Showing 153001 words to 156000 words out of 255288 words
Chapter 52 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete
kai wanan yaron Allah yai maka albarka kaji,
Ban san may zan maka in saka ma da alherin da kake muna ba,
Kai haba dai baba ai duk yiwa kai ne wanan baba idan ban maka ba wazan mawa irin haka
Dakai da iyalen ka kun nuna min kauna da yarda a fili baba bakku taba yi min wani abinda zai nuna min cewa ni badaga cikin zurian ku nake ba,,
Anty Dije ce take ce wa baba kako ji yadda akai mai, a gidan yarinyar da yake bida,
Ta, ce wallahi baba mugun zagi akan wai iyayen Yusuf ba musulmai ba ne,
Nan dai ta kwashe komai ta shedawa baba yadda akayi,
Baba sai faman kada kai yake yi don al,ajabin maganar da yaje ji
Baba yace wai ina ki ke, Dije ?
Ta amsa da cewa naam baba,
In har abin ya zama haka ga kaunar shi nan ai sai su shirya ko ?
,,,,, ,,,,,,,, ,,,,,,,,, ,,,,, ,,,,,,,,
SEENABU ZEEE IDRIS MAKAWA,
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
6⃣3⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
IYAKA NA ABBUD WA,IYAKKA NA,STA,IN
Gyaran muryan da baba yayi ne yadawo da duk kusan wanda ke acikin falon da tunanen shi,
A hankali maryam wace ga zafin ciwo ga kuma nauyin maganar baba a tare da
Ta dago ganin ta ido taf da hawaye wani na bin wani,
Tace cikin kwantar da murya baba may zai sa ai mun wanan acikin yan uwana ?
Baba ko don ban da uwa a gidan zai ai mun irin wanan acikin mu,
Baba kasan cewa ina da wanda nake so zan aura don may za ai min wanan hadin tankar wace bata da gata,
Murmushi baba yayi kafin ya kauda kai ga kallon mamakin da yake yar tashi da yai bugun gaba da ita,
Sai baba bai taba tsan manin cewa maryam zata iya yi mai haka ba,
Maryam wani irin daci taji a zuciyar ta ya wani tokare mata makoshi
Baba kaji tausayi na kada kasani abin da ba ra,ayina ba,,,,,,,,
Bata kara sa maganar ba Anty Dije ta daka mata wani irin tsawa a lokacin,
Murmushi baba yakara yi yace maryam may yai zafi haka ,
Ki kwantar da hankalinki ki bi zabin da nai maki zaki ga alheri a cikjn sa
Ni mahaifin ki na bazan cutar da ke ba har abada, ke dace zan iya bugun gaba dake a hanlin yanzu ba tare da na samu wani matsala ba,,,,,
Kasa karasa maganar yayi saboda ta makale mashi ,,
Sai kawai yamike batare da cewa kowa kallah lahu ba ya mike yafita
Yusuf wanda ke zaune tun fara zancen kamar ruwa ya cinye shi bai ce kala ba,
Ya mike yabi bayan baba,
Don yaga ya fita lafiya a irin yadda ya bar gidan a cikin bacin rai,
Wajen minti talatin bayan fitan Yusuf da baba,
Ba wanda ya kara, magana kowa da abinda yake sakawa azuciyar shi,
Jiki babu kwari maryam ta mike tayi cikin dakin su inda tana shiga ta rusa wani irin ihun kuka cikin ban tausayi,
Sai da tayi kukanta ta ci mai isar ta batare da kowa ya shigo gurin ta ba,
Anty Dije ce ta shigo dakin da sallamar ta gami da tura kofan,
Dauke take da kulan abinci da kwayoyin maganin maryam,
A kwance maryam din take a takure, guri guda can gefen gadon ta,
Maryam takira sunan ta, kamar wace zatai kuka itama don ganin irin yana yin da yar uwar ts ke ciki,
Wani irin kuka maryam din takara sawa wanda yasa jikin Anty Dije makyarkyata,
Saboda sam bata taba ganin maryam din ta acikin yanayi irin haka ba,
Hasalima dai sam ita bataso baba ya yanke irin wanan hukuncin akan yar uwar ta ,taba,
Maryam ta kara ambatawa cikin sarkewar murya tana cewa,
Zauna tayi a bakin gadon dab da yar kaunar na ya
Hannu takai saman jikin maryam din wace jikin ta a hanlin yanzu yai wani irin zafi radau,
Ido ta tsura mata sai kuma taji saukan hawaye ita ma a idon nata,
Magana ta fara yi kamar haka,
Kiyi hakkuri maryam da hukuncin da hukuncin da baba ya zartan batare da yin wata shawara akai ba,
A halin yanzu babu abin da zamuyi akai sai dai mu bari har zuwa lokacin da hankalin shi ya kwanta,
A hankali maryam ta taso cikin yanayin jin jikin da takeyi ta kwantar da kanta a saman ciyar yar nata,
Tace Anty da gaske ko dai baba baya so na ne kamar sauran diyan shi?
