Showing 102001 words to 105000 words out of 255288 words

Chapter 35 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1754

mama zan sa rai kuma haba dai,
A sanyayae takara fadin to anty zanyi yadda kikace din,
Kafin sukashe wayar Anty takara jaddada wa Maryam takira Yusuf taimai godiya dan Allah,
Kayan wanki take hadawa amma tunanen yadda zata kira layin Yusuf da anty ta turo mata, takeyi,
Aikin ta tacigaba dayi inda yan kannen ta maza da mama tahaifa a wanan gidan ke taya ta,
Har zuwa dare takasa aiwatar da abinda aka umuce ta tayi,
Gashi kuma Anty tace mata don Allah dai takira tayi godiya,
Ita kuma bata son a hadata da Allah tayi abu taki yin sa,
Saida tagama komai har yar fitilar kwan dake makale a dakin mama yau tasamu wanki ta kuma sa ancika shi da kallanzur,
Yau mama tadan ji dama don har ta dan dago daga kwanciyae da takeyi kullun,
Abincin da kishiryar ta tayi ne aka dan zubo mata awani plate na silver
Ta danci shi sosai don har tana, yar lasar miyar dake a kwano duk da bataci wani abu mai yawa ba,
Wayan ta tadauko, tafar lalubar nobar Yusuf da aka turo mata,
Yusuf yana tsaye a dakin shi na hotel shi kadai bayan fitar Jibrin wanda, suka gama shirin yadda zasu tafi gidan su, Safiya gobe,
Wanka yafito a lokacin yana dauke da wani dan farin towel a wuyan shi,
Karar kira ce tashigo mai, alokacin saidai bakuwar noba ce yagani
Kamar ya aje saidai kuma wata zuciya tace mai,
Amsa kawai kaji kowaye a wanan lokacin da duk wani mahaluki ke bukatar hutu,
Cikin yar siririyar muryan ta tayi mashi sallama,
Saibkuma tai shiru wayar yadan daga yagani ko ankashe ne ,,,
Amma sai yaji muryan muryan nacewa dazu kun dawo lafiya,
Nagode kwarai Allah ya saka da alheri Allah ya bar zumunci, sosai
Dama anty ce tace in bugo ma in maka godiya abin da kayi muna dazu din,
Murmushin da maganar ta yasa shiyi yasa tace nagode sai anjima,
Sai kawai ta kashe wayar nata batare da jiran taji ko da abinda zai ce,
Wayan nashi yakara dagawa sai ya wurgata saman gado yaci faba da taje gashin shi da yakeyi,
Sai mamakin zancen yarinyar yake yi nacewa anty ce tace taimai godiya,
Wata ajiyar zuciya ta sauke gami da fesar da wata iska irin ta relief din nan,
Bakin katifan da mahaifiyar ta take kwance ta zauna sai wani bala,in tausanyi ta yakama ta,
A hankali takai hannun ta asaman wuyar mahaifiyar nata sai taji da zafi, har yanzu,
Shin kodai malaria ne ya kama ta haka, ba wani kula, balle a yi treating,
Gawani ruwan kwata kusa da kofar dakunan su daje fitowa daga wani lungun gidan,
A zuciyar maryam tace gaskiya insha Allah gobe zan gwada gyara wanan gurin mugani ko zai rage aje ruwa haka,
Tana kojarin kwanciya sai taji wayar ta na kara, mamakin may kiranta a wanan lokacin tayi,
Don azaton ta ko A,A masugan ta ne yakira ta, nobar Safiyace
Zagi tafara jefa mata da iskanci yanzun ne lokacin kiran mutum,
Darita safiyan tayi tace ke dan Allah niki saurara koda yake ma nasan kin sani kawai dai zan fada maki ne dan karkice ban fada maki da baki na ba,
Gobe Jibrin yace zasu zo su gana da mahaifina, kafin ya koma
Wani irin dadi maryam taji, taitawa safiya din ba,a dakuma fatan alheri
Safiya tace amma dai zaki shigo gobe din ko,maryam,?
Maryam tace bani ma cikin gari safiya ina nan gurin mamana bata da lafiya,
Safiya tace cikin mamaki maryam mama bata da lafiya shine baki fada min ba,
A haka dai suka yi sallama bayan sun dan taba hira,a tsakani,
Tana aje wayar sai zancen A, A yafado mata wanda tun jiya takirashi taje sheda mai abin da baba yaxo ya fada masu gamay da maman ta,
Sauguda yakirata da safe yana tambayar ta koza ta dawo yau ne ,
Azaton ta ko zai ce zai tafine saitaji yace idan bazata dawo ba sai ya sani don kada yazo ace bata nan,
Tsuki tayi wanda har sai da mahaifiyar ta cikin dakusasshen muryan ta irin na marasa lafiya tace,
Baki ji dadin kwanci saman tabar ma ko yar baba,?
Sai alokacin matasan cewa idon ta biyu zafin ciwo ne kawai yasa ta yin shiru da lafewa,
Maryam tace mata aa mama mantuwa ne dai kawai nayi,
Daga haka har dan barci yadan kwashe ta tana maicike da jin haushin A,A wanda tarasa ko wace irin soyayya ce yake gwada mata,,,,,


