa da ita ba, ke nan,
Aiko nan take jikin ta yafara rawa, don wani irin mugun tsoro ne ya shige ta alokacin,
Shiko Yusuf yana ganin haka ya fahinci halin da take ciki hakan ya sanya shi kara rike hannun nata sosai,
A hankali tadago idon ta da suka sauya zuwa na mai kuka, ta na mai wani irin kuka,
Shima kallon nata yakeyi cikin cikin wani irin yanayi,
Ido cikin ido kowa ke kallon dan uwa, wani irin kallo da kowa da abinda zuciyar shi ke fadi,
Kallonta yake yi ita ma dai kallin nashi take tin cikin tuhuma da kaguwa ya sake ta, ba tare da sun daina ba,
A hankali ya dago hannun zuwa bakin shi ya dan subban ta,
Cikin wani irin sauri maryam tai kokarin jaye hannnun nata da yasha riko,
Sai kallon kofa takeyi da alamar kada wani yazo ya riske su a hakan, ta ke wa gudu,
Safiya ce tai murya tankar mai waya tana cewa hello,
Ai ko nan take wani irin kunya ya lulube maryam irin kunyar da bata taba jin shi ba don gani take safiya ta ga halin da suke ciki,
Cikin sauri da wani karfi ta fisge hannun ta yi masa wani irin kallo na don may, tai wani kasa da kan ta alokaci guda
Ko shi Yusuf din sakin hannun ta yayi batare da bata lokaci ba don a zaton shi fitowa safiya zatayi a lokacin,
Ya koma a kujerar da ya taso da farko ya dan kai bayan shi a kai ya kwanta,
Ya na mai da numfashi da sauri da sauri kamar wanda yai wasan tsere,
Jikin shi yaji yai mai wani irin sanyi gaba daya, don irin yanayin da ya riski kan shi alokacin da ya rikewa maryam hannu,
A lokacin safiya ta kara so falon tawa maryam din wani irin kallo cikin wasa tace lalai ma maryam,
May uncle ke fada maki haka da har kika mantacewa ina cikin daki tun dazu,
Gashi har nagaji da jira ki na kai ga fitowa don ba gadin daki nazo maki ba,
Kallon Yusuf din tayi wanda idon shi suke a lumshe tankar ba shi ba ne wanda ya dagulawa kawar ta lissafi har take ba tun kuka,
Kallon shi tayi kamar ta yi mai magana sai kuma ta fasa kusa da maryam ta dan zauna,,
Don ta kawar da shirun da sukayi a falon kowa da abinda zuciyar shi ke sakawa,
Safiya, ce ke kokarin jan maryam da dan fira dan ta sake jiki,
Maryam ta kasa cewa safiya din uffan sai da kai kawai take iya ansa mata,
Γ€nty ce ta shigo dauke da wani ruba tab da wake mai ruwan milk a ciki,
Maryam wace sai yanzu tai magana tun bayan halin da ta shiga, don haka har sadiya tagaji da fira da ita,
Yusuf wanda ke zaune a gefe batare da yace wa kowan su komai ba ,
Sai tunanen zuci kawai yake yi, a cikin ranshi duk ya dabur ce,
Tsam yamike yana mai yiwa Anty sai anjima jiki ba kwari,
A lokacin da ya isa gidan shi zama yayi saman wani kujera, sai tunane kawai yake,
Zuciyar shi tace mai Addu,a ce kawai ta kamance ka salim,
Ka roki Allah shine kawai zai kawo ma ka mafita ,
Abinda zuciyar shi ta dinga raya mashi ke nan a lokacin,
A take kuma ya amince da hakan, don haka da sauri ya mike zuwa bathroom din shi inda ya dauro alwala,

Itako maryam bayan fitan shi suka hada ido da safiya sai kawai safiyan ta kwashe da dariya
Wani dan filon kushin dake a gefen maryam ta dauka ta jefawa safiya din inda ta cabe shi a hannun ta,
Tana ci gaba da yi,wa maryam, din dariya har da kyalkyatawa,
Anty dije tagane may suke nufi amma sai kawai tashare su tankar ba ta fahince su ba,
Don ta kauda zancen sai cewa tayi dan wake take son yi da wanan waken da aka bata gashi kuma milk colour ne zaifi kyau ga dahuwa,
Sai a lokacin safiya tadan rage sautin dariyar ta tace wa anty aiko zai yi kyau so sai da dan wake ,
Har zuwa yamma Safiya na gidan sai a lokacin Jibrin yazo ya dauke ta ya mai da ita gidan su,
A gogon dake false n gidan ya nuna goma saura na dare yanzu,
Hakan ya ba wa Anty dije tabbacin cewa Yusuf ba zai shigo cin abincin dare ba ke nan yau,
Don haka ta umurci maryam da cewa ta rufe masu gida don dare ya yi ko,
Wanka tayi ta shirya cikin kayan barcin ta wando da riga masu ruwan light green,
Ta daure kanta da ribon kamar kullun takawo gyale dan karami ta daure kan nata dashi,
Zaune take bakin gadon su tana adduan shiga barci kamar yadda ta saba,
Wayan tane yai kara a lokacin alamar kira ya shigo mata,
Ta dan jima tana kallon wayan tana tunanen may zaice mata kuma yanzu,
Har wayan na batun katsewa takai hannun ta tadauka tare da yin sallama cikin wata murya,
Muryan wace ta sa Yusuf, kara rikicewa da jinta har ya rasa irin ansar sallamar da zai mata,
Tunane ya farayi bayan ya karba wayan yana mai cewa,
Shin wai dama haka wanan yarinyar take tun farko ko dai yanzu ne ta koma haka,
Jin muryan ta tana gaishe shi yasa shi saurin tuna cewa a saman layi yake fa,
Ansa gaisuwar na ta ya yi cikin wani muryan da zaka zaci ba ta shi bace,
Shiru, ne yabiyo bayan gaisuwar amna sai Yusuf din yai kokarin kauda shirun nashi,
Maryam ina abinci na ya tambaye ta cikin wani murya tankar ba tashi bace,
Uncle abincin ka yana kitchen mana ko kazo ne mu bude gida,
Sai da yai murmushin jin yadda ta rude a lokaci guda,
Ya ce No na hutar da ke ni ina gidana ai, yau bana jin cin abinci sam,
Kawai sai maryam ta tsinci kanta da tambayar shi ko saboda may ?
Ya ce saboda ke maryam
Yau kin sani a cikin wani yanayi kin ruda min zuciya ta kwata, kwata bani da sukuni yau,
Maryam yadda tayi tankar Yusuf yana ganin ta a fili don nuna kan ta tayi tana tambayar ita,?
Sai da yadan lumshe ido shi tankar maryam tana ganin shi, a fili itama,
Yace Yes of course ke, maryam don kin sa duk na wani susuce akan ki,
Idon ta tadan runtse saboda bakon ya,na yin da take ji a yau,
Uncle din ya koma mata tankar wani bako wanda bata taba gani ba arayuwan ta,
Daga haka yaci gaba da dan mata kalamai masu dadi a hiran nasu,
Maryam wace sam ta kasa sakin jiki da shi sai ansawa da Eh
Ko Um,umm takeyi sune kawai ansar nata da take iya bayar ba,
Harzuwa dan wani lokaci sannan yai mata sallama,
Sannu sannu ya dinga dan jan ta da hira tana dan sake jik wani lokaci tana hira dashi sama sama a kunyace,
Wanan dan kwanakin da sukayi dan sabo maryam ta kara haddace ko waye Yusuf din,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login