Da sauri Anty Dije ta toshe mata baki,
Hawaye wasu na bin wasu ta, ta ce maryam kada fa don rayuwan ki ya baci, ki kama sake maganar da bai dace ba akai,
Yanzu karbi magani ki sha maryam insaha Allah zan san yadda na bullowa baba yafita batun wanan zancen,
Anty don Allah kada ki bari a rabani da A,A saboda ina son shi kamar yadda yake so na,
Wani irin kululu cikin ta ya yi tace subbahanallahi maryam ai komai na Allah,
Murya kasa,kasa tace irin ta may jin jiki tace don Allah anty ki taimaka min kada baba yai min haka pls Anty,
Ta kara riko hannun Antyn na ta tarike su gam tana she,shekar kuka,
Da kyat Anty maryam ta samu maryam ta dan sha ruwan kunun da takawo mata tare da bata maganin ta don ta sha,
Da kyat ta hade maganin da take ji tankar tana hadiyan guba ne a lokacin,
Yusuf wanda ke jin kanshi tankar zai tsage mai gida biyu, a lokacin,
Tunda yafita waje ya hango baba har ya sha kwanar xuwa gidan shi, ko,
Don haka sai yaji sam baya da bukatar komawa cikin gidan,
Kawai sai ya sa kai ya shige motar shi kan shi yake ji yana mai wani irin dan ciwo, ciwo kadan kadan
Sannu sannu yana jin muryan maryam yadda take wa mahaifin ta kuka
Abin na,soya mai zuciyar shi ciwon kan shi ya na karuwa a lokacin,
Yana shiga gidan shi yaron gidan shi mai kula da gida yana ganin shi ya taso cikin murna
Amma yau sai ya kula da cewa Yusuf maigidan nadhi bai a cikin hankalin shi,
Don haka bayan sannun da yai mai sai kawai ya fara kwasan kayan maigidan nashi yana shiga da su ciki,
A hankali ya tura kofan falon sanyi da kamshi ne suka daki hancin shi duk da bacin ran da yake ciki bai hana ya jinjina wa yaron mai kula da gidan ba a irin yadda yake kula mai da gida,
Saman kujerar falo mai kama da Royal chair ya fada a saman kujera daya,
Yana dafe da goshin shi da yake ji yana kokarin tsage mai gida biyu,
Hannin shi guda dafe da goshin shi kan shi na dage yana yana kallon sama,
Idon shi a rufe suke ga kuma hannun shi dafe da goshin shi,
Maganganun da maryam taita jero wa mahaifin ta a gaban idon shi suke mai yawo a cikin kwakwalwa,
Baba may zai sa ai mun haka a cikin yan uwa na da kowa ?
