Showing 114001 words to 117000 words out of 255288 words

Chapter 39 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1374

suna bayan mota zaune inda Safiya ke zaune gaban mota tare da Jibrin,
Iyakar burgewa sun burge Maryam sosai tun lokacin da Anty tace wa Safiya ta zaune gaba tare da Jibrin din,
Saida suka tsaya wani shago sukayi mai tsaraban kayan fruits kala,kala shake a leda duk da Jibrin yace kada su saye, akwai shi cike a gidan,
Amma sai Anty Dije ta, ce su dai saye tunda ba,a zuwa gaida mutum hannu saje,
Zaune yake saman sallaya a folon shi ya kunna tashar madina yana sauraron kira,a,
Yana saye cikin wata yar farar jallabiya mai guntun hannu,
Da sallama suka shiga inda Ibrahim yatare su cikin mutumci,
ร€nty Dije tace a,a lalai Yusuf jiki yai kyau, tunda yau gaka zaune,
Yana kokarin tashi zaune don tariyae su hannun shi yana dauke da casbaha, yana ja,
Da murmushin maganar da anty tayi yakai zaune da kyau saidai bayan shi na jingine a kujeraa,
Kafin ya kai karshen murmushi sai Anty Dije takara cewa gaskiya dai ya kamata yanzu ace Yusuf ka aje mata kodon taimaka maka da wani abu,
Yar dariya mai sauti yakarati daidai lokacin da ya zauna da kyau Assalam yana kusa dashi zaune,
Jibrin wanda ke shigowa adaidai lokacin yaji maganar da Anty taiwa Yusuf sai ya cabe zancen da cewa ai barshi kawai anty,
Dama akwai wata Cousin sister dina da ta sani gaba da zancen Yusuf tunda dadewa,
Ibrahim dake ta gurin fridge yana aje ledojin da suka shigo da su yace,
Aiko zakayi fada da Aisha idan taji ka da wanan zancen,
Kai Aishan may can inji Jibrin wanda ke kokarin zama saman kujerar da Yusuf ya jingina akai,
Daidai lokacin yadago kai inda Safiya da Maryam suke zaune guda saman kujera guda tana zaune a hannun kujerar,
Murmushi yai masu yana mai ansa gaisuwar da safiya tai mai,
Itama maryam gaishe shi tayi a hankali tare da tambayar shi karfin jikin shi,
Duk hiran da akeyi daga Maryam har safiya babu mai cewa komai daga cikin su,
Sannan ita Maryam bata jinko mai gamay da Yusuf har kasan zuciyar ta,
Kamar yadda shima Yusuf din bai, jin komai gamay da maryam azuciyar shi sam,.
Dan daukar ta yajeyi a matsayin yan uwa kawai daga ita har Anty Dije,
Daga kofar shigowa gidan suke jin murya ana sallama,
Ibrahim ne ya leka dan ganin mai yin sallaman alokacin
Baban su maryam ne da Anty wai yatafi gida ake cemai sun zo nan mai,gidan bai jin dadi shi ne,
Duk sunyi mamakin ganin baba amma sai suka ga cewa kanin ya illiya ne ashe yakawo shi,
Baba yai mai fatan alheri tare da fatan samun sauki,
Anty Dije ce take cewa baba yau ba,a fita kasuwa ba ke nan ko ?
Kaiyya Dije ai kasuwan sai a hankali yanzu, mutum ya fita tun safe karshe baifi yasamu abin sayen abincin rana ba kawai,
Yanzu kinga aiduk dan jarin ya karae sai maneji nakeyi, kawai,
Allah ma ya taimakeni nasamu makwaci mai albarka shike taimaka min watarana,
Baba bai dade ba ya mike yana cewa to shi zai koma, inda su Assalam ke cewa baba tsoho ka sayo muna mangwaro a kasuwa,
Maryam tace akin a saya maku nawa kuka bashi jari,
Baba yace a,a yar Baba kyale su ai zan sayo masu ko kadan ne,
Saidai ba kamar da ba leda ce ya miko wa Yusuf yace abin gyaran baki nagani a hanya nasiyo ma,
Jibrin ne yamike yabi bayan baba da yara suka bishi har kofa suna cewa ya sayo masu abu kaza da kaza,
Sai ga baba yadawo cikin mamaki da kudi rike a hqnnun shi yana gwadawa Anty dije kudin zaikai dubu biyar,
Yadinga sa masu albarja dafatan alheri a rayuwan su,
Sai da baba ya wuce Anty dije tacewa maryam ta dauko wa Yusuf fruit ya sha,
Yadan daga kai yakalli anty yace da na anbarshi ai, don ban dafe da sha ba,
Maryam wace a lokacin har ta dauko wani plate ko daga ciin basket din abincin da suka shigo da shi,
A gaban shi ta aje fruit din har zata juya sai Anty tace mata,