Washe gari duk zancen boyar Allah da yagani acikin wahala ya cika mai zuciyar shi sosai, don da zancen ta ya kwana,
Sai karfe hudu na marance zasu tafi ganin iyayyen safiya,
Don haka, ya yanke shawaran cewa gara ya koma ya taimakawa matar yasa suzo asibiti adibata,
Maryam tana tsakar gidan saye da wani tsohon zanin mahaifiyar tasai aikin gyaran kwatan sukeyi tunda sanyin safiyar nan
Wani yaro yashigo yake cewa kishiyar mama wai wani mai mota yanawa, baba sallama a waje,
Kafin tabada amsa sai gashi yafito yana cewa guri nako aka aiko ka mai motafa kace,
Fitar shi ba,afi minti gomaba saiga su tare da Yusuf sun shigo,
Yana saye da wata bakar rigar sanyi a jikin mai kama da leda bayan shi, yasa wandon Jean's,
Mamaki ko rudewa yasa maryam tai saurin sake tsintsiyar dake hannun ta,
Tana kallon shi cikin mamaki,
Muyan mijin mamane ke kiran ta daga inda take tana wanke kafar ta,
Cikin sauri da ladabi ta isa dakin kara gaida Yusuf din tayi tana mai tambayar lafiyan su antyn ta,
Mijin mama yace maryama, asibiti za,akai mahaifiyar ki yanzu,
Don haka sai ki yi kokari kishiryata kada mu makara ko,?
Da mamaki ta waiga inda yake zaune kamar jiya, don har yau kujerar tana gurin,
Wani yaro ya shigo dauke da wani ckofin silver mai marfi,da kosai acikin leda yace wai ance ga kunin ki, inji mamana,
Karba tayi tace kace angode,ko kaji,
Cup din kunun ta aje agaban Yusuf tace ga kunu da kosai,
Sai ko taga ya aje wayan shi ya jawo kofin , sosai yasha kunun, yaraga mata saura,
Yana gamawa yatashi zuwa waje, don ya jirasu su shir ya,


ZEEE. MAKAWA
[3/7, 1:15 PM] ‪+234 803 381 3188‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
4⃣4⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA,

