Showing 147001 words to 150000 words out of 255288 words
Chapter 50 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete
dasune a ciki,
Sai suka samu gefe guda saman fararen roba dake karkashin wani runfa suka zauna,
A daidao inda suke zaune akwai mata gun,gun a zazaune saman fararen kujerun roba,
Wa su, kujeru da wasu matasan mata suke zaune akai su uku sai kallon inda su maryam suke suna kus,kus,
Sai leken su maryam akeyi, tun farko maryam ta halkanta da su amma sai ta shere su don gudun zargi,
Amma kawai sai daya daga cikin matan ta tasao har inda suke, zaunr tace, wai kamar Ejoma wanan ko ?
Safiya ce tai carf tace Naimat dai ko, ?
Matar tana murmushi tace gaskiya kamar su yai yawa sosai ,
Naimat tace nice da sauri ta waiga gurin da yan uwan ta suke zaune tace,
Itace bana fada maku ita bace, ashe kin musulunta ne,
Safiya tace haba tunda har kin ga zahiri may ye na tambaya pls,
Ke ko yar uwa don ance mata tubabba shine wani abu,
Haba amma hakan ya zama tozarci ko tunda har mutun ya riga ya zama musulumi,
Sai gudan tace to am a ai don an tuba ba a taba cewa batai zama kafira ba ada,
Innalillahi, maryam tace cikkn nuna bacin rai ga matan,
Haba dai Anty Rukkaiya ai wanan bai dace ba ga addini ko ?
Safiya tace ga wanda yasan addini ke nan maryam
Wai mutane sai su manta da cewa da wanda yai shekara dubu da wanda ya shigo yau fuk guda suke ga Allah,
Har ma wanda ya shigo yau idan ya rike addini saima ya fika don shi baida zubi tukun yana tare da gafaran ubangijin shi,
Haka abin yaso yazama kamar fada a,tsakanin su don Safiya ta dauki zancen da zafi,
Su basu ko farga cewa Naimat ma bata gurin ba tunda taga irin yadda abin ya zama tozarci ta sulale ta fita kofar gida,
Sai da wasu manyan su suke tambaya wai akan wace,ce ake zancen
Safiya taje ta nuna Naimat taga babu kowa aguri ,
Da mamaki take kallo. Maryam tana tamba yar ta cewa ina Naimat din take,
Mikewa su kayi a,lokacin da ake cewa matan basu da gaskiya
Su daina yiwa mutun tozarci irin haka saboda hakan yazama cin fuska,,
Naimat wace ta koma can kofar shigowa gidan tai zaune cikin bacin rai,
Shigowar Anty Dije ce yasa tadan yi kamar ta sake, fuska,
Tambayar ta Anty ke yi ko may yasa ta fito waje, ina kuma su Maryam da Safiya,
A wanan lokacin suma suka i,so gurin suna neman ta ta,
Ko ba,a fada ma mutum ba yasan cewa a cikin bacin rai take kawai,
Safiya ce tai kokarin yiwa Anty bayani kamar yadda akayi da matan
Cikin bacin rai anty ke cewa su tsaya ta samu wanda zai maida su gida,
Sai yanzu take, da ta sani tabar su agida kamar yadda su ka bukata tun farko,
Cewa su bazasu zo ba za su zauna gida kawai har ta dawo ita da yara amma sai tace tun da buki yaune kawai su tafi tare kawai, yafi, shine har maryam ta gai,yato safiya don su tafi tare,
Zaune yake jikin shi duk kamar ba nashi ba Naimat tana ta labarta mai abinda ya faru,
Sai hawaye take ta zubar wa tana ta kokarin share hawayen da ya zubo mata a fuska da gyalen da ta yafa ajikin ta,
Maryam tana tsaye gefe guda tabi lafiyan bango tana sauraren yadda yake bata hakkuri,
Wani irin tausayin su take jin ya kama ta a lokaci
Batasan cewa hawaye na biyo mata fuska ba har sai da taji mutum tsaye gab da ita
Ta yadda bazata iya ko da motsawa ba handky ya mika ma ta batare dayi mata magana ba,
Girgiza kai tayi alamar aa ya barshi kawai yana kallo tasa habar hannun ta ta goge hawayen
Ko karin wucewa take yi zuwa ciki a lokacin batare da tace mai uffan ba,
Sai dai babu hanyar da zata bi ta wuce ko ka dan ga kamshin shi da ya cika mata hanci kamar kamfanin turaren,
May ki,ke,wa kuka maryam kifada min dan Allah
ZEEE SEENABU MAKAWA
[3/28, 9:00 AM] 0mmer Farouk: πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
FUREN JUJI
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
6β£1β£
ZAINAB IDRIS MAKAWA
IYAKA, NA,ABBUD WA,IYAKA NASTA,IN,,ππππππππ
Tsaye yake a tsakiyan falon gidan shi daga shi sai singlet da wandon shi dogo dake jikin tun da rana,
