Showing 159001 words to 162000 words out of 255288 words
Chapter 54 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete
su karasa kallo yara suka dinga shigowa da caton din drinks din da ya sayo masu, a can,a
Ba Maryam ba har anty da safiya sai da sukai mamaki irin yawan drinks din da a ka shigo da shi,
Maryam mamakin ta shine cewa yaushe a har ya sai masu shi bata sani ba,
Dai lakacin da suka shiga shagon ya umurci wani da ya loda mashi su a mota, kafin su fito,
Safiya ce ta dan juya gefen da maryam take tana cewa, o ya sai ki zo ki ta sha tunda don ki a ka siyo ,
Batare da maryam tai magana ba tamike kawai niyar wuce wa dakin
Muryan Anty Dije ce ke cewa maryam din wa zaki bar wa wanan kayan a,nan,
Cak ta tsaya guri guda don jin maganar da yar na ta , ta yi,
Idon ta, takai kasa gurin da kayan suke zube, Safiya ce tagani tana ko,karin maida kayan a cikin ledan su,
Dukawa tayi ta dauki leda, daya daga cikin ledojin tai gaba kawai a,binta, ta bar sauran inda suke,
Bayan ta anty dije tabi da kallo tana mai tausayawa rayuwan yar kaunar nata,
Saman kujeran su ta zobe kayan gefen Naimat kadan,
Safiya ta biyo bayan ta dauke da sauran kayan a hannun ta,
Dai dai, gefen maryam ta zauna inda ta dauki hannun ta ta dora a saman ciyan maryam wace, ke kokarin cire, dan kunnen ta,
Sunan maryam din takira a hankali, tare da kara dafa ta don su fuskan ci junar su,
Maryam ina son ki bani aron hankalin ki nan ,a cikin murya mai nu fushi maryam din tace ina jinki ai,
Murmushi safiya din ta dan yi wanda bai kai ciki ba mai alamar yake,
Maryam may ke tsakanin ki da uncle Yusuf, ne ?
Batare da ta kalli inda safiya take zaune ba,tace a takaice, may ki ka gani halan, ?
Hmmm kawai safiya ta ce ma maryam din don jin ansan da ta bata, a takaice din,
Maryam look duk da nasan cewa ,ba wai zaki fada, min ai,nihin gaskiyar zancen gaskiya ba,
Akan abin da ke a tsakanin ki da uncle din ba amma aini kuma bawai yarinya ba ce da ba zan iya gane ko may kuke a ciki ba,
Kin dai sani, ?
Ta karashe zance tana mai yiwa maryam din wani irin mugun kallo ,
Barin fada maki gaskiya idan zakiyiwa kan ki fada wallah maryam kiwa kan ki don naga wankin hula na shirin kai ki dare,
Safiya may kike shirin fada min ne wai akan uncle ne ?
May ke a tsakanin na dashi ban da mutuci kawai,
Amma zaki zo ki wani dinga min tambaya kamar wani ya aiko ki yi min shi,
Sanin halin maryam da safiya tayi kawai sai tai dariya maimakon ta mai da zance wasa,
Ba kamar yadda ita,maryam din ta dauki maganar tankar da zafi ba,
Hakan da maryam din tayi bai hana Safiya ci gaba da mata zancen Yusuf din ba,
Maryam kiwa kanki fada wallahi don dai uncle zai so ki ya kuma rike amana, ba kamar yadda A, A da ki,kewa rawan kafa yake gwadamaki ba,,
A hasale maryam ta juyo tace kamar may ki ke nufi A,A yake gwada min safiya,?
Maryam inji safiya wace ta kira maryam din cikin nuna kulawa,
Ki yarda da zance na pls akan cewa da nai maki cewa akwai wani abu a tsakanin ki da uncle yusuf wallahi,
Wani irin mugun takaicin safiya ne ya rufewa maryam din ido wanda har yakai ta iya wa safiya din maganar komai a lokacin,
A hasale ta juyo da karfi tace Safiya tun,da har kin matsa da,cewa akwai,
To kwai din samay don naga cewa magana kawai ki ke son yi,
Maimakon safiya din ta biye mata sai ta mike cikin wasa take wa maryam din idan yai tsami ai maji,
Don Ruwa Baya Tsami banza inji, Maman Farida,,,,,
Sosai suke ta harkokin shirin bukin auren Naimat wanda yanzu saura yan kwanaki kadan ayi shi,
รnty Dije wace tai matukar kokarin wajen ganin cewa taiwa amarya duk wani abin da ya dace ai mata, alokacin aure,
Kaya masu kyau nagani na fada yaiwa Naimat din na daki,
Sai a,wanan lokacin ne su Anty suka san cewa akwai yan tsirarrun Christiatorchi da dama agari wa yanda suka musulunta,
Kamar hadin baki sunyo gaiyyan junar su zuwa gurin karar wanan bukin
Maryam wace ke ta kokarin kawo masu ruwan sha tare da abin sha a lokacin tana jin irin yadda suke tawa Naimat murna da arzikin shigowa, cikkn muzulunci,
Anan take jin wata far addatijowa tana Naimat magana a cikin gwari gwarin hausan su,
Cewa kada kiyar da ki irin musuluntar Nao,mi, wace kusan sau uku tana musulunta tana kuma komawa Christian,
Saboda kawai wai ta kashe auren da tayi da musulmi,
Wanan maganar da maryam taji a lokacin yai matukar bata mamaki
Bata san lokacin da tasa bakin ta azancen ba tana mai tambayar su ko lafiya, ta dinga wanan irin Riddah hakan ?
