Showing 135001 words to 138000 words out of 255288 words

Chapter 46 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1384

jira har a gama girkin dare ta ci,, ai,
Yusuf na jin su sai bai ko kalli inda suke ba yai kamar baiji abin da,sukeyi ba,
Bai wani dade ba yafita lokacin duk suna ciki gaba dayan su,
Sai, dawo, wan shi suka gane dauke da ledoji a hannun shi,
Kayan su fruit ne da snacks sai drinks kala,kala, leda guda,
A sanyaye yake cewa anty ga shi nan abawa kowa ya dauki abin da yake so,
Kuma abar Assalam yadauki duk abinda ran shi ke so a ciki,
Duk da anty dije tagane cewa saboda maryam ya sayo don yaji ana cewa bazata ci dafa duka ba,
Mamaki tayi sosai da irin halin halarcin rayuwa irin na Yusuf ,
Sai tunda yafita lokacin bai kara dawowa gidan ba har zuwa dare,
Anty ce tai karfin halin buga mai waya don taji ko lafiya bai zo cin abinci ba,
Sai cewa Anty ya yi tayi hakkuri ba zai samu zuwa ba ya tafi wani guri
Dariya take mashi a lokacin tana cewa kodai ya tafi gurin sarrakuwar ta ce,
Maryam wani haushi ya kama don dai ita kawai haka taji bata kaunar Sadiya a rayuwan ta,
Tafi mai kwadayin ya samu wata yarinya kaunan Safiya da ake cewa Sariya,
Sariya tana da kyau ga kuma ilimin addini sosai a tare da ita,
Amma wanan sadiya din inbanda fashion da nuna tsawo bata san komai ba,
Muryan Ejoma ce, kecewa gaskiya sister bana son zance yariyan nan da brother sam, sam,
Wai kin san may rana ya kirata a waya yace ga maman Choima su gaisa,
Kawai sai cewa tayi ita wai batasan yadda zata gaida ita ba gaskiya,
Amma kin san may wallahi ni nagane nufinta sarai saboda muna Christian ne fa,
Kin san wasu mutane basa iya boye kyamar su a gare mu,
Shiyasa nima da yace a wanan gidan zan sauka da farko har na shiga damuwa amma sai gashi daga baya yake ce min da kaina zan bashi labarin halinkirki naku,
Maryam na,jin su sai tai dariya kawai don tasan ta kuru da an raina mata hankali
Don dai da farko tayi niyar nuna rashin mutuncin hada ta daki guda, da Ejoma da akayi,
Gurin da zata ajewa Ejoma kaya take dan gyarawa,
Sim din da ta dade da boyewa, ne tagani ya fado daga inda ta boye,
Cikin sauri ta,dauka ta na dubawa a hankali cikin dubara ko wani abu ya samay shi,
Sawa tayi acikin wayanta don ta diba ta gani ko zai yi,
Kira guda ya shiga cikin muryan shi mai kama da mai jin barci,
Assalamu Alaikum, wani iri taji a zuciyar ta,da sauri ta kashe wanya takoma saman gado ta zauna,
Text ta rubuta mai kamar haka,
Tai,mako a cikin addini sadaka, ce ita sadaka riga kafin matsifu ce,
Ka, kara taimako a saman taimakon da kakeyi ka kara ganin alheri a rayuwan ka, @@
Ya dade yana kara nanata karantawa yana mamakin mai turo mashi da wanan texts din
Don yadauka tunda ya musulunta andaina ke nan ,sai gashi yau yaga mai