Safa da marwa yake yi a,cikin falon, a inda ya goya hannayen shi a bayan shi,
Komawa yayi yadan jingina bayan shi da bango kadan,
Yadan daga kafar shi guda ya dage a bayan bangon,
Da sauri ansar da tunanen shi ya bashi akai yai sauri girgiza kai tankar da wani yake magana alokacin,
Ina sam ba gaskiya bane sam sam yariyar da bata ko kai Ruth shekaru ba,
Ina sam wanan zancen banza ne may zan so gurun maryam,
Ko shi saurayin nata ai kawai rigimar tane ya kai ta amma ai da,sauran ta, kawai dai don tayi saurin fara karatu ne kamar yadda yaran hausawa ke saurin shiga makaranta,
Tsuki mai tsawo yaja batare da ci gaba da tunanen ba ya juya zuwa bedroom din shi,
Hakan ya fada saman gadon shi batare da tsayawa sauya kaya jikin shi ba
Sai cikin dare daidai lokacin da ya,saba tashi don yin kiyamallaini ya mike zuwa bathroom,
A gurin da yai sallah asuba yana lazumi nan barci ya kara daukan shi mai tsawo,
Wani mafarki ne yadan dauke shi zuwa duniyar mafarkai,
Tafe yake yana rike da hannun wata, mace wace, ke dauke da tsohon ciki a jikin ta
Tafiya matar keyi da kyat tana faman ciji baki don wahala,
Iya tausayi matar ta bashi hakan ne yasa shi zuwa ya dan taimaka mata,,
Dukawa tayi don wani irin azaban zafi da ya ziyarce ta, da sauri ta fisge hannun ta gare shi,
Ta dan kai wani lokaci agurin duke tana fama da murdan ciki,
Sannan matar ta dago fuskan ta da yaga ni shi yasa shi ja da baya cikin wani irin mamaki
Sai kokarin nunata da yatsa yake saboda bai san cewa itaba ce ke wanan wahalar,
Juyawa yayi daga inda yake a kwance,, daga haka sai yabar wancan mafarkin na farko,
Wani mafarkin kuma shiga yi inda yake tsaye yana tura wata yar matashiyar budurwa a saman wani lilo
A,hankali yake tura ta inda kanta yake duke, sannu a hankali ta dago kai zuwa saman kirkin shi ta kwantar da kai
Sun dauki tsowon lokaci a haka da ita sai dai sam baya iya ganin fuskan ta,
Ya kai wani lokaci agurin yana kwance a kasa saman carpet yana barci,
Zuwa yanzu tun bayan musuluntar shi yasaba da irin wanan kwanciyar a saman abin sallah shi idan ka gan shi ya dunkule guri guda zaka,zaci cewa ba shi bane,
Γ yadda zaka ganshi matashi dan kwalisa mai i,limin zamani kuma ga naira ta zauna zaka zaci cewa ba zaiyi jimirin jurewa yin ibada ba
Badon komai ba kuma sai,don za,a iya cewa haye yayiwa addinin a sama ,
Ba zai iya rike ta da kyau kamar yadda yakeyi a yanzu ba,
Karan wayan shi ce ta tashe shi daga barcin da ya samu mai dadi barcin safe ke nan,
Idon shi a rufe saboda dadin barcin ya mika hannu dai,dai inda karar wayan nashi yake fitowa, ya dauko ta cikin kasala,
Antonia ya gani rubuce, zubur ya mike don kiran da yagani daga NANI ANTONIA,
Hlo, how you na dey,
Batare da ta ansa mai ba,take cewa Oga Pipkin dey sick since yesterday,
E no even go to school woo,
Mikewa yayi zubur yace subbahanallah, gami da furta sunan dan yaron,
Abdulraham a fili, tare da kokarin mikewa tsaye, daga gurin da yake kwancen,,
Hlo,
Antonia yace cikin harshen turancin yan kudu,
Ki shirya, shi kun ji zan kira doctor yazo ya diba min shi yanzun nan pls,
Yana kashewa ya shiga neman nobar doctor chukuma,,
Doctor chukuma wani likitan yarane da yake yawan kai yaron gurin shi tun bayan dawowar su Abuja,
Ba wani bata lokaci ya kira doctor din ,wanda a kira na farko ya, samu nobar doctor din a gurguje yai mai bayani cewa ya je gidan shi ya diba mai boy bai,da lafiya,,
Wanka yafada saboda ya samu ya isa Abuja da wuri ranan
Sai alokacin yake mamakin irin wanan gwaunatin ta Nigeria,
Ace babban gari mai tsohon tarihi kamar garin kwantagora ,
Wacce ta tara din,bin al,umma iri,iri wai har yanzu ba ai mata wani abin cigaban al,umma kasar ba,
Ya kamata ace yadda take business center tana da hanyoyin masu sauki daga railway ,zuwa airport, da sauran su,
Amma saboda handama manyan kasar mu da basu da kishin zuci har yanzu an rasa wanda zai yiwa wanan kasar irin wanan aikin cigaban, na al,umma,
A cikin barci da sukeyi na safe mai dadi da shiga rai suke jin muryan Yusuf