A dadafe aka tallabo mama zuwa bakin mota,inda za a sata su tafi,
Cikin sauri Yusuf, ya bude kofar motocin da taimakon shi aka tallabata akasa ta, acikin motar sai maida numfashi takeyi guda guda,
Duk yadda, zaka zata matar na jin jiki fiye da hakan saboda duk ta zube,
Maryam da ke tsaye gefe rike da wani leda da suka dauko ta dan kwantar da kai zabban tausayi,
Saida yaga cewa an zaunar da ita, a hankali cikin motar sannan ya dan dago kai ya kalle ta,
Fusksnta duk ya canza yana yi saita baka tausayi
Kwana guda a kauye duk ta jemay tayi wani irin fau, da ita,
Badake za,a tafi bane don bamu san ya abin zai kasance ba a can,
Tajuyo ta dan kalle shi alamar kamar zatai kuka, alokacin,
Cikin rawar murya tace, bari su tafi zan shigo motar haya yanzu in samay ku,
A raunane yace no, bari dai abawa namiji kudin mota ya samay ko,.
Don mata biyu da maza har uku ne suka matsa suka shige a wanan dirkekiyar Jeep din,
Wacce tunda aka saye ta bata taba daukar loadi irin haka ba sai yau,
Da sauri karamin yace shipa gaskiya ba zai sauka ba don dai dashi za,a tafi,
Karamin ne yace ba matsala barin sauka, maryam da duk wanda ke cikin motar basu so hakan ba,
Saboda Awalu yana da kokari sosai don kusan komai shike zuwa nemowa ,
Ya na sauko Yusuf ya ciro kudi dubu biyar cur yace ka shigo mota kasamay mu a asibitin tagwai pls,
Ai ba kunya kuma sai Isah yayan shi da yace ba zai sauka ba,
Yai caraf yace a,a shima motar kasuwa zai shiga ya fasa bin su,
Wata mata tace amma dai kaikan ,Isah anyi mutumin kawai,
Baka ji kunya ba, yace kedai kikaji dan nace kawai na fasa nima,
Dariya suka sa alokaci guda duk wanda ke gurin, shiko isah ko a jikin shi,
Shima dubu biyar aka bashi kudin motar kamar yadda akaba Awalu,
Hakan yasa su samun fili su wala yadda suke so batare da sun matse ba,
Baya maryam ta zauna tare da sauran matan dake baya,
Yusuf ya tada motar shi inda suka fara tafiya sauran mutane na ta masu fatan adawi lafiya,
A,hankali yake tuka motar cikin gwanin ta da kwarewa,
Babata wani lokaci suka isa, cikin gari direct asibitin suka nufa,
Sai da yafara fita yaga likita ba bata lokaci saiga wasu nurse da keken daukar mutane suka kama mama suka wuce ciki da ita,
Suna shiga Maryam bata tsaya ba saboda duk a rude take a lokacin,
Mashin ta hau sai unguwar su ganin ta kawai anty tayi, a lokacin,
Da mamaki anty ke kallon ta saidai kafin tai magana tagane cewa maryam a cikin tashin hankali take,
Dan natsuwa ta tattaro guri guda sanan tafara bawa anty bayanin zuwan su da kuma yadda suka kwana da maman jiya,
Ita ma Anty Dije nan da nan ta rude ta hau shiru don su tafi,
Saida suka fara zuwa gurin baba suka sheda mai tukun ,
Sannan suka wuce zuwa asibitin, ba tare da bata lokaci ba,
Sun samu an daura mata ruwa, ana mata kari,
Amma tana barci a lokacin don haka suka dan fito daga waje don gudun kar su ta da ita daga barci,
Ganin yadda suke a tsa,tsaye tasa anty Dije shawaran zuwa gida don dauko masu, tabarma da dan sauran abin bukata,
Tare suka fito ita da maryam a lokacin tanawa maryam fada cewa ta kwantar da hankalin ta dibi yadda ta koma jiya zuwa yau,
Motar Jibrin ce agaba sai ta Yusuf din, nabin shi a baya,
Ganin su yasa Anty Dije tsayawa don su gaisa taimai godiya,
Both suka ga an bude tabarmi ne har da su filo sabbi yasayo masu sai kuma dangin kayan abin ci da sha,,
Baki bude Anty Dije ke kallon shi cikin mamaki da abin da idon ta yaganar mata,
Fa murmushi ya karaso gurin dauke da kaya a hannun shi wanda karasowar tashi tai daidai isar maryam kusa tana mai mika hannuwar ta takarba,
Maryam tana barin gurin Anty Dije tace Yusuf waban irin dawainiyar haka, ?
Saida yadan goge hannuwar shi da kyale, tukun sanan ya na murmushi yace,
Anty wanan ne kawai irin damar da mutun ke samu ya taimakawa mabukaci, wallahi,
Idan ba anan nazo naga mutane acikin yanayi ba a ina zan gansu a can tunda ba shiga cikin mutane mukeyi irin haka ba,
Tausayi so,sai, maganar shi taba Anty Dije wace sai faman kada kai tajeyi don gamsuwa da zancen shi,
Tace to amma dai ai zaka fada min kaga sai in dauko nawa agida ko, basai kasawo ba,
Yadaga hannun shi guda guda na acikin aljihun shi yacewa anty dije,
Haba dai No, no no, ai ya zama wahala hakan kawai a siyu yafi sauki,
Ajiyan zuciya kawai ta samu yi tana mamakin halin rayuwa irin na wanan bawan Allah,
Maryam ce ta karaso gurin tana rungumay da hannayen ta saidai fuskanta acikin damuwa yake,
Alokacin Yusuf kecewa Anty Dije likita yace malaria ne ke damun ta so,sai shine sukuma wai sun cire mata hakin wuya,
Ido daga anty har maryam suka fitar don mamaki jin maganar,
Yadan kara gyara tsauwar shi ya na fuskantar su duk su biyun yace,
Wallahi Anty mutanen mu na kauye suna kashe kan su da bata,
Shiyasa bature ke cewa African people killed themselves by risks, before there, time,
Kawai sun tashi kashe tane da lokacal treatment fa,
Tun jiya dana ganeta hankalina bai kwanta ba,sam, wallahi,
Yakare zancen yana dan siririyar, dariya ba mai tsawo ba,
Kai, kai kauye dai gaskiya akwai jahilci sosai wallahi,
Maryam tace cikin siriyar murya,
Yanzu mai likita yace akai ?
Dan kallon gefen da take ya yi sai yaji duk yarinyar takara bashi tausayi,
Saboda duk yadda mahaifiyar ka take kana son abin ka,
Yace nop likita da wai zai bamu magani akoma ai treating din ta a gida,
Sai nace mai a,a yabarta kawai a nan mugani ko zata dan kara covering, zuwa gobe sai mu koma
Ya kalli inda anty dije take tana gyara goyon Abubakar yace ina ga haka zai fi da ace su,koma gida a haka,
O, O YUSUF mun gode kwarai wallahi Allah dai ya saka ma da alherin sa
Haba, haba anty ki bari dan Allah wanan ai ba komai bane dai,
Maryam ce ta hango mijin maman ta zai je bidan ruwa ya kewaya, wa,
Da sauri maryam tanufi gurin inda taga ya dauki wani tsohon buta, takarba taje samo mai ruwan,
Ido, suka bita dashi gaba dayan su yarinyar tana basu tausayi duk da tana kokarin danne damuwar ta,

