Showing 117001 words to 120000 words out of 255288 words
Chapter 40 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete
Yusuf, arayuwar ta,
Kin gane ne sadiya ki bari zan mashi magana insha Allah zaki kiji ko mai, a guri na,
Sadiya ba tasan lokacin da ta fara zabgawa Jibrin godiya ba,
Murmushi yai mata kawai, yana mai jin tausayin ta,
Don da da farko haushi take ba shi akan zancen amma yanzu yaga da gaske takeyi son Yusuf takeyi,
Jibrin bai ja wani dogon lokaci ba gurin tuntubar Yusuf da zance inda yakara mai bayani akan Sadiya, din,
Yusuf bai wani bashi amsa ba cikakke sai dai yar murmushin dayayi wanda murmushhi wani part ne na rayuwar shi
Don haka sai Jibrin yafara tuntubar Γnty Dije don yasan cewa ita abokiyar shawar Yusuf ne kuma,
Kwarai Anty tai murna da wanan labarin don har ta kasa boye farin cikin ta,
Rana ake kodawa saboda giragizai da suke yawo a sararin samaniya,
Garin sai yadauki zafi gashi NEPA sun dauke wuta,
A gajiye maryam ta dawo, saboda zafin ranan da akeyi duk ya kode ta,
Γnty Dije wace ke ta farin ciki da labarin da Jibrin yaba ta tana zaune da Abubakar sai waka take mai,
Hakan yasa maryam gane cewa, Anty ta cikin farin ciki yau,
Takalmin da tasa na Tommy, shi take ko,karin cirewa,
Ta wallwale daurin dake a kan ta da tayi na rolling, ta wurga a saman kushin,
Fridge ta nufa ta dauko, ruwa a cikin leda sanan tadawo inda anty take zaune ta zauna tana zukan ruwan a hankali,
Sannan tai yar ajiyar zuciya saboda sanyi da taji yadan ratsa ta alikacin,
Anty naga kina wani farin ciki ne yau tunda na shigo, ?
Marya na kokarin, mikewa tsaye, take tambayar yar nata, .
Kedai maryam kani na ya kusa zama ango shima,
Wake nan Anty ?
Maryam ta tanbaya a lokacin kai tsaye,
Yusuf mana,
Taba ansa a takaice, Maryam wace a lokacin ta kusa kai wa tsakiyan falon sai ta juyo tana yiwa Anty nata kallon mamaki kawai,
Yusuf fa Anty ?
Shifa inji anty sai kokarin yiwa Abubakar wasa takeyi,
Cak Maryam ta tsaya don karasa sauraron zancen da anty ke fada mata,
Wallahi ke dai maryam ina wanan cousin sister din ta Jibrin da muka gani a gidan atika,
Dammm Maryam taji gabanta ya bada sai dai bata san ko na maye ba dai,
Sai kuma ta yake baki tana cewa Allah yasa dauka,sirious, dai,
Daga haka tasa kai ta wuce zuwa cikin dakin ta kawai,
Tana shiga daki ta fada saman gado ta rub da ciki ,
A,cikin kasala ta dan jawo filo zuwa kan ta, sai da ta kwanta da kyau kanta na sama yana kallon silin sanan .
Maganar Anty yafado mata arai,
Azuciyar ta tace kai badon aure hafin Allah bane da sai tace, gaskiya basu dace ba sam,
Ita wanan Sadiyar da bata da marmari sam duk yadda kake bata iya gaishe ka ko kuma ta nuna ma sakin fuska,
Ire iren tunanen da taitayi ke nan har zuwa wani lokaci,
Don kan ta tamike zuwa watsa ma jikin ta ruwa don ta dan ji sanyi,
Abinci da take dauki ta dawo ta ci sai gashi har da tuni anty tai mata ,
Duk yinin yau a kasalance maryam ta , wuni
Amma bata san ko may ke damun ta ba, kawai dai sai taji batajin wani kuzari,
Don haka, tun shiganta daki, bata kara fitowa ba har dare.,
Anty Dije ce taga cewa maryam bata fito ba don haka ta, tashi ta aza masu girkin, dare,.
Anty Dije ce,ta matsawa maryam ,da cewa tafito su ci abinci,
Dole badon taso ba tafito ,
Abinci kadan tazuba a plate, amma duk da zaman shi kadan ta kasa cin shi, sai tsakura takeyi tana cusawa,,
Ido Anty ta zuba mata har na wani dan lokaci ,can ta nisa tace, maryam may ke damun ki, ne wai,
Cikin jin wani irin nauyi maryam tace, ranan da na kwaso ne, yasakar min ciwon kai,
Wayar Anty ce tai kara alamar kira ,
Maryam wace, ke kusa da,waya itace ta mikawa Anty wayar,
Da dariya Anty ta karba sallama tana cewa mun kusa shan buki ashe Yusuf,?