Daya daga cikin matan wata mai hausan da ba daidai ba ta juya gurin da maryam take rike da kwalin drinks a hannun ta tace, acikin magana a hankali da kuma bacin rai da kaico a fuskan ta,
Kin san wasu basu da karfin imani a tare da,su, don haka auren da taiwa musulmi da zaran ya mutu sai ta koma matsayin ta na Christian,
Idan kuma wani musulmin yazo again ya aure ta sai ta kara canzawa zuwa cikin islama,
A haka har tai wanan kusan kashi uku yanzu haka tana a cikin Christian ne,
Maryam kara tambayar matar tayi da cewa kuma an kasa samu musulumi wanda zai rike ta,
A matsayin amna tun da tana da ra,ayin yin addinin muduluncin,
Sai matar tai wani irin daga hannun ta zuwa harba ta rike a cikin nuna wa?
Tace wasu maryam wacce tsayuwar ta da zancen da sukeyi ya jawo ra,ayin mutane da dama gurin su,
Matar tace ai kin san halin mutanen musulmai yanzu ba wai taimako da sukewa irin wanda ya musulunta haka,
San,nan kuma ita wanan matar, kishiyoyin ne ke hana ta zama a gidan mijin,
Bawai itace bata son zaman auren ba, saidai kuma mai maimakon idan tafito tasamu gidan wasu musulmai ta zauma a a sai dai kawai ta koma gidan su ta zauna
A haka yau da gobe sai kawai muji cewa ai ta koma Christian again,
Sai da maryam tai wani irin ajiyar zuciya mai nauyi sai ta ce Allah ya kyauta,
Duk gurin suka amsa da fadar Ameen Ameen, gaba daya a lokaci guda,
Daga haka maryam ta wuce zuwa gurin da suke aiki sai dai zuciyar ta cushe da bakin cikin halin da wanan matar take ciki,
Tun zuwa lokacin da takoma haka kawai sai ta tsinci kanta a cikin damuwa da maganar,
To sai dai kuma ta ina zata fara wa zance daga karshe ma zuciyar ta ya bata shawara akan
Ita wace,ce da may ma zata iya tallafa mata tai tsuki tana mai cewa ina ma a ce musulman mu masu zuciya ne kamar yan mabiya addinin Christian,
Da wanan tunanen suka risketa a zaune, duk sallama da maganar da Jibrin kewa maryam hankalin ta ya zurfafa a cikin tunanen wanan matar da taji labarin ta dazun,
Gaba dayan su mamaki yadda yar karamar yarinya take irin wanan zurfafan tunanen da kurciyar ta,
Jibrin ne yasa keys din motar shi kusan fuskan ta ya dan kada mata shi a fuska,
Firgigit tadawo a cikin hankalin ta yayin da ta sauke idon ta a kan su su uku,
Suna tsaye suna mata wani irin kallon mamaki cikin sauri ta dukar da kanta kasa tana mai gaishe su da shigowa a lokacin,
Kara tambayar ta Jibrin din yayi a cikin tsigar wasa,
Ko dai A, A din ta dan masuga take tunane ya kira mata shi,
Murmushi mai kama da harara tai mai tana cewa ai ba sai kakira min shi ba,
An fada ma, ni banda wayan kiran shi ne a guri na,
Ke dai gaskiya barin kira maki shi kawai,
Wani wawan tsuki Yusuf yaja daga bayan Jibrin din yace
Ke Maryam Anty tace zaki fitar muna da kulolin abinci ko ?