Shi ya maida Anty Dije gida don taje, ta yi girki, kafin yara,su dawo saboda bakowa gida,
A hanyar shi ta dawowa ne ya ratse ya sai masu ruwan GOJE WATER, mai yawa da sabuwar buta, Da nama gassasa mai yawa tare da drinks, sai su fruit kala,kala,
Maryam wace ke zaune saman steps din da zaka hau ka shiga cikin asibitin,
Tadan yi tagumi da hannu ta biyu ba,abin da takeyi sai tunanen halin da mahaifiyar ta take ciki,
Ga talauci ga wahala, ga kuma ciwo yazo ya shigeta haka lokaci guda,
Badon Allah ya gyara ba da kilama surasata, ta wanan ciwon
Maryam bata ga lokacin da ya iso ba don tati nisa a tunanen da takeyi,
Saidai ganin mutum da tayi a gaban ta wanan karon yati wanka ya cire kanan kayan da yasa a jikin shi,
Sannu da dawo wa ta ce mai cikin , karamar murya mai nuna damuwa,
Ledar dake dauke a hannunshi ta mike tana kokarin karba daidai lokacin da mijin mama ya fito daga cikin asibiti hannun shi dauke da tasbaha,
Ko bata bude ba kamshin da ya daki hanncin ta ya sanar mata cewa gassan nama na cikin ledar,
Gurin da masu jiya suke zaune ta nufa da ledar, duk sukayo mata caaaa da ido
Don suga komay aka dauko a cikin ledojin da ya shigo da su,
Tunda tafara budewa sai da gaban ta ya fadi don ganin yawan abubuwan da yakawo masu,
Shim shi wani irin mutum ne wanda baida jin zafin kashe ma wani kudi,
Sun dade cikin dakin da aka kwantar da mama tare da likita da mijin maman,
Dole haka tasa kai ta shiga don ta kai mata fruit din da nama kozata ci,
Mijin mama ne yake cewa maryama cikin tausayawa, ina ganin fa yau duk baki ci komai ba, fa,
Murmushin yake tadan yi tace na karya a gida ai kafin mu fito da,safe,
Zai kara magana sai wayar ta dake a cikin yar jakar ta tai kara,
A,A dun tane yakira duk da akwai mutane a dakin amma sai tadan daure tace hlo, daga haka tai hanyar fita waje,
Ba gaisuwa ko wani abu sai cewa yayi a gadaran ce ya mai jikin,
Da sauki tace mai a hankali, gamu nan asibitin tagwai, da ita,
Tun yaushe kuke nan ya tambaya cikin dan nuna concern din shi,
Tace mai yau da safe ne aka kawo ta saboda jikin nata ya kiya,
Ok to zan shigo idan na rarage abinda nakeyi, Allah ya sauwaka daga haka ya kashe wayar shi kawai,
Sam ta mantacewa a kusa da kofar dakin ta tsaya tana kashe wayan tadago kai sai caraf idon ta akan na Yusuf wanda ke kokarin,bude wani ledan magani, don aba mama,
Jibrin ma wanan karon a cikin shiga ta mutunci shima ya shigo dakin yana mai gaida mama,
Muryan Yusuf ne ke sallamar su yana cewa zasu dan je wani guri su dawo,
Maganar Safiya ce ya fado mata arai azuciyar ta tace lalaima can zasu tafi ke nan gurin ganawa da mahaifan safiya din,

Sai kusan bayan la,asar sosai A,A yazo asibiti cikin shigar shirt sky colour, da wando baki sai tie da yasa a wuyan shi kawai,
Maganar shi a gadarance yake yin shi yana mai nuna cewa shi din wani ne,
Tambayar mujin mama takeyi yasukabar har ciwo ya ci ta haka gasu ba wani nisa suke dashi ba da gari,
Yace ai yanzu ba,a wasa da ciwo komai kan,kantar shi,
Sai mijin mama yace to ko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login