Shine a tare da,Sadiyar shi zaune a cikkn motar shi,
Suna hira don tun da yazo garin yaune karo na biyu da yazo gidan su hira,
Wani kanin mahaifintane yazo zai shiga gidan nasu a lokacin
Ganin bakuwar mota akofar gidan na su ne yasa shi da,katawa bai shiga ciki ba kamar yadda yai niya, shiga.
Yaran yake tambaya ko motar waye a kofar gidan nasu,
Wani dan yaro cikin wasu dinkin yadi blue yaje cewa baban nasu ai anty sadiya ce da saurayinta,
Kamar ya wuce amma sai wata zuviya tace yahe yagani kowaye,
Ganin shi tafe inda suke yasa Yusuf yai saurin fito daga cikin motar
Har kasa ya tsugun na yana gaida kanin mahaifin nata dace shike bi wa mahaifin ta gurin haihuwa,
Bai karba gaisuwar da Yusuf ke mashi ba sai nuna shi da yatsu yakeyi,
Yace kai Sadiya ashe abinda ake fadi a kan ki gaskiya ne,
Yanzu ace kin rasa wanda zaki jawo muna sai wanan Furen Jujin,
Dam gaban Yusuf yafadi don jin sunar da aka kirashi dashi, wai FUREN JUJI,
Mutumi yaci gaba da fadin wa zaki jawo abin kunya ke da mahaifinki,
Don mutanen gari su ce kwadayi yasa muka baki Dan Ka Tuba, watau, (TUBBABE),
Kuka Sadiya tafara yi wi,wi don jin kanin mahaifin nata yafara nuwa Yusuf halin shi,na jahilai ,
Barin fada maki gaskiya badai acikkn zurian mu ba Sadiya,
Don babu mai kawo muna dan gin kafirai a gida wai jikoki,
Ya juya inda yusuf yake duk kai a kasa don ji yayi kamar kasa ta tsage ya shige irin yadda yake ji,
Yace wa Yusuf din tun wuri kaje ka bidi irin naka ba a gidan nan ba kaji,,,
Juyawa yayi ya shige cikin gidan nasu yana ta zabga masifa shi daya,
A, hankali ya juya bude mota yashiga Sadiya wace kanta yake a duke tana ta faman rusa kuka wiwi,
Da kyat Yusuf yai gyaran murya ya ce ta yi hakkuri tabar wa Allah komai yafi,
Ita ko sai hakkuri take ba Yusuf din cikin kuka tana mai mashi magiya cewa kanin mahaifin nata baida hankali sosai ne,
A dadafe sukayi sallama da juna yatafi zuciyar shi a cushe kamar zata fito mai,
Don irin cin fuskan da akai mai yai mai muni,har ji yayi kamar ba,zai iya tuki ba,,,,

Tunda yadawo yake zaune a falon shi ji yayi tankar kan shi zai tsage mai a lokacin saboda irin ciwon da yakeyi mai,
Ga zuciyar shi na mai wani irin soya kamar zata fashe mai,
Zaune yake asaman kushin ya mai da kan shi baya saidai kuma yadafe goshin shi da hannun shi guda,
Wasu hawaye madu dumi yaji sun gangaro mai a fusaka saboda tuna sunan da aka kira shi dashi, wai FUREN KAN JUJI,
Ya Allah ya furta a hankali yace Allah kai kasan dalilin yina a haka,
Nakuma gode maka ya uba giji na da ka bani ikon bin hanya madaidaiciya,,
Idon shi ya kara lumshewa yana ma zubbda hawayen bakin ciki,
May ye laifin shi a yanzu kuma bayan dashi da su duk matsayin su guda a gurin ubangiji,
Da wanda yai she kara dari da wanda ya shigo yau duk abu guda suke a gurin Allah subbahanahu, wata,ala,
Dangin shi kuma ko ya suke shi ba zai guje su ba saboda sune nashi,
Bai san ko daga cikin su akwai mai rabon shiga musulunci ba a ta dalilin shi,
Irin tunanen da yai tayi ke nan har dare ya raba tsakiya ya kasa barci, ga wani daci da yake ji a makoshin shi,
Sai zafi da yaji jikin shi ya fara yi kamar wanda fever ke shin kamawa,

Kiran wayan shi take tayi tun tana jin yana,shiga sai ya katse layin da kan shi,
Anjima kadan kuma takara kiran shi amma sai taji ya katse, wayan
Daga karshe ma sai taji kawai ya kashe wayan ma gaba daya,
Tsuki tayi ta wurgata da wayan ta kwanta taci gaba da zubar da hawayen bacin rai,
Tana mai Allah waddai da irin halin baba Ado wanda bai san darajan addini ba sai kuri da shi,
Ko a wani nafsi akace mai an kya maci auren wanda ya tuba
Ita dai a sanin ta baba Ado ya hada da al,adace kawai in bashi ba don mai zai kira Yusuf din da wai furen kan juji,,
Sai zuwa dare tayi taji kira ya shigo mata a waya lokacin har ta yi shirin barci, duk da tasan cewa yau ba zancen barci gare ta,
Jibrin tagani barobaro a wayanta, saida tai tsuki tadauka da fadin cewa kaga damar daukar wayan
Don kaga ina kiran ka shine harda kashe min layi ko,
Dariya yayi mata ya ce haka kawai zan yarda ki damay ni ga banza
Kuka ta farayi tana aheda mai abinda Baba Ado yaiwa Yusuf yau da yazo gurin ta,
Innalillahi kawai Jibrin ke ta nanatawa alokacin saboda maganar tazo mashi a ba,zata,
Yace wai ko dai da gaske Baba Ado bai da hankali kamar yadda mutane kece mai mahaukaci
Ra,ra,shin ta ya yi yace ta bari yaje gurin yusuf din yagani ko ya akayi,
Yusuf wanda alokacin yana can cikin bargo yana jin wani irin amai da zafi na damun shi,
Kuma duk yabi layin wayan shi ya kashe gabaya ba mai kiran shi ya samay shi a lokacin,
Jibrin gidan Yusuf din yazo direct don yadiba shi am.a sai yaga duk ko ina a kulle yake,
Dole yakoma badon yaso ba don yana gudun ya ta dashi daga barci,