Baba ko don banda uwa a gidan za aimun irin wanan a gidan,
Ritse idon shi yayi maganar na ci mai rai,
Baba kasan cewa ina da wanda nake so yake so na, zan aura,
Don may za ai mun irin wanan hadin tankar wace bata da gata,
Subbahanallah ya furta ya furzar da iska mai zafi daga bakin shi irin iskan da ke sauke relief a lokaci guda,
Shi Yusuf mai ke faruwa dashi ne haka da har zai zama abin kyama a lokaci guda,
May mutane ke kyama agare shi da har suke gudun shi haka
Yau gashi har da mutanen da a yanzu yake jin su tankar wani sashe na cikin jikin shi,
A gaban idon shi maryam ta nuna bata kaunar shi sam
Duk da dai shima din bawai kaunar ta yakeyi ba, amma ai bai dace tai wanan kalaman a gaban shi ba,
Wata zuciya tace, kyamar ka takeyi ita ma ai,
Da sauri kuma zuciyar shi ta raya mai da cewa kai yarinya ce shatab, shi ya kawo hakan,
Kawai sai yaji wasu hawaye masu dumi suna bin fuskan shi,
Yau shi Yusuf dake jin kanshi a cikin dubu akewa gudun asali irin haka,
Gam ya ritse idon shi mai yasa mutane ba su da fahintar maganar Allah ne,
May aciki don shi yana musulmi yan uwan shi na Christian,
Har kan su da ban tashi daban kuma ma ai yana fatan a ce su ma sun musulunta, din
Karan da wayar shi tayi ne yasa shi sauri dagowa daga cikin zurfin tunanen da ya shiga,
Anty Dije ce ke kiran nashi kamar ya share ta sai yaga rashin kyautawar haka fon dai ita batai mai komai ba ai,
Yana dauka batare da ko sallama ba yaji muryan ta tana cewa,
Yusuf kana ina ne wai baka shigo ba tun da zu gashi dare nayi,
Sai a lokacin da yaji tace hakan ne ya daga ido ya dubi window dakin yaga gari duk ya gauraye da duhu,
Zubur ya mike saboda sallah da bai yi ba na magrib da isha,i
Cikin yanayin magana wani iri kamar wanda ya dade yana jinya
Yace ina gida ai Anty bazan samu zuwa ba zan dan fita unguwa ne yanzu,
Ba,wai ta yarda da zancen shi ba ta amsa mai da cewa, ok to Allah ya tsare,
Ya ansa da fadar ameen yana mai kashe wayar shi saboda bai son yakara koda wani kalma ne a kai,
A dadafe ya isa cikin kuryan dakin shi bai tsaya komai ba yafada bayi don ya gabatar da alwala yai sallah,
Sai washegari yasamu shigowa gidan anty don ya karya,
Duk da bai ganta ba kawai sai ya tsunci kan shi yau da jin nauyin sukamar may daga Anty har Maryam din,
Saboda dai shi yanzu yasan cewa abin tausayi yake, don har da yar karamar yarinya tana kyamar shi,
Gaisawa kawai yayi da Anty sai yaji bama zai iya hira da ita ba yau sam irin yadda su ka saba yi,
Ita dai Anty Dije tsayin lokaci tana zaune a gefe tana shayar da yaron ta,
Babu wanda ya iya cewa kala daga cikin su falon yai shiru, in ka cire karar na,urorin dake aiki a ciki
Sai ko ajiyan zuya da,su keyi a jefi jefi,
Anty Dije ce ta kau da shirun na yadda taga Yusuf din ya daure fuska yakuna sauya mata yau
Tagumi ta dan zuba tana mai kura mai idon ta
A gogon dake daure a hannun shi, ta ga ya kalla,sai kuma ya ja wata yar tsuki,
Anty Dije ta dan dago kai ta dube shi tace haba Yusuf ban zaci cewa kaima zaka biyewa halin yarinta irin wanda maryam tayi jiya a gaban kowa ba,
Murmushin yake ya ka,karo a fuskan shi yace haba Anty ba wanan zancen ke damuna ba
Sada kan shi yayi kasa kamar mai tuna nen wani abu mai nauyi,
Kan shi ya dago daga kasan da yasada din yana mai kokarin kara kakaro murmushi,
Murya kasa kasa ya ce Anty na fahinci kowa na guduna yanzu,
Kasan cewa ta acikin al,umman hausawa kuma musulmai,
Maryam wace tun shigowar shi gidan idon ta biyu tana sauraren su,
Wani irin abune ya soki kirjin ta don jin abinda yace a gamay da kan shi,
Da sauri Anty Dije ta tare shi da cewa haba Yusuf ban taba tsan manin jin wanan kalamin daga bakin ka ba,
Maryam sam ba nufin ta ke nan ba a,kan ka, ita irin yadda baba yai matane a gaban mutane zai ce wai ya baka ita idan kun shirya,
Alhalin kuma yasan cewa tana da wanda take so tun farko a rayuwan ta,
Sakin wani murmushin takaici yayi yace, haba Anty akwai fa alamar tambaya a irin yadda maryam ta dinga magana a gaban baba jiyan,
Sanin halin ta da kowa yayi cewa yarinya ce mai ladabi ita,
Wani irin tausayin shi Anty Dije taji a lokacin da yake wa yan nan maganganun,
Da sauri tace Yusuf na fadama cewa ka daina irin wanan tunanen hakan zai saka shiga cikin wani yanayi har ka fada sabon Allah,
Baice kala ba again sai ma mikewa da yayi da nufin wucewa alokacin
Tambayar shi Anty tayi cikin kulawa kamar yadda yaya takan yiwa dan kanin ta idan ya shiga wani hali,
Tafiya zakayi yanzu baka bari har zuwa anjima idan rana yai sanyi,
A nutse yace mata gida zan koma in dan kwanta,
Sai dai abin da bata sani ba shine cewa daga nan gidan ta Abuja ya wuce direct.
Sai zuwa dare da bata ga ya shigo ba tai mai waya yake sheda mata cewa ai gashi ya kusa shiga garin Abuja
Sosai ran Anty Dije ya baci sai kawai ma taji bataji dadin wanan zancen da baba yayi ba,
Don kada ya tarwatsa masu zumuncin su da suka dade sunayin abin su gwanin ban sha,awa,
Tafiyan shi ya yi wa maryam dadi sosai don koba komai zata dan samu enough time na tunane ta dan sake jikin ta,
Sati biyu da wannan zance maryam ta dan sake jikin ta yanzu saboda taji ba wanda ya kara zance,
Saidai matsalar ta kawai shine baba, don har yanzu bai karba mata gaisuwar ta kamar da,
Amma hakan baisa ta damu ba don ta san cewa wata rana zasu shirya ai,
A cikin haka Anty Dije ta samu baba da zancen don ganin irin yadda ya dauzafi ga maganar,
Baba yace duk wanan abin da kikaga nayi Dije don Allah nayi sai kuma na biyu don ke da shi yaron,
Yanzu wa kike ganin zai dauki yar shi yaba shi kai tsaye a irin yadda aka san halin mahaifin shi,
Amma idan maryam ta aure shi duk wani mai ganin cewa baida asalin kwarai zai daina hangen hakan,
Ko don ita matsayin ta na yar kasa zai sa jama,a da dama kara hurda dashi har addinin,shi yakara karfafa,
Ajiyan zuciya Anty Dije tayi don jin irin hikimar da yasa baba yankewa yar kaunata dakuma Yusuf wanan irin matakin,
A gaskiya itama zata dauki nata irin matakin gurin, ganin cewa ta yi wani abu akai don karfafa wanan zancen,
Yusuf yana Lagos saboda wani aikin da ya tafi yi gurin, depot din su,
Don yanzu ya koma harkan business din mai sosai fiye da da,
Don an gyara masu gurin matatar man su, da suke business tun farko,
Wayan Anty Dije ne ya shigo mai alokacin yana tsaka ga aikin a cikin wasu takardun su,
Fuskan shi dauke da yalwataccen fara,a tankar Antyn tana kusa dashi a,lokacin,
Nan ya shiga sosai ranan sukayi hira inda yake sheda mata cewa yanzu businesses din shi na Lagos ya tashi sosai zai ci gaba da harkan man petroleum,
Tai mashi murna sosai sai daga karshe ne takira sunan shi a cikjn natsuwa, hakan ya tabbatar mai da cewa za tai serious magana dashi ke nan,
Anty Dije tace Yusuf may yasa yanzu ka daina duk wani korin irin yadda kake yi gurin sada zumunci da sauran su,
Shiru yayi a lokacin da take maganar tankar bai saman layin sai da tace hlo taji ya ansa, sanan ta tabbatar da cewa yana saman layin,
Amsa mata yayi da fadi, No, wallahi ba hakana bane,
Kawai dai aiyuka ne sukai min yawa amma da zaran na samu chains zan shigo insha Allah,
Shigowar su Assalam yaji muryan su ta cikin wayar,
Hakan yasa shi cewa abashi yaran su gaisa da su,
Sosak sukayi hira da su Assalam din inda yaran suka ce mai ga Anty Naimat da little Mum,
Maryam da ke kokarin kwankwatsa waken da za suyi miya a cikin turmi, tai wani irin saurin juyowa cikin watsa masu harara,
Ya dade da Naimat suna waya sai daga baya taba maryam din,
Wace a lokacin tana bakin famfo tana wanke kayan miya,,
A hankali yakira sunan ta yana mai tambayar ta lafiyan jikin ta inda ta ansa mai da cewa da sauki
Ya kuma tambaye ta ya karatu ta ansa shima da fadin lafiya lau,,,,
Sai kuma shiru ya biyo bayan zancen don baida a bin fada mata kuma,,,,
SEENABU ZEEE MAKAWA
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
6⃣4⃣
ZAINAB