Bude ledar da baba yakawo mugani, ko may ye acikin shi haka, ?
Zogala, ne mai yawa hade da kayan gyaran shi
Wani plate ta,dauko ta juye aciki inda Anty, ta bukaci a zuba mata,
Tayi hakane don Yusuf ya sake jiki yaci zogalar don zai gyara mai bakun shi,
Har safiya saida suka vi zogalan amma banda maryam wace ke zaune ta kura ma tv ido tana kallon yadda ake rubuta haruffa kira,ar da akeyi,
Ke baza kici ba ne, yatan baye ta a hankali saida safiya tadan tabo ta sannan tagane da ita yake yi,
Kan ta dake kasa ta girgiza tana wasa da wani dan stone da ke makale a gefen kujera,
Idon ta kem akan shi sai yanzu ta ga irin raman da yayi cikin kwana biyun nan,
Harda wani dan kwarmi kwarmin gurin idanun shi yayi,
A hankali yake cin zogalar shi hankali kwance ba abin da ya damay shi,
Kallon shi sosai taba da himmar yi, hakan yai daidai da dago idon shi daya don yace ta miko mashi ruwa,
Kanta ta mayar kasa da sauri, cike da jin kunyar shi na kama ta da yayi tana mai kallon kurulla,
Maryam help me with water pls,
Yace alokacin da ya kura mata ido,
A kunyace ta ansa mashi da to,
Tamike a hankali har zata fara tafiya sai kuma ta tsaya tadan kalli inda yake tace mai sanyi ko kuwa,
Kai ya girgiza mata alamar a,a mara sanyi yake so,
Goran ruwan majidadi water ta aje mai a gaban shi, ruwa mai kyau da tsabtar sha,
Sai cup da ta hado mai dashi nan yaron anty Abubakar yaga ruwa sai yaron ya hau tsalen cewa abashi ruwan yasha shi ma,
Yaron na,ta kokarin zillowa daga jikin uwar shi,
Abubakar sadiq ko ruwan kake son shane inji Yusuf wanda hankalin shi ya kai ga yaron,
Kyale shi kawai, a,a haba anty ruwa fa yake so, ko banza aikin san mai sunan ba abin wasa bane fa,
Sunan amin ma,aikin manzon Allah ne, shiyasa nake girma ma duk mai wanan sunan,
Ruwan ya tsiyaya a cup ya cewa Maryam miki min shi yasha,
Yaron ke faman kwankwadar ruwan amma ita maryam duk wani irin shock ke jan ta,
Saboda dan hucin numfashin Yusuf dake bugo ta,
Shima bangaren Yusuf din hakane yake ji kamshin turaren Bushrah da black oud din data shafa duk ya wanu susuta shi,
Zogalar da yadaina ci ke nan saboda wani irn mugun kasalar da ya sauka i a lokaci guda,
Assalam ne ya cinye duk sauran zogalar
Idon shi yana a lumshe bayan shi da wuyar shi suna jingine da kujera,
Kamshin yakara dukan hancin shi abinda ya sanar mai da cewa maryam takara zuwa kusa dashi ke nan,
Muryan tace tana ce mai ga ruwa ya wanke hannuwar shi,
Thanks a lot ya furta a yar siririyar murya ta yadda ba kowa ne zai iya jin shi ba,
Bayan ta yabi da kan lo nadan second sai yai sauri ya kauda kan shi dan guda shiga hakkin ido,
Ita ko maryam tana shigowa falon daga gurin da taje zubar da ruwan
Sai ce masu tayi tana mai kokarin daukar gyakenta anty mutafi ko,?
Jibrin muke jira yadawo dafa sayen magani ai, ko,
Dole ta koma ta zauna saman hannun kushin din again zaman da yai daidai da kiran wayar ta,
Kamar kada ta dauka saidai ta daure ta ciro dan ganin kallon da Safiya tai mata,
A,A ne kiran ta saidai kuma ta tsinci kanta da jin nauyin ansa kiran nashi,
Har kiran ya katse bata dauka ba, tana kokarin mayarwa a jakanta ne wani sabon kiran yakara shigowa,
Dole badon taso ba tadauka tana mai cewa Assalamu Alaikum,
A hankali take ansa mai maganar sai kuma tamike tsam daidai lokacin da take cewa mun fitane zuwa unguwa, duk kan mu
Idon kusan duk suka bita da, bishi a lokacin kowa da abinda yake sakawa a ranshi,
Shiru yadan biyu baya a falon sai Yusuf ne ke, cewa Assalam gobe tare zamu tafi massalaci ko,
Sai a lokacin Anty Dije wace ke wani tunane can ta dan nisa tana mai cewa,
Har ka ji saukin fitane Yusuf aidade ka bari har ka, kara, ji sauki, ko,?
A haba no,no,no Anty ai zan iya zuwa insha Allah I am ok now,
Kaiwa a shirya min shi, mutafi,

