Showing 165001 words to 168000 words out of 255288 words

Chapter 56 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1792

sai dai jefi,jefi tana kallon shi idon shi a lumshe suke,
Ba ai wani dadewa ba Jibrin yai sallama tare da mai kayan,
A kofar falo suka yi sallama maryam wace ke zaune da yaran suna kallon a wayar ta takarba masu sallaman su,
Dukkan su a falo suka zube sai kayan da mutumin ke kokarin budewa daga cikin wani buhu,
Zannuwa masu yawa tagani suna fitar wa daga cikin buhun,
Jibrin din ne yasawa maryam wace ke ta waje kira,
Sai da ta dan ja aji irin na mata tukun sannan ta mike zuwa ida suke,
Tun daga nesa ya tsai da hankalinshi gurin ta irin yadda take tafiya,
Tabbas maryam ta, tara abubuwa da dama da sai yanzu yake gani su daga gare ta,
Idan ma don kyau ne ta na dashi uwa uba kuma hali duk yarinyar tana da,su,
Cikin yaga da nuna isa ta yan matan taka ta iso gare tana mai cewa gata,
Tankar ba shine yakare mata wanan kallon ba haka yanzu,
Wayar shi kawai yake, ta famar tabawa ya Allah chatin yake yi ko kuma game,
Jibrin ne yadan kalle ta yace ki taya mu zaben zani mai kyau daga cikin wa yan nan pls,
Kurawa zannuwan ido tayi zuwa dan wani lokaci
Sai ta jawo wani mai ruwan zuma, daga ciki yana da wani ado kamar gidan sugar
Shi ta mika masu tana mai cewa wanan kamar yafi dama saboda baida ado da yawa so sai,
Kai ya daga ya kalle ta da mamaki don jin cewa ra,ayin su yazo daya, da ita,
Saboda tun da aka zube zanuwan idon shi yake akan wanda ta zaban
Har zata juya don barin gurin saboda rashin sanin ko may za su yi da zannuwa haka,
Muryan mutumin taji yana cewa zan,nuwan ai kudin su kaza ne,
Dan juyowatayi tace wa mutumin kai malam fadi gaskiya yaushe kudin su ya kai haka,
Jibrin yace wa maryam ta fada masu kudin kayan a takaice maryam tafada masu
Amma kuma sai tace sai dai in har zasu bashi yadda yace ne saboda tai mako,
Dariya duk suka agurin ban da Yusuf wanda dan murmusawa yayi inda ya bukaci mutumin da ya bashi turmi talatin,
Yace idan basu isa ba zai kirashi ya karo mai,adadin yadda ake so,
Daga haka mutumin ya kwashe kayan shi ya tafi yana mai zabga masu godiya,
Inda maryam take ya dan kalla yana mai cewa ki kwashe su ki adanawa anty kafin ta dawo,
Mamaki takeyi zuciyar ta,ace kaya masu yawa haka kuma kala guda,duk, za,a saye, koma na may ye oho,
Sai kawai ta tsinci muryan Yusuf yana cewa duk wace tazo muna wanan farin cikin za a bawa
Cikin mamaki tadan kalke shi kamar zatayi masu magana sai kuma ta bi umurnin shi tafara kwashe kayan zuwa saman wani kujera,
Hira yaci gaba dayi shida Jibrin inda maryam takoma daki ita da yara har zuwa dawo wan su Anty dije,
Bayanin da Yusuf kewa Anty Dije inda take sauraren shi a cikin mamaki,
Turmin zani atamfa da kudi dubu biyar yabawa ko wace mace da tazo sha,anin bukin,
Bakaramin mamaki Anty tayi jin wanan irin kyautar da yai wa mutanen ta,
Don haka daya bayan daya ta dinga aika masu da alherin su gid kuma tana,sheda masu wanda ya basu,
Ta aikawa iyayen mijin ta dashi da kuma, nata,uwayen
Hakan ne yabawa baba daman kara tunawa da zancen shi na son ya hada zuri,a da wanan yaron,
Saidai yasan cewa mutane zasu zarge shi da cew saboda abin hannun shi Yusuf din ne yake son yin hakan, ,
Amma dai shi in son samu ne yana mai son wanan abin ya tabbata,

Bayan buki da kwana biyu Yusuf ya shigo gidan Anty inda ya samay su gaba daya zaune a falo,
Ya saye cikin wata wagambari,mai ruwan sky colour, sai agogon da ya,daura, a hannun shi,
Hular kan shi baka ce sai takalman kafar shi bakake, sai kamshin da ke tashi,
Ganin su gaba daya afalon har mijin Anty wanda ya,shigo garin bayan kwana daya,wuce,
Wani irin nauyin su Yusuf din yaji ,,inda yai, kamar ya koma baya,
Amma sai mijin Ànty din yace mai haba dai kai,ko shigo mana,
Yace haba dai Yusuf kamar wani bako can idan baka sake jikin ka ba har yanzu da Anty naka sai zuwa yaushe ?