ZEEE. MAKAWA
[3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN, JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
5⃣7⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA,

Ya Allah mun gode ma dakayi acikin Al,uman Annabi Mohammad S,A,W,
Allah kaba ikon koyi da Sunnan a tafarki mai umfani,
Ya Allah katai make muslimi kasar Syria da ma na duniya baki daya,
Ameen Ya AllahπŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘



Har muslim sha dayan rana ba labarin Yusuf anty dije sai fada takeyi cewa ya na biwa ta mutane yaki zuwa ya yi breakfast,
Ganin sha biyun rana yana batun yi yasa takara, kiran nobar wayar shi ko zai shiga,
Cikin sa,a tasamu kira guda ya shiga, sai dai wayar tana ta ruri har ta kusa katse wa ya samu da kyat yadan daga wayan,
Yanayin muryan shi kawai ya wadatar da mutun yasan cewa yana acikin wani yanayi
Gaban Anty Dije ya fadi Dammm,
Jin muryan kanin nata a cikin wani bakon yanayi da bata sani ba,
Cikin rawar murya tace Yusuf baka da lafiya ne ko may ke faruwa haka, ?
Dan ajiyar zuciya ya sauke mai dan karfi a lokaci guda,
Hankalin Anty duk yatashi ga network kuma ba kyau bata jin shi sosai abinda yake cewa,
Cikin daga murya take kwalawa maryam da ke kitchen kira,
Da sauri maryam ta iso falon don dajin kiran tasan cewa kiran na sauri ne,
Hannunta take kokari gogewa a lokacin saboda ruwan dake a hannun nata,,
Anty ce ke kokarin mikewa tsaye tana sabe da Abubakar dake shan nono,
Maryam don Allah shirya ki je gidan Yusuf ki dibo min ko lafiya,
Don kin ga ba dama in aiki wanan Yarinyar don kada yan uwan ta su ganta a agari,
Wani irin abu maryam taji amma ba tada yadda zatayi don ba zata iya yiwa antyn ta musu ba,
Jiki ba karfi ta shiga dakin ta tafara shiri, wasu, dongon rigar material ta sa inda tasa wandon lages ta ciki,
Sai kamshin da ta feshe jikin ta dashi tsab kamar ba a kitchen ta fito ba duk da dama tayi wankan safe ko,
Ita aganin ta ba kwalliya tayi ba amma duk wanda ya gan ta zai zata gurin wani buki zata alokacin,
Kudin mashin anty ta mika mata, har zata fita takara kiran ta tace da ta tafi mai da kayan breakfast din shi can,
Dole haka maryam ta dauki kayan niki, niki zuwa inda zata tari mai mashin,
Kofar gidan kamar a rufe take amma dai don ta tabbatar sai ta dan tura a hankali,
Mama ki tayi lokacin da taje a bude yake, A,she tun da yatafi, massalaci sallah a,suba da yadawo bai kara rufewa ba,
A,hankali take tafiya, ta ratsa wani dan dogon corridor sanu a hankali ta isa kofar shiga folon ciki,
A kwance ta hango a falon cikin gidan a kasa, bisa carpet,
Yana sanye da da wata yar far singlet da wando short, nica,
Kamar ta koma amma kuma yadda taga yanayin kwanciyar shi, yasa ta kasa wuce wa,
Hannun shi guda yana dafe da goshin shi,
A hankali ta isa gurin shi, ta durkusa daidai tsawon shin,
Gaban tane ya fadi ras don ganin yadda ya koma cikin kwana guda,
Ta kasa wani magana a lokacin sai kallon shi takeyi kamar taga wani abu,
Kamshin maryam din yaji a lokacin hakan yasa shi saurin bude idon shi,
Tabbas maryam din ce a gaban shi ba wai shake bane,
Cikin wata irin murya yai magana tankar ba shi ba,
Yace Maryam,
Kece a tafe yanzu ?
A sanyaye tace mai eh nice
Anty ce tace inzo in diba ka ko lafiya ? tun, jiya baka zo cin abincin ka ba,
A cikin zuciyar shi yace Allah sarki Anty na,
Sai,da ya lumshe idon shi sanan ya ce mata, wallahi maryam,
Bana jin dadin jikina ne tun jiyan kirji na kamar zai fashe ,