Magana sosai sukeyi da Anty ida maryam ke jin yadda Anty Dije take lalashin shi, akan ya daure ya yi wanan abin da jibrin ke kokari ganin ya hada,
Maryam dake zaune a kasa, saman ties, sai ta dan kai kwance, a bayan kushin,
Ta sa kan ta, saman kujerar da take zaune a kusa da shi ,
Murmushi, tayi tana wasa da Abubakar wanda ke ta washe baki, a gaban ta,
So,sai suka dauki lokaci tana kwantar wa Yusuf da hankali akan kudirin su,
Acewar Antyn wai yin auren zai rage mai damuwar shi sosai,
Su,kayi sallama Anty Dije ta dan kalli inda maryam take tana wasa da dan yaron,
Tajima kafin tayi barci a ranan, bayan tabar falon tayiwa, anty ban kwana,
Alwala ta daro ta dinga jero nafilfilu masu ma,ana,
Sai ji tayi zuciyae ta yai wasai, kamar ba ita bace ranta yake a jagule,
Sai a lokacin ta, maryam ke ji a ranta bata jin komai gamay da zancen da akafada mata, ,
Yusuf ya iso kofar gidan Anty Dije, bayan sati biyu, da misalin karfe biyar na yamma,
Da sallama ya shigo cikin gidan alokacin maryam tana zaune cikin shigar shadda kamfala,
Shiri takeyi zata gurin bukin wata abokiyar ta na tun secondary school,
Zaune ta a saman kujera yar tsuguno tana ta faman gyaran fuska,
Dawani guntun broking mirrow, sallamar shi ce tasa ta tsaya wa daga fente fenten fuskan da takeyi,
Da yar fara,ar ta, a fuskan ta ,tare shi
Sannu da zuwa ta iya furtawa a hankali amma tana mai dukar da kai,,
Kallo guda yai mata yaga yadda ta koma kamar wata, classic baby,
Yaji wani yarrr amma sai bai ba da wanan abin yaji wani ma,ana ba,
Kafin ya karba mata anty dije ce tafito, a lokacin,
Γnty Dije ce ta fito daga ciki tana dariya da murnan ganin Yusuf a wanan lokacin,
Oyo, yo da mutane Lagos ne ko Abuja, sai da yai yar dariya na nuna farin ciki, yace ai nafi zama a Abuja yanzu,
Maryam ce ta tashi daga inda take ta dauko yar jakar kayan make,up din ta,
Tagaban Yusuf tayi bi inda kamshin nan nata kamar kulun yadaki hancin shi,
Ga dikin purple shadda kamfalan da tasa ya karbi jikin ta, tsab,
Daidai da zaman shi a lokacin ta dauko mai ruwa a cikin gora, hade da cup
A gaban shi ta dire kayan karo nabiyu kenan da wanan kamshin da ta budawa jikin ta yasa shi lunshe idon shi,
Thanks ya,furta a hakali kamar yadda ako yaushe maganar shi mai rowa ce,
Idon shi a lumshe kamar mai barci taji muryan shi yana cewa, maryam ga key a,dauko wa an nan kayan dake cikin motar,
Wani irin haushin taji don tasan zai bata mata lokaci ke nan,
Da sauri ta kalle shi tace saidai kila ba yara a wajen ko, ?
Daga shi har anty ido suka zuba mata dn jin maganar ta ,
Wanda ya nuna tana uzuri ne hakan yasa tace masu ba yara,
Anty Dije tace maryam sai kace ba wace iyakarta cikin kwantagora ba,
Wallahi Anty bana son in makara ne saboda sun riga sun sa cewa bazan zo ba ma sam,
Nikuma ina son basu mamakine su ga na riga kowa isa gurin,
Takara sa fada cikin shagwaba kamar yar karmar yariya mai shirin yin kuka,
Da ga ida yaje zaune ido kawai ya zuba mata alokacin ,
Don yadda take maganar kamar wata yar goye,
Anty ce tace inbanda abinki maryam tun da ga sauki Allah yakawo maki kawai da kin kwaso sai kibi Yusuf ya sauke ki tun da hanyar su zaki bi,
Kai kasa cike da jin nauyi likamata bin shi da antu tayi tace,
Ai basai na bishi tun da bai tashi ba kawai zanbi motar kasuwa,
Muje in sauke ki idan nadawo zan samu yara su sauke kayan,
Wani irin nauyi maryam taji a lokacin sosai, don jin ansar shi,
Ba musu dole ta jawo gyalen ta ta yafa tare da murza mai turare tako ina
Tsaye yake a bakin motar shi yana waya fuskan shi na kallon ta cikin gidan nasu,
A nutse ta ke takowa zuwa ida motar shi take, waya yaje yi amma kallon tsab yake kara mata ,
Tsayawa tayi daga dan nesa dashi kadan ta yadda bazata ji may yaje cewa ba,
Yagane nufinta don haka ya tsaida wayar yana ce mata bissimillah mana mutafi ko,
Mamakin irin saurin kwashe dabi,un shi na hausawa,musulumai da yayi da sauri takeyi,
Bayan motar ta tukara inda yace mata haba dai ai bayan ba guri duk kayane a ciki,
Dawo gaba kawai ki shiga ina ga zai fi,
A hankali ta saje hannun ta nufi dayan bangaren ta bude,
Kamar kullun sanyi da kamshi dai yana nan a motar nashi,
Ya na kokarin tada motar ne yake ce mata ina,ne gurin da zaki din,?