Maryam dauko mai cup mu karya tare, inji mijin Anty Dije yace wa maryam din
Yusuf wanda kan shi na kasa bai daga ba yace wa mijin anty ai baya son tea so,sai yafi da, son ya sha kunu, shi,
Da mamaki yake kallon Yusuf din inda yace kai kan iyalinka sun huta, gaskiya da wahala,
Sai kuma yai saurin kai kallon shi ga Yusuf wanda ke shirin zama a lokacin yace
Ya maganar zancen da Dije tace baba yai maku ne kai da maryam, naji shiru mana,
Maryam wace a lokacin tana kokarin zuba mai kunun shi na gyada dake a cikin jug a cup
Wani irin kallin mamaki ta aikawa Anty nata dashi wace itama dai mijin ta take kallo,,
A hankali takai kallon ta ga Yusuf wanda shima kokarin sauke kai kasa yake yi,
Jin gurin yai tsit ne yasa Illiya dagowa yai wa kowa kallon mamaki kai tsaye ya fara magana,
Mijin Anty Dije ya kai kallon shi ga Yusuf din wanda kan shi ke a duke yace,
Yusuf mu ba,zamu so, ace baku shirya dajuna ba kai da maryam ,
Sabo irin yadda muke tare da kai a matsayin dan uwa daga cikin mu,
Don dai ita maryam nasan cewa bazata kyatare zancen mahaifin ta ba,
Da sauri ta kara kallon mijin yar ta don jin abinda yace a kan ta,
Don Allah ya Illiya ka taimaki rayuwata kasa baba ya janye wanan zancen,
Wanda yake kokarin kwace min daga farin ciki na wanda nake kauna
Wanan furuncin nata na karshe yasa,duk kan su kura mata ido,
Yusuf wanda ke dan motsa kunu a cup ya ansa da cewa tabbas maganar maryam gaskiyane,
Tunda tana tare da wanda take son tun da dadewa
Kaga bai dace ace an rabata da wani ba dan wani,
Wanan maganar da Yusuf yayi ta karshe shi ya,bawa mijin anty tausayi so sai
May maryam ke nufi da cewa a bawa baba hakkuri sam bai taba zaton haka daga gare ta ba sam,
Don haka cikin tsawa yadaka mata cewa baki da hankali a she maryam ina maki daukar mai hankali, ?
To ki san da sanin cewa indai babane iyakar maganar shi ce ya fada ba wai zabi yabaki ba,
Don ma dai kawai Yusuf din ya kasan ce shi bako ne daga cikin mu dakin ga aiki da cikawa,
Hawaye ne ya fara silalo mata daga fuskan ta tana sharewa a hankali,
Mijin Anty Dije yace ina ma wanda kikewa ikirarin cew kina dashi din yake, ?
Maryam wacce saboda haushin irin yadda mijin yar ta yai mata a gaban Yusuf kamar wace ba tada gata,
Yasa ko kallon shi ba tayi ba takama hanyar zuwa dakin takawai tana mai share hawaye,
Tukin mota yakeyi amma hankalinshi na ga magganganun da sukayi da safe a gidan Anty Dije,
A hankali ya shafa fuskan shi da tafin hannun shi,
Inda ya hade wasu miyau masu daci da suka tsaya mai a bakin shi,
Har ya isa garin Abuja maganar taki fita mai azuciyar shi,
Bai huta ba ita kuma maman Choima ta haushi da fada akan cewa ya cuce su da ya aurawa Ibrahim da Naimat,
Don may ya musuluntar da ita batare da sanin iyayyen ta ba,
Dukan shi tsohuwar ta shigayi da hannun ta bibiyu tana mai yin kuka da ihu,
Ganin zata iya bata mai lokaci ya sa shi janta a hankali zuwa dakin ta inda ya zaunar da ita a hankali saman gado yana mai ce mata ba gaskiya bane,