Zaune yake a gaban dan dan matashin dattijon yana taunan goro yace wallahi Ema ina fada maka cewa shi nagani a massalaci dazu,
Mr Ema ya dan ce no,no,no nafadama bashi ba bashi ba,
Joseph ba zai zo wanan gariba again
Saboda idan yabar zuwa wanan garin, zai dai na sa addin ku a zushiyan shi,
Amma waik,a she min kagani Joseph namu a mosque naku karya ne
Isowar Edowed shi ya tsayar da zancen su da yare suke gaisawa bayan sun gama gaisawa ne Edowed ke ce mai ashe Joseph yazo ne,
What, yafada da karfi har yana dan yi kamar zai mike tsaye sai kuma yakoma ya zauna saboda wani irin duhu da yake gani,
Dauda wanzan nata cewa to Ema nikan zan shige ke nan sai wani lokaci ko?
Kai douda idan zaka tofi ka wushe abunka mana may,nene ne kana damay ni haka,?
Rana ko yar biyar bai samu ba gurin uhan gidan nashi da ko yaushe yakewa fadanci,

Tsaye yake a gaban wani standing table dake dauke da kwalaben giya kala,kala,
Magana yake makama da fada ko kuma rada,,kamar wanda bai,son aji may yake cewa
Samuel wanda yai niyar fita cikin shirin shi nazuwa evening service, jin abinda mahaifin shi ke cewa yasa shi komawa baya yasha jinin jikin shi don sauraron uban,
A hankali ya,koma baya, don gudun kada uban ya gan shi,
Maganar uban ke mai yawo a kunnuwar shi, don may mahaifin su zai ma dan uwan shi haka,
Bayan irin girmama shin da dan uwar nashi ke yi amma ce duk,mahaifin su bai gani ba,
Saboda kawai ya canza addinin da yake bukata, don ra,ayin shi,,,,,
Gaskiya bazai iya kyale wanan zancen ba zai fadawa brother din shi don yasan abin yi tun wuri,
Yadauki wani ikacin don ya gwadawa uban cewa baiji komai ba,
Da harara Mr Ema ya bishi don yau duk haushin kowa yake ji,
Har yadan gwauta shi sai ya sa mashi kira yadawo baya,
Kallo guda yai mai sai yaji duk mahaifin nasu yafita mai a rai,
Tambayar shi yayi ina zai tafi sai yake cewa uban na shi zai tafi, service ne,
Fuska murtuk yakada mai kai alamar yatafi,
Saida Samuel yagama fada ma Yusuf duk abinda yaji uban na fadi ga waya,
Yusuf ne cikin murmushi, yake kwantar wa da kanin shi Samuel hankali da cewa ba abinda zai samay shi insha Allah,
Amma sai Samuel din cikin rudewa yake cewa no, brother you know how uncle Jackson is,
That man can kill person
"I swear,
Samuel just cool down your mind, Dad will not do anything, successful to me,
Da haka yai,ta kwantar wa Samuel da hankalin shi shi har ya yarda




ZEEE. MAKAWA,,,


๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ
FUREN JUJI
๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ๐ŸŒบ
4โƒฃ9โƒฃ