Sai a lokacin maryam ta farga da su a tsaye bayan jibrin
Yusuf din wanda tun fara wasan ba,an su yake faman dan,nan wayar shi, kawai,
Irin yadda yai magana ta mayar mai da ansa ita ma,
Ta mike suka shiga fito masu da yawan kololin abincin da a ka dafa masu don jama,an su,
Gaskiya duk sun yaba da irin kalar girkn da anty dije ta tayi ita da sisters din nata,
Maryam ce ta dangware wasu set din plates masu yawa a gaban kololin,
Yusuf wanda ke can daga bayan su don yaki karaso kusa yadaga wayan shi yana kira,
A daidai lokacin da wata daga cikin matan tazo tana mai wani kirari a cikin harshen yaren su,
Sai wata yar boyayyar murmushi yake yi a hankali tankar wanda bai son asan may take cewa,
Matar ta juya da harshe hausan wanda ke da,surkin yare aciki tana mai cewa wasu jibrin,
Wanan da kuna ganin shi a nan,
Shan gerin mu shune manya, manya sosai don de baba nashi bai jauna a gida bane
Da yan junan yazama serki a gerin na su ko,
Kudi masu yawa yafito dasu ya mika mata sai ga sauran matan dake saye da zanin su na IBO
Anyi fanti, fatin sama da kasa sai farar bluewers, da gwagwaro a kai,
Nan suka shiga raira mai wani waka acikin yaren su suna mai yi mai kirari,
Tsatsaye su maryam sukayi suna mai kallon su gwanin ban sha,a wa,
KB da Jibrin su ma suka basu kyautan kudi masu yawan gaske,
Safiya ce ta dan muntsili maryam din tana mai mata nuni da Yusuf din,
Wani irin wawan duka takai ma Safiya din wace ta kauce tana dariya keta,
Caraf sai a idon Yusuf wanda, idon shi yakai gare su tun fara wasan nasu,
Daure fuskan shi yayi yana mai masu wani kallon ku daina haka man,
Duk kan su, suka sun,kuyar da kan su a cikin lokaci guda,cikin jin kunya,
Still, uncle inji Safiya ka bari mu ji kirarin ka mana ko zamu iya muma muyi ma, irin shi,
Duk daure fuskan shi da yayi sai da maganar safiya ta sa shi yin yar murmushin,
Ya dan kada kai yace kai,safiya baki da dama fa,
Dariya ta saka mai tana mai jawo maryam, wai zasuyi wa Yusuf din kirari,
Kanta ta koma sadawa kasa saboda irin kallon da Yusuf ke mata,
Mayar da hankalin shi gurin da kololin abincin suke ya yi
Juyawa kawai maryam tayi zuwa dakin, abin ta batare da takara wani abin ba agurin,
Ko da ya juyo bai ganta a gurin ba ta wutsiyar idon shi, ya dan hango ta, zata shige daki,
Daga cikin daki taji dirin motocin su, sun kwashi kayan abincin zuwa gurin da za ai recipetion,
Wanka maryam tayi bayan shigan ta daki inda ta fito cikin wani Dakkaken dinkin shadda din da yusuf ai,kowa Sadiyar, ce daka karshe kuma yace abar ma,maryam din,,,
Sune Anty Dije ta bayar akai mata wanan dinkin mai wani hannu shara,shara,
Sai lece, da aka darza mai bayan anyi mai aikin wuta, da kuma stone a jikin shi,
Kayan light green, sunyi mugun karban jikin ta takai wani lokaci a gaban miro tana gyara jikin ta tsab,
Itama dai safiya irin shaddan ta sa sai dai gurin dinki ne kawai suka sha banban dana maryam,
Sun kai wani lokaci a cikin daki suna yar hiran su ,saidai muryan mutane da suke ji sama sama a,waje,
Da sauri ta mike zuwa waje don tunawa da tayi cewa Anty fa bata gida suna gurin gyarawa Naimat gidan da zasu zauna,
Zaune yake shi kadai a cikin falon su, ya dan zauna rigingine.
Ya dafe kai da hannu shi guda idon shi a rufe ya lumshe su,
Ganin da tai mai haka yasa ta kudirawa barci yake yi a hankan,
Juyawa tayi da niyar ta koma cikin daki inda suke ta zabga hiran su,
Maryam, yace cikin wata irin nishadaddiyar murya,
Cak ta tsaya don jin mai zaice, mata,
Still bai kalle ta ba hannun shi ya na dafe da kan shi,
Jikin ta taji yai sanyi don irin yadda yai mata,
Kan ka ke ciwo ne yaya ta samu kanta da tambayar shi,
Shiru nadan lokaci tukun kafin ya cire hannun shi yadan kalle ta da idon shi da su ka kada mai sukai jajir kamar yaci kuka,
A hankali ya ce mata may kika gani ne haka ?