Tace mai ai Samuel ya zo bayan baya nan yake sheda mata abinda ke faruwa,
Sai da ya samu yadan lalabata ya wuce zuwa dakin shi,
Rigar dake ajikin shi ya sabule gaba daya tare da jefata saman gadon shi,
Shima fadawa yayi tare da lumshe idon shi yanamai karanto Subbahanallahi, Walhamdullahi Wallahu ,Akbar,
Har zuwa lokacin da yaji zuciyar shi tai mashi sanyi,
Sannan ya mike zuwa bathroom don yadan watsa ruwa, ko zai ji sanyi a rayuwar shi irin yadda yake ji,
Sai bayan ya fito ne yana,saye da wata jallabiya mai ruwan milk, colour,
Yana dan goge ruwa a kan shi wayar shi tafado mai a rai,
Sai a lokacin ya tna cewa yasa ta a silent tun yana hanya,
Da sauri yadauko wayar yana dibawa, kirane kusan talatin da wani abu,
Inda akasarin su duk kurane daga anty Dije sai kuma sauran friend's da abokan aiki,
Kiran karshe dayagani shi ya bashi mamaki don sam bai yi zaton ganin kiranta ba a wanan lokacin,
Ba kowa bace illa maryam da mamaki yake kallon sunan nata yana mai tambayar kan shi ko may take so dashi har takira shi,,
Wayan ya ajiye inda yanufi gurin da sallayar shi take yana kokarin shimfidawa,
Karar wayar shi ce ta katse shi a lokacin don ya mai da ita da karar ta,
Anty yagani rubuce a screen dinwayar tashi alamar itace ke kiran shi,
Dauka yayi amma sai ta haushi da masifa tana mai cewa ina ya shige haka tun da safe take neman shi bata samun shi,
Nan yake sheda mata cew yana Abuja kada ta damu,
Cikin kwantar da murya tace Abuja Yusuf ?
Abuja ka koma baka fada muna ba may yafaru Yusuf kawuce yau ba sallama haka,
Murmushi yai mata a karo nafarko yau tun xa gari ya waye mai,
Yace ba komai Anty tafiyar ce kawai ta riskeni a haka,
Shirune yadan biyo baya batare dakowa yai magana ba daga cikin su,
Kashe wayan yaji tayi abinda bai taba faruwa ba ke nan a tsakanin su,
Yana kashe wayar kamar hadin baki kiran maryam na shigowa
Amma sai ya share kiran nata kawai yatada sallah shi abin shi,
Ya dade a zaune yana lazumi inda yake ta kai kukan shi ga Allah akan Allah yai mai mafita, da kuma zabi na alheri a rayuwar shi,
Ya mike don ya kwanta ko zai dan samu barci yadan huta,
Ya kwanta kamar minti biyar yaji kira ga wayar shi kokarin kashe wayar yakeyi a daidai lokacin da yaga sunan maryam again a saman wayar,
Kamar ya share ta saidai yadaure ya dauka saboda time din da agogo ya nuna mai nadare,
Muryan taji a cikin wani yanayi tana mai ce mai hello,
Inda shima ya karba mata da cew wa,alakissalam,
Sai kuma tai shiru batare da ta furta komai ba,
Idon shi yadan rintse don wani irin abu da yake ji yana taso mai a zuciya,
Yana niyar kashewa ne yaji muryan ta tana cewa Uncle dan Allah ka taimaka min agurin baba ka fada mai gaskiya cewa ba soyayya atsakanin mu ko kadan,
Yanajin tafafi haka yakatse wayar tashi tare da rufe layin nashi yana mai runtse idon shi da suka kada sukayi ja,alokacin,,,,,,, l