ZAINAB IDRIS MAKAWA


Sosai maryam ta maida hankalin ta ga karatun dake a gaban ta,
Na ci gaban zango da,zasu shi badadewa ba saboda sani cewa FCE ba wasa ga al,amarin karatu a gare su,
Cikin sauri sauri take tafiya,saboda kada, ta makara,
Tsaye take a bakin titi tana jiran taxi yazo, sai motoci ke gittaiya a gaban ta,
Wata civic ce da ta,wuce tayo ribas baya ,baya,zuwa inda take, kokarin tsaya wa motar take yi,
Ganin haka yasa Maryam kau,da kan ta gefe, guda, kamar bata gan shi ba,
A hankali ya sauke glass din motar shi yana mai mata wani kallo cikin natsuwa,
Ina zaki haka ne, don na wuce dazun nan kadan naganki tsaye a nan,
Sau guda ta kalle shi ta kau,da kai, saboda kwarjinin da yai mata a fuska,
Murmushi yayi yace, well,
Kiyi hakkuri in sauke ki pls kada ki makara, don ko baki fada ba nasan cewa, F C E zaki dan ganin yanayin shigar ki kawai ya nuna min haka ya karasa zancen shi yana mai daure fuska,
Kai ta,daga ta dan kallan titi ko zata samu motar da zata shiga,
Titin, kamar an, share ba taxi tafe a lokacin, don haka ta daure duk da zuciyar ta bai kwanta daganin mutumin ba,
A hankali ta zagaya zuwa dayan gefen, na mai zaman banza, ta bude a hankali, ta zauna,.
Nagode tace batare da ta kalli gefen shi ba, wakan dan kwairo ya na Sarkin Das Billiyaminu,
Kidan, wakar na tashi kamar speaker din zai ruguje, abayan motar
Sai sanyi A, C da yacika motar da kamshi air freshener da ya gauraye motar,
Tsam Maryam take a cikin motar zaune kawai take amma kamar, jira takeyi, a ce mata ke ta sheka,
Shi bai mata magana ba ita ma din dai batai mashi magana ba,.
Daidai get din farko yadan waigo inda take, a karo, na biyu yai mata magana,
Tun bayan shigar ta motar, tambayar ta, yake yi,
Wani guri zai sauke ta a cikin compound din makarantar,
Da musali har suka kai inda zata sauka motar ,sai a wanan lokacin maryam wace hankalin ta ya kwan,ta ganin cewa, sun shigo cikin mutane,
Tace na gode Allah saka da alherin sa,
Dai,dai yana ribas da motar, shi, ya dan waigo inda take yana cewa kai ba komai ai
Iam Alhasan Bashir, daga zaria GTBank, manager,
Saida maryam ta waiga saboda jin abinda yace, ina fatan hajiyar zata fada min, sunan ta,

Maryam Abdullahi Bobi,
Ta fadi a takaice batare da ta kalle shi ba "nice name yace, kawai
A,lokacin da ya balle mata marfin motar ta fita, batare da kara kallin shi ba,
Har yai nisa da motar ya yadan lumshe idon shi badon komai ba sai don shakar kamshi turen ta da yayi, a karo na biyu,
Yana son mace mai yawan amfani da kamshi,
Yanason mace kamila mai aji,
Yana son mace wace bata canza halittan jikin ta,
Dan ganin Maryam da yayi yau sai yaga cewa duk ta, tara, wa yan nan abu,buwan da yake bukata,
Maryam Abdullahi bobi ya kara nanata sunan a hankali,

Tsaye yake a bakin motar shi, hannun shi a cikin Aljihun wandon shi,
Sam bata ganshi ba sai kokarin gyara saba jakar ta takeyi
Jikin tane yabata cewa ana kallon ta sai kawai ta daga kan ta sama, gurin da tasan ana anje motoci,
Ido biyu, sukayi da A,A dinta yana tsaye hannun shi guda, a cikin aljihun shi,
Sai guda da ya rike kofar motarshi kafar shi na ta ciki kadan,
Damm gaban Maryam ya ba da, amma sai ta dake kawai,
A, tsanake take tafiyan ta batare da ta nuna mai wani darrr dan ganin shi ba kamar yadda takeyi da,
Mamakin yakara kama shi kwarai don bai yi zaton haka ba daga gare ta,
Tafiya yakeyi, amma hankalin shi na ga wanan guy din da yaga ya aje Maryam,

Wayan ke ta kara batare da an dauka ba, har wayan ta katse,
Wani sabon kira takara yi a karo na biyu, sai,dai ko rabi ba,ayi ba a ka daga wayar,
Ke yar kauye ya kike inji Jibrin yaje cewa Sadiya Mohammed joda,
Bayan sun zauna tare da yi wa juna barkwanci a tsakanin su,
Sai Sadiya tai shiru
Jibrin yace ke wai lafiya kika kirani da wanan ranan haka,
Hmmm ai kaima kasani don Alkah dai mubar wasa muyi maganar gaskiya yau,
Jibrin ina mutumin ka ne wai tafada tana yar dariya kasa,kasa,
Duk da ya gane watake nufi amma sai ya dake yana ce mata,
Wai wa kije nufi ne sadiya, haba Jibrin don kaga ina mutuwar son abokin ka shine kake min haka,
Wai har yanzu ki na ga son shi ne,, Sadiya ?
Murmushi tayi, tace ai kaima ka sani Jibri, ka dai ki hada mu da shine kawai,
Tausada taba jibrin don ya dade da,sanin cewa sadiya tana son Yusuf da da dewa,
Amma yau sai ta ba shi tausayi saboda irin yadda yaga,tana mutuwar son

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login