Cikin dakewa tace idon ka sunyi ja da yawa uncle,
Kan sa ya girgiza mata, yace babu wani ciwon kai dake damu na maryam,
Illa magana da ke kokarin tarwatsa min zuciya ta,
Maryam bana son in na fadawa mutum gaskiya,yana dauka ta tankar banda daraja agurin mutum,
Baki ta dan murgada mai kadan tace nidai ya Yusuf na dai kusa aure in huta da duk wanan sa idon da kuke min,
Don dai ni banga abin da nake yi ba har kake cewa hakan,
Niyar barin gurin tayi tana kun,ku ni, tana cewa wallahi shi yasa bana son shigowar ku KG sam, saboda takura da sa ido,
Tajuya kawai abinta,
Saidai batai nisa ba ta jiyo muryan shi yana cewa,
To aiko nai maki murna da kika fada min cewa, kina son aure kwanan nan
Don haka zan je in samu baba da Anty in sheda masu, abinda ki ka ce,,
Da sauri ta juyo tana fuskan tar shi batare da wani jin dariri ba ko kunyan shi,
Sai dai, kuma wanan karon kamar bashi ke kwance da zu ba,
Yanzu a zaune ya kyam,kamar ba shi ba, ya na mata wani kallon cikin zaki gane kuren ki,
Ba kunya ta, kama yar hararan shi, tace, ban san may yasa kake yawan samin ido yanzu ba wallahi,
Kawai ta juya ta shige abin ta zuwa inda ta hango Naimat zaune tare da bakin ta,,,
Bayan ta yabi da kallo a daidai lokacin da kiran sadiyar shi ya shigo mai,
Tana mai sheda mai cewa ga ta a kofar gidan รnty tazo mai buki,
Tashi yayi daga inda yake yadan leka inda yaga maryam tabi,
Tsaye take sina diban waya ita da Naimat da Safiya,
Ganin shi ya leko daga kofan falon yasa su mai da hankali gurin shi banda maryam wace kanta yake duke tana kallon waya,
Sunan ta yakira yace tafita waje ta shigo mai da baki pls,
Lokacin da ta fita, ta samu su Sadiya ne bakin da yake nufi tai bakin ciki sosai don ita tana ganin cewa yai mata rashin mutunci sosai,
Ita Sadiya din bata san kofar shiga gidan bane da zai tura ta taron su,
Kallo guda Sadiya tai wa Maryam sai taji wani irin tsanar yarinyar ya kara shiganta,
Ita dai sam bata ra,ayin wanan yarinyar a rayuwar ta bata san mo may ya sa ba,
Rai a dan bace maryam ta dan tare su inda tai masu iso zuwa cikin gidan,
A falo kamar yadda tabar shi su ka samay shi a zaune hankalin shi kwance,,,,
SEENABU ZEEE MAKAWA
๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ
FUREN JUJI
๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ
6โฃ6โฃ
ZAINAB IDRIS MAKAWA,
IYAKA, NA,ABBUDU WA,IYAKKA, NAS,TA,INN,,,
Ina mai baku hakkurin rashin jina da bakuyi ba kwana biyu, da fatan zakuyi hakkuri dani dan Allah,
Sanya suke cikin dogayen rigunar shadda mai ruwan powder, wanda dinkin shi ya,kai har kasa kamar yana jan kasa,
Hannun dinkin shara,shara, dashi har ya dan zarta hannun su,
Takalman su masu tsinin duduge, da su da kuma tsawo,
Sai chewing gun dake a bakin su suna taunawa kas,kas, kas,
Duk karan chewing gun din ya damu maryam wace ke gaba tana masu jagora zuwa ciki,
Idon su kem a kanta, yanayin ta da kuma yanayin shigar ta ya sasu yin hassada da ita a cikin zukatan su,
Kayan da ke a jikin ta da nai bayani baya din kin yan Senegal yakarbi jikin ta yai mata dan karen kyau, a jiki,
Yana zaune kamar yadda ta bar shi kafin ta fita,
Sai dai wanan karon waya ce a hannun shi yake yi,
Takon su takalman su da ya cika gidan duk ya ruda ko ina,
Wanda hakan ya jawo hankalin mutanen dake ta wajen tsakar gidan zaune,
Inda suka zubo masu ido caaaa, suko sai wani ran gwada sukeyi abin su
Gurin zama maryam din ta nuna masu saboda samun shi da sukayi yana waya a lokacin,
Fita tayi zuwa dauko tire inda