SEENABU ZEE MAKAWA YAURI KEBBI STATE,,,
[4/7, 5:57 AM] ‪+234 810 770 2287‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
6⃣7⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR YAURI,

Alhamdullahi Rabbil,Alamin


Ànty Dije tare da wasu daga cikin yan uwan su ne suka tafi kai amarya gidan ta dake a unguwar GRA,
Motoci kusan biyar ne suka zo don daukar a maryan sanin cewa ba wai tana da wasu mutane da yawa bane a garin,
So sai ko jama,a suka dan taru don zuwa rakiyar amarya gidan ta, da misalin karfe biyar na marancen, jumma,a,
A bin gwanin ban sha,awa saboda irin yadda, mutane sukayi don Anty Dije, kusan duk wace take hurda da ita tazo mata wanan karar na buki,
Amarya Naimat tasha ado a cikkn wasu lace farare kal dinkin buba, sai farin mayafi da kuma wani farin sarka mai daukan ido,sai wasu, fararen takalma a kafarta
Idon ta alamar taci kuka saboda irin yadda sukayi mata wani irin lub, lub da su,
Maryam ce kawai aka bari don tsaron gida tare da kau da sauran kayyayakin amfani da suka bari a waje,
Sam bata san shigowar Yusuf din gidan ba saidai muryan shi da ta ji gab da bayan ta,
Inda ta juya a yar razane cikin dan rudewa saboda rashin sanin mutum na kusa da ita,
Fararen shadda ne a jikin shi dinkin tazar ce har kasa,
Hannayen shi a harde saman kafadar shi inda ya kura mata ido kawai a cikin rashin sakin fuska kamar yadda yake a kullun,
Sai da tayi kokarin saita kan ta,tukun, na san nan ta samu bakin yi, mai gaisuwa,
Ya ansa mata kamar kullun a takaice sai dai na yau yana da dan banbanci da saura,
Gurin fridge ya wuce direct inda ya bude ya,dauko goran ruwan Inuwa water,
Kafa kai yayi batare da ya jira kofi ba, ya kama kwankwada, inda duk ya kwankwade ruwan tas,
Yau she su Anty za su dawo ne maryam wace ke kokarin shiga store din su, dan aje kaya ta ansa mai da cewa,
Anjima kadan shiru yayi ba tare da yakara magana ba ,
Gurin kujera two site ya nufa nan yazube sama yana mai cewa Ya Allah,
Akawo ma abinci ne ta tambaye a cikin dan dari, dari,
No thanks kawai yace mata inda ya maida idon shi ya kara lumshewa,,
Aikin ta taci gaba da yi abin ta batare da takara bi ta kan shi ba,
Yusuf wanda ke kwance tankar mai barci sai dai a zahiri idon shi biyu yana tunanen duniya,
Wayar shi ce tai kara gurin da, yake aje a gefen shi,
A hakali ya mika hannu shi ya dauki wayar sunan Jibrin ya gani,
Dan gyara kwanciyar shi,yayi ya na mai kokarin daukar ,
Tambayar shi Jibrin yake, yi ko yana ina ne haka
Sai da ya ja dan guntun tsuki kafni ya ansa mai wayar shi, tu kun,
A takaice ya bashi ansa da cewa gidan Anty mana ,
Jibrin yai yar dariya kafin yai mai magana, tukun
Da iskanci ai ba na fadama cewa zan dan gudo in huta ba kafin su dawo,
Ansa yabashi da cewa an fa kawo kayan da ya ce akawo mai ga mutumin yana neman shi,
Sai da yadan lumshe idon shi, sannan ya dan sukunyar da kan shi yana mai kallon ties din falon yace,
Ya ce gaskiya Jibrin bazan iya zuwa in duba ba saboda ina hutawa yanzu,
Amma zai iya kuzo nan ai maryam tana gidan sai ta tayaka dubawa, ko,
Jibrin din ya ansa mai da cewa gashi nan zuwa tare da mutumin,
Yusuf din ya ansa mai da cewa ya yi kyau sai kun ka raso ina ciki idan kunzo,
A lokacin ne kuma su Assalam suka shigo gidan daga can cikin gida gurin kakan,nin su,
Ganin yana bukatar hutu yasa maryam kiran yaran zuwa gurin datake,
Aiko can gurin ta suka dan bata lokaci sai dai jefi,jefi tana kallon shi idon shi a lumshe suke,
Ba ai wani dadewa ba Jibrin yai sallama tare da mai kayan,
A kofar falo suka yi sallama maryam wace ke zaune da yaran suna kallon a wayar ta takarba masu sallaman su,
Dukkan su a falo suka zube sai kayan da mutumin ke kokarin budewa daga cikin wani buhu,
Zannuwa masu yawa tagani suna fitar wa daga cikin buhun,
Jibrin din ne yasawa maryam wace ke ta waje kira,
Sai da ta dan ja aji irin na mata tukun sannan ta mike zuwa ida suke,
Tun daga nesa ya tsai da hankalinshi gurin ta irin yadda take tafiya,
Tabbas maryam ta, tara abubuwa da dama da sai yanzu yake gani su daga gare ta,
Idan ma don kyau ne ta na dashi uwa uba kuma hali duk yarinyar tana da,su,
Cikin yaga da nuna isa ta yan matan taka ta iso gare tana mai cewa gata,
Tankar ba shine yakare mata wanan kallon ba haka yanzu,
Wayar shi kawai yake, ta famar tabawa ya Allah chatin yake yi ko kuma game,
Jibrin ne yadan kalle ta yace ki taya mu zaben zani mai kyau daga cikin wa yan nan pls,
Kurawa zannuwan ido tayi zuwa dan wani lokaci
Sai ta jawo wani mai ruwan zuma, daga ciki yana da wani ado kamar gidan sugar
Shi ta mika masu tana mai cewa wanan kamar yafi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login