Wani irin tausayin shi maryam din taji, don yadda taga ya dafe kirjin da zai dan tashi zaune,
Ya,dan daga kan shi ya kalle ta, yace na so inyi karfin halin zuwa gidan amma ba,zan iya ba gaskiya,
Wani iri taji a ranta sai ta dan lumshe idon ta a lokacin taji hannun shi cikin nata,
Wani irin zafi taji radau alamar yana cikin zazabi mai karfi a tare dashi,
Zuwa kirjin shi yakai hannun nata yana cewa maryam kirji zai fashe saboda yadda nake jin shi,
A hankali maryam din ta saurin cire hannun ta a cikin nashi,
Shikuma ya maida kan shi saman carpet din ya kara kwantawa,
Murywn ta yaji tana cewa tun yaushe ne baka da lafiya ya Yusuf ?
Yadan kalle ta a sanyaye idon shi sunyi wani lusu,lusu da kyat yake iya budewa,
Tun jiya nai bayan nadawo gida, nafara jin haka,
Tace to ka kasha magani ne, ?
Kai ya girgiza mata tankar yaro karami,
Mikewa tayi tsaye daga inda take a tsugune tace barun hada ma ruwan wanka tukun, sai kaji dadin yin break din,
Tamike a hankali ta nufi cikin kuryan dakin ta hada mai ruwan wanka,
Har da maclen sai da maryam ta matsa mai a brush tare da aje mai tawul a gefe,
Sanan tafi tace mai bissimila
Da kyat taga ya mike tare da taimakon dafa kujera da bango,
Maryam na ganin ya shige ciki tai sauri cire hijab din ta,
Ta fara gyara mashi falon duk da tsab yake baida wani datti so sai,
Saidai kuryan dakin ne keda dan gyara shima kafin yan mintina yakoma tsab,
Ta kwashe kayan wankin da taga a wa,wa tse takai, bakin kofar bathroom din ta aje,
Yan,kudaden da tagani ta mayar a karkashin filo ta aje,
Traveling baga din shi ta bude tafitar mak da wasu simple kaya marasa nauyi, ta aje agefen gado,
Ta koma falo ta aje mai kayan break din ta yadda zai iya jin saukin ci,
A kofar dakin ta tsaya tana mai ce mai Ya Yusuf ga abin karin nan fa kada yai sanyi,
Yana zaune a bakin gado lokacin daure da wani farin towel iya gwiwar shi,
Ta juya zuwa falon batare da tashiga cikin dakin ba ko daga labulen kofan,
Tun a cikkn dakin Yusuf yaga canji don yaga ko ina fes tankar ba wanda ya,ba ri da kazanta ba kafin ya shiga wanka,
Haka ma falon yake tass kamar bashi ba sai kamshi ke tashi hade dana cooler
Gefe tadan koma nisa dashi kadan tana kallon yadda yazauna ya harde kafa guri guda
Amma yana cusa abinci da kyat kamar mai cin magani,
Kiran wayar Anty ce ta shigo a wayar maryam din
Cikkin daga murya Anty ke cewa maryam ya akayi gaki shiru baki dawo ba balle muji ko lafiya,
Ganin zuwa kawai tace wa Anty n nasu batarr da tai mata wani bayani ba akai,
Ganin maryam na kokarin hada kayan da yaci abinci yasa shi sauke nunfashi har sai da ta juyo,
A hankali ya furta mata nagode kwarai maryam, ina gaid Anty,
Jibrin ne yashigo falon da sallamar shi yana cewa
Man don Allah dai kayi hakkuri wallahi naso zuwa tunda safe
Sai kawai muka tafi unguwa ni da baba diban wani dan uwar shi da bsi da lafiya,
Ashe haka kukayi da wanan mahaukacin Ado wanda bai san Allah, ba,
Shi har ya,na da ikon da zai gayama wanan magana haka,
Ai gara kai sau miliyon a,kanshi, wanda ko addini bai sani da har zai kiraka da wai tubabbe dan furen juji,
Kai kawai Yusuf yakada yana murmushin karfin hali,
Sai kuma ya tuna da maryam wace a lokacin har ta gama sa kayan acikin basket ta mike tsaye ko,
Ganin Yusuf ya kalli maryam yasa jibrin shima saurin kallon inda maryam din take,
Sai alokacin ya tuna cewa tana gurin ai, bi kamata yaita sake layi ba haka,
Koma maye ai ta gama ji ko a lokacin don haka tai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login