Showing 21001 words to 24000 words out of 255288 words
taso kuma yan zun ne yasamu wanan ci gabar duk da dai basu san ko shi waye ba to amma dai sun san yana da shi,
Muryan Nasir ce tadawo da shi inda yaji Nasir na fadin cewa
Allah yasa ko yar Suzuki yasamu ya saye shima, hakadai duk sukayi ta hira a tsakanin su inda kowa ke fadin albarkacin bakin shi,
Har zuwa goma na dare suka kai agurin suna hira sannan KB yadauke shi sama wata rubaban mashin din shi zuwa gida,
Tun da safe yabar gari ya ko gurin harkokin shi don ci gaban shi,,
Tunda yadawo yadawo da kudin tallafawa mutane da dama aran shi,
Din shi a ganin shi duk wanda kuka wahala tare har Allah yabaka samu daga cikin ku to bai kamata ka manta da yan uwa ba,
Sanar,ar da suka fara shigo da dan yar Gas dama ainihin pure Gas din,
Gani harkan ta karbu yasa shi yin kokarin gani sun gyara system din business din yadda ya kamata,
Shigowa da mai din kasar arewa yasa shi kawo KB daga cikin wa yanda za,aiwa interview din zama members nan gaba,
Waya yai ma KB yace su hadu Abuja next week Wednesday, don su dan tatauna, akai,
KB duk da bai sam komaiba bai yi kasa a gwaiwa ba ya shirya zuwa Abuja din, don ansa kiran da joe ya mashi,,
Cikin lokaci ya samu isa Abuja inda yasamu, har Joseph ya cika mai duk wani form da ya kamata,.
Briefly Joseph yai mai bayani sai gashi kawai, ankira shi don yashi ga ciki duk da bawasu tambayoyi bane masu tsauri amma dai Joseph din yana darrr kada kb ya kasa amsawa duk da baida shakku akan shi, don yasan cewa yana da kokari,,
A cikin ikon Allah KB yai nasaran lashe interview din ,,,a cikin masu yi harda Joseph a cikin su,
Murna da farin ciki a gurin su baa musalintawa, duk da har yanzu bawai KB ya gamsu da kowace irin aiki bane,
Amma dai gani masu taron ya tabbatar mai da ba karamin aiki bane,,
Wanan abin ya jawo ma Joseph surutu acin abokan harkan shi,
Don sai cewa suke yi ya dauk hausa ya sa acikin harkan shi ya bar yan uwan su sun fadi,
Wanan damar a cikin sune ya kamata wani ya samu ba,a cikin northern side ba,
Suko hausawan dake cikin su sun yi mamaki kwarai daganin Joseph ya kawao candidate din shi bahaushe,
Tun a wurin akaba KB sabuwar mota da kuma gida inda zai dinga besing a Abuja
Sai sabuwar office da aka bude masu washegari,
Kabiru gani al,amarin yakeyi kamar a mafarki wai yau shine da wanan abin da bai taba tunane samu ba,
Sai gashi Allah ya bashi cikin dan lokaci guda, don haka bakaramin nasiha Joseph yai mai ba don ya fada mai cewa sai yasa ido ga harkan so sai kuma ya rike gaskiya don akwai bata gari wa yanda zasu iya batasgi cikin dan lokaci,
Don zasu iya hada mai tracks kalakala don kawai ama wani hanya,shi a kore shi,
Kwantagora ta dauki zance kwaaaaa cewa KB yadawo da sabuwar mota, ya samu aiki,
Amma ba,a san kowace irin aiki bane haka da har ya samu wanan cigaban cikin lokaci guda,
Wasu suka fara cewa ai yafara irin harkan Joe ne Joe din ya jefa shu cikin kungiya,
Wanan zancen har ya fada a kunen KB da yan uwan shi,
Inda mahaifin shi yakira yin mitin tare da duk wani dan uwanshi tare dashi KB din,,,,
Anan KB ya fada masu cewa wallahi har ka ce ta sanar man Gas wanda duk wani Gas da zai shigo nan arewa saida sa hannun su a ciki,
Nan dai yai masu bayani har suka fahinta suka kuma yi mashi fatan alheri a harkan,,,
Saodai cikin gari kan wasu sun yarda wasu ko ba su yarda ba har yanzu,,,
Sadiya Mohammad jodi wata sabuwar matashiya ce mai tashen budurci a cikin gari
Tun ranan da taga Joseph tare da su Aisha Allah yasa mata son shi a rai saidai kawai matsalar ta da akace mata ba musullumi bane shi,
Don har ta kasa boyewa a zuciyar ta saida ta samu jibrin tai mai magana akai,
Dayake akwai wasa a tsakanin su yasa Jibrin duk inda ya ganta sai yace mata ta Joseph ita kuma sai tace aa, saidai Yusuf,
Wanan wasa ko yaushe jibrin kewa sadiya, indan sun hadu ita ko bata gajiya da bashi ansa kamar kullun,
Maryam ce zaune tana wanki a bakin famfo gidan su.
Wayan Anty Dije yai kara alamar kira ya shigo mata, a lokacin
Maryam tamike cikin tafiyar ta maikama da rangwada kasan cewa ba wani jiki gareta ba,
Daukar wayan tayi don ganin bakon noba ke kira, cikin yar siririyar murya tace Assalamu Alaikum,
Hello Anty kuna lafiya ya yara da gida,
Wayan ta dan daga ta kalla,sai kuma ta kara manna wayar a kunen ta,
Wake magana ne tace ?
Anty Hadiza nake nema pls aka bada ansa,
Bata nan ta,shiga makwabta yanzu, dan shiru yayi sai kuma yace Assalam na kusa pls,?
Baya nan shima tare suka tafi, ok in tazo ki fada mata Joseph ya bugo mata,
Joseph kuma ? Joseph fa, kai is wrong noba pls
Kada ka kara bugowa nobar matar aure ce pls
Dan murshi yayi har tana iya jin shi, alokacin yace ba nobar maman Assalam bane?
Tsuki tayi tana fadin mukan ina muke da wani arne wai Joseph da zai kira Anty
Daidai lokacin da ta gama fadi ta kashe layin,
Tana ta faman fada wai kawai don suyi magana da matan mutane suke kiran wrong noba,,,
Shiko joseph dake zaune a saman wani leda cushion ya rike wuyan shi da hannu bibiyu ya furzar da iska, daga bakin shi,
In akwai abinda yafi mai munin ji shine ace mai arne, ko kafiri,,,,
Tun yana yaro yai hating din wana kalman a rayuwan shi,
Don in mutane suka ga su jibrin ko kabiru tarrme dashi lokacin sai yaji sun ce baku barin yawo tare da dan kafirai ko ko dan arna ko,
Wani bukin Christmas daya kawo masu abinci kamar yadda su ma suke bashi abinci sai cewa wasu mata sukayi
Ku fita mu na da abincin kafirai a cikin gida kada muyi amai
Wa zai ci abincin arna jagwagwalen banza kawai babu ko tsarki,
Shikuma yadai san cewa duk wani tsabta a lokacin mamanshi tanayi,
Kuma shi har gobe idan ya kewaya yana tsarki kamar yadda ya ga kowa nayi,
Amma sai ake ce mai wai baida tsarki haba mutane ne,????
Anty Dije tana shigowa tare da su Assalam daga makwabta ko daki bata shiga ba,,,
Maryam ke fada mata cikin fada cewa wani kafiri ya bugo mata waya wai sunan shi Joseph nikan nace wrong noba ne
Dan rainin wayo kawai Anty Dije dake tsaye sororo tana kallon yadda maryam ke ta faman halako fada,
Tace kafirin banza kafirin wofi don ma bakiji hausan shi ba wallahi kamar fa hausan mutum kwarai,
Anty Dije tace maryam ina fatan duk wanan zancen baki fada a waya ba dai ko,
To may ye Anty in ma na fada mai kawai ina aikina kafirin banza ya kirani, ya bata min lokaci,
Saida Anty ta zauna take cewa maryam mutumin nan ne fa abokin Assalam,kike ta surfa ma masifa,
Barin wankin tayi tana kallon Anty Dije tace Anty ce min fa maishi yayi sunan shi Joseph fa,
Shine mana Anty takara ce mata da dan karfi wai anty shi kafiri ne dama ba musulumi ba,
Ke baki sani bane dama
Hmmmm lalai mishon bat da musulumi,
Wallahi anty ni na dauka cewa musullumi ne shi duk ganin da nake msi,
Dan guntun kara dake gefe anty tadan duka ta dauko tana cewa wallahi ke dai kamar ace mai musulumi
Don dai gaskiya ya duk halin shi na kwarai ne, wallahi,
Daga inda maryam take tsaye tace furen juji kenan shi,
Ga halin kwarai amma ba alkiblan kwarai,
Dama malamin mu na islamiya ya fada muna ce wa akwai irin wa yan nan mutane acikin yan Ahal,kitab,
Saidai basu da yawa so sai daga cikin su, masu halin rayuwa irin na mumunai
Daga haka ta tabe baki taci gaba da wankinta tana cewa Assalam abokin Christian, shiko sai dariya yake mata don bai san ma,anar maganar ta ba,,,
Yinin ranan sai maganar ta dan tsaya mata a rai kawai tausayi yabata mutum kamar wanan ace baya sallah Allah ya kyauta kawai take cewa aranta
Sai ma daga karshe takama jin haushin shi, da takaicin kawai,,
Mr Emanuel yanzu girma ya fara kama shi don haka yanzu iyakar shi zama gixan man su ya daina yawan harkoki kamar da
Kamar su saida manja, saida robobin aiki irin na mata duk suna da shagunar su acikin garin kwantagora,
Yau ma kamar kullun zaune yake saman wata far kujera kamar kulun da yamma haka yakeyi sai zuwa shidda yake wuce wa church wani lokaci,,
Wani musa mai aski ne yazo inda yake don sun saba da musa,wanzami tun tuni
Saboda zaman uguwa guda, da suka taba yi ada,
Shine sabon su yai karko har zuwa yan zu
Musa yakan dan biyo ya samu dan abin ihisani akai akai
Bayan sun gaisa ne yake kokarin zama gefen da Ema mai manja yake, daidai lokacin yake cewa
Ashe taimakon da yaron ka yayi wa dan gidan Tanimu kafinta ke nan
Mr Ema ya ce taimakon may ke nan fa, acikin hausar su irin ta IBO,,,
A, ba ance ya samo mai babban aiki a Abuja ba har ma yai kudi lokaci guda,
Wani yar Mr Ema yaji kamar an datsa mai mashe a zuciyar shi,
Sai da yai kokarin boye ma musa wanzan da halin da ya shiga tukun sanan yace har ya fara aikin ne ko,
Musa wanzan yace kai tun yaushe aiki kan har mun fara cin moritar ta,
Don nafito zan wuce kauye nagan shi yana magana da wasu masu aikin gina wai yana son ai masu katangar gidan su,,
Wani iri mr Ema yakaraji a ran shi watau ke nan har maishi yadan fara karfi da tai makon Joseph din,
Alhalin ga yaran su cikin gari birjit da suka gama karatu suna ta bin shi yasamo masu aikin yi yana cewa ba aiki yanzu,,,
Musa na ta zuba shi bai ko jin may yake cewa a lokacin,,,
Kai musa pls zan tofi wani anguwa ka tafi kawai zamu hadu gobe ke nan,
Daga haka ya tashi sai gurin motar shi ya nufa rai bace
Gidan shi ya nufa cikin fada yake kwada ma Samuel kira
Ya wurgat da sandar da yake yawan rikawa mai alamar sandar sarauta,
Lokacin Samuel yafito daga cikin gida inda yake daka sakwara,
Call your brother for me pls,
Cikin mamaki Samuel din yace ok Dad,
Kira daya na biyu ya dauka
JOSEPH da kakausar murya yakira shi hakan yasa Joseph din sani wani muhinmin magana ya faru
Don haka yai shirin sauraren baban na shi,,
How may time D I warn you about dis hausa boy's,,, ??
Baba what's going on. Sai kuma yace cikin yaren su maya faru baba,
Ya akayi ka samo ma yan gidan hausawa aiki bayan nayi ma warnings akan MAKu da su,
Sosai yake mai masifa shi dai sauraren shi ya keyi batare da ya ce uffan ba,,
Daga karshe kuma sai ya sasauta muryan shi zuwa lalashi,
Yace You have to be,careful with dis people they are very dengerous,
Haka dai yai ta ma mai nasiha shiko yai shiru kamar mai saurare,
A karshe ya sheda mai cewa yana jin kunya abokan shi da yan churches din su su ji cewa yai eanan aikin,,,,
ZEEEE. MAKAWA. ππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
FUREN JUJI
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
1β£1β£
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Why why mutane suke da gulma haka, may ye aibun taimaka ma KB dayayi da har za,a fada ma Dad din shi,
Wai may yasa mutane basu kaunar suga cigaban yan uwan su ne musan man hausawa,
Don dai yasan cewa wanan maganar daga bakin hausa yafito zuwa kunen mahaifin shi,
Zubur ya mike tsaye daga inda yake daga shi sai dogon wando da singlet a jikin shi,
Gurin window dake facin din titin da ke unguwar su ya nufa,
Fitinlo ne karara suka haske ko ina sai kuma duhun dare da ya gauraye gari lif,
Ya kai wani dan lokaci a gurin tsaye yana kallon sararin samaniya kawai,
Daga karshe bayan yasamu mafita yai wani dan ajiyar zuviya mai nauyi,
Fridge ya bude alcoholic ke ciki kala kala duk sunyi rabar sanyi yadda yake so,
Hannu ya mika da niyar yadauko wani mai berry a ciki,
Caka hannu shi ya tsaya daidai wuyar kwalbar
Muryan Jibrin ne ke mai yawo a kwakwawa duk addinin mu bai yarda da shan giya ba,
Duk wanda ya ganka a lokacin kana cikin maye baya kara kallon ka da dara a idon shi,
Don duk sanda ya gan ka wanan yanayin mayen dayagan ka aciko zai fado mai zuciyar shi
Kaga kimar ka da mutuncin ka yazube a idon shi,
Idan kuma ka samu iyali za,a dinga goranta masu cewa uban su dan giya ne, ai,
Cikin sauri kamar wanda akai ma tsawa ya dauke hannun shi saman kwalban,
Marfin fridge din ya buga da karfi kamar zai balla ,shi,
Da karfi ya fada kan gadon ta baya yana mai rike goshin shi da hannayen ,,
A haka wani irin barci mai nauyi ya kwashe shi bai farka ba sai misalin karfe tara saura na safe ,
Dan hasken ranar da hudu ta cikin labulen window dakin ya haska mai idon shi,,,
Mika yayi ya gyara kwanciyar shi don ya cigaba da barci amma sai kuma ya kasa ci gaba da barcin,
Mikewa yayi yashiga bayi yai wanka bayan fitowan wanshi ya na daure da towel
Yazo bakin gado ya rusun na kan shi saman gado
Nan yafara jero addua, our father whose as at heaven ,
Hello be there name,,,,,,,,,,,,,
Bai tsaya ba saida yakai karshen addu,an shi kamar kullun yadda ya saba yi duk safe kafin yafita,
Saida ya kintsa tsab ya sauko inda yasamu break fast din shi an shirya mai komai tsab
Jin gidan shiru yasa shi daga murya yana kiran Uchee, da karfi,
Uchee da ke can yana gyara cikin gida yazo cikin ladabi,
Cikin muryan nan tashi mai nuna sanyin hali a koda yaushe yace ma Ucheen ya na duk bear dake cikin gidan shi a kwashe su a zubar da su,
Jin maganar Ucheen yayi kamar a mafarki cikin sauri yadago kanshi ya kai wa ogan kallo,
Joseph da kanshi ke duke yana dan kada ruwan zafin da ya zuba a cup,
Batare da ya daga kai ya kalli Uchee ba yace
Yes I Mean it,,,,
Uchee zuciyar shi fam da farin ciki yasamu gara basa, yau,
Duk yawan giyar gidan oga a ce wai ya kwashe ya zubar,
Ba bata lokaci ya kwaso su jiki na rawa yafita dasu gidan,,
Saidai a kasan zuciyan shi yana mamakin ko may yasa ogan nashi ya ce ya fita mai da su gaba daya,,
KB ne ya kira Joseph din wanda duk yinin yau bai fita ko ina ba yana zaune a cikin gidan shi da ke cikin birnin Lagos,,,
Cikin kasala yadauki wayar don bai son yin wani dogon motsi yau,
Hello, KB ya kake ne yau ya, Abuja,?
Yace a lokaci guda sai KB ya amsa mai da cewa lafiya kalau gashi ma zai tafi suleja dibo wasu motocin da suka samu matsala,
Kuma suna dauke da mai a cikin su,
Duk da Joseph din yai kokari wurin bashi amsa sama sama,
Hakan bai hana KB gane cewa Joseph din yana cikin wani irin yanayi yau din,
What's wrong with u, today,,,?
KB ke tambayar shi a karshen maganar su da Joseph din,
Nothing ma,,
Inji Joseph din yaba KB amsa a takaice, kawai, daga haka suka kashe wayan,
KB din ne yadan shiga tunane don saboda dan zaman da sukayi da Joseph yakai kowa na iya gane mood din wanin su,,,
Duk abinda KB keyi hankalin shi na gurin Joseph don shi a zaton shi ko baida lafiya ne
Don yasan cewa ciwon Joseph kamae fitina ce ga duk na kusa dashi,
Saboda irin mutanen da basa ciro ne da wuri ranan da duk zasuyi sai duk wanda ke tare da su hankalinshi ya tashi,