Tace mai MARAFA parks,
A takai ce tai maganar don haka bai kara tambayar ta ba,
A marairaice kamar mai shirin kuka tace, don Allah ina son zan dan tsaya Blue, sea, super market,
Batare da ya kalli inda take ba yace mata ok kawai, .,,,,,,,,,, ,
ZEEE MAKAWA,,,,,,
[3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: .πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
FUREN JUJI
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
5β£0β£
ZAINAB IDRIS MAKAWA,
UBANGIJI ALLAH YASA MUGAMA DA DUNIYA LAFIYA BAKI DAYAN MU YAN UWA MUSULMAI,,,,
πππππππ
Dan zagayawa take yi, cikin super market din, tana dan dibawa ko zata samu, abinda zata saye a matsayin gift , duk da bawai wasu kudine masu yawa acikin jakar na taba,
Layin sai,da kayan kamshi take dan zagayawa don dibawa,
Duke take tana kokarin ciro wasu set na shafa, irin ta mata, acikin wata, yar kit,
"Yan mata ya kike kwana biyu, ?
Muryan take tunane a ina tasan shi ne wai, don ko bata waiga ba tabbas tasan wanan muryan,
Bashir Alhasan ne tsaye da wasu kayan da mafi yawan matasan maza hausawa ke sawa a yanzu,
Tunane takeyi a ina tasan wanan fuskan ne wai, kafin second ta tuno, dashi.
Bata san lokacin da ta sake wani dan munrmushin da iyakar shi fuska,
Ina yuni tace cikin yanayin muryan nan nata,,
Yar kwaikwayon ta yayi hakan yakara sata sake wani lalausar murmushi again,
Tsayuwar shi yagyara yace ai nasan dama kida baki fada min inda kike ba wata rana zamu kara haduwa ne,
Yakara zancen, yana mai dan rausayar da kai, kamar wani kara min yaro,
So ya kwana biyu ya karatu Maryam Abdullahi ko,
Yana mai mata wani kallo irin na wayyaun maza,
Kafin ta bashi amsa yakara jefo mata wani tambaya,
May a kazo saye ne haka, ?
Bata bashi ansar ko guda ba sai dai yar murmushin da takeyi a kasa kasa,
Set din kayan, da ta dauka ya mika hannu ya karba yana dan karanta sunan shi,
Yace da alama dai gimbiyar gift take dibawa ko,
Hannu taga ya mika can ciki ya dauko wani babban set mai kaya kala kala cikin kit din,
Yace ina ganin ai wanan zai yi ko,
Maryam wace sai binshi da ido take don kara tan,tance halin shi,
Sai ya dan daga kai saman yana karanta wasu set haka, dake gurin,
Yadawo da kanshi yana mai kallon ta fuska a sake yace bazamu layin Sweet bane ko?
Kai ta girgiza mai alamar a ,a bazata ba, don haka yadan daga kafadar shi alamar ba ruwan shi,
Zan wuce ta furta, a hankali, kamar mai maganar rada,
Ok muje ko yace mata tana kokarin ce mashi ai ya barshi,
Sai ganin Yusuf tayi tsaye da alamar tun tsayin su gurin yake kallon su,
Tsaye yake a bakin wani da kantar kaya yajin gina da wani bango dake gurin kafar shi a harde, acikin wani,
Biye Bashir yake da ita, duk tawani kunya da ganin su da yayi, atare,
Suna tafe sai yaba kyawon kwaliyar ta yake yi yana kokarin cusa ta gwaunatin gare ta,
Sun kusa kaiwa inda Yusuf yake tsaye cikin dakewa sai wayar shi yaje latsa,
Maryam ta dan kalli Bashir,ta juya inda Yusuf yake tsaye tace,
Ga yayana ku gaisa dashi,
Wani kallo yai wa Yusuf na second, inda yagane cewa ba karamin mutun bane, don komai na jikin Yusuf zaikai kusan million, guda,
Yana yar dariya yace au kice min bake kadai bace dama,
Hannu ya mikawa Yusuf suka gaisa, sai dai Yusuf din,ya, na yin hausa sai Bashir din ya dan waigo maryam,
Tagane may yake nufi a cikin style ta kada mai kai alamar eh,
Amma tunda nayi ni,yar biyan kudin, wa yan nan kayan ina fatan cewa yayan mu zai bari in biya ?
Fuska aba walwala, Yusuf yace wa maryam indan kun gama sai ki samay ni a mota, ina jiran ki,
Daga haka ya juya zuwa waje inda suka aje motar su,
A tare suka fito dafa cikin plaza din da bashir wanda motar shi take aje a gefe guda,
Gurin motar Yusuf Maryam ta nufa ganin haka Bashir yadan fidda idon shi yana mamaki hafin maryam da wanan guy din,
Yusuf na kallon su daga cikin motar shi dake makale da tin tak glass,
Sun kysa kaiwa gurin motar maryam taja tai tsaye tace mashi, to na gode kwarai Allah saka da alheri,
Yadan sa key holder din shi ya sosa kan shi,
Sai kuma mukara haduwa ko maryam makarasa zancen mu ko ?
Da,sauri maryam ta dan kaleshi, tace yaushe kuma zamu kara haduwa ai ko yau sa,a ce,
Sai,da yai yar dariyar maganar ta, san,nan yace, aini dama ko yaushe a cikin sa,a nake,
Kai kasa cike da jin nauyi maryam tace to shi ke nan nagode badamuwa ki, sallamar min da yayan mu,
A nutse kamar kulun ta isa gurin motar inda tadan kwan kwasa mai glass, ,
Tana shiga motar yataya suka harba saman titin, sai dai a hankali yake tukin shi
Duk da kasan cewar motar babbace amma hakan bai,sa,shi yin gudu ba,
Sun dayi tafiya kadan, batare da, yawaigo inda take ba yace,
Wani, kuma sabon mayaudarine kika,samu, haka ?
A cikin mamaki take kallon shi ido a zazzare
Kallo, mai kama da harara ta yayi yace, gaskiya maryam ko wanan bai dace da ke ba, sam wallahi,
Kanta aduke tai shiru saboda wani irin bakin ciki da ya tokare mata mokoshi,
Ya dago ya kalle ta idon shi ya canza zuwa bacin rai,
Haka itama maryam domin maganganun sun daga mata hankali,
Idanu a runtse tana jin wani irin bacin rai, da kunar zuciya,
Haba ya Yusuf, ai wanan maganar bai,dace ka fada min ba,
Cike da mamaki, ya ware ido yana kallin ta don sam bai dauka maganar zai sa bacin rai haka ba,
What maryam bakya son a fada maki gaskiya ne, ?
, a,fusace kamar wace zatai shirin kuka, tace mai, haba dai daga ganin mutum kawai zaka yanke man hukunci akan shi,
Yakamata ace katambayeni bayani akan shi bawai kawai a yanke mun hukunci ba
Ya Yusuf ya,kamata ace kana cikin wa yan da zasu shedeni,
Kamar yadda kake tuhumar ina hurda da yan duniyar samari,
Ma,ana nima din yar duniyar ce ke nan ko,?
Murmushi ya yi kawai har zuwa lokacin da ta kare fadar maganar ta,,
Hakalin shi ya mayar a,titi, sanan yace,
Don nasan cewa,ke yarinyace karama , duk sun fiki wayo da sanin duniya,
Sam baki dace dasu ba gaba dayan su ,bai,kamata ace kina tsayawa dairin su ba,,
Daga haka ya mai da kan shi a kan titi sosai, bai kara,bita kanta ba,.
Saida suka kawo unguwar ya tambayi maryam tai mai kwatance a takaice ,
Kofa ta bude tana kun,ku ni, tana cewa wanda ke tare da irin su Aisha da sadiya ba ace mai ya bari ba sai wace ba ruwan ta za,a sawa ido,
Lock din motar ya dan na tayi tayi ta bude ta kasa sai a lokacin ta waigo in,da shi,ke zaune,
Kamar ba shi take jira ya bude mata kofa ba, sai kawai,ya kama lalabar wayar shi,
Cikin murya mai nuna karaya zuciya da kuma kuka, tace mai,
Ina son zan fita ne
Bai juyo ya kalle ta ba, tankar da dutse take,
Sai da yagama taba wayar shi san nan ya dan,na unlock, motar ta bude,
Ran ta a bace ta sa kai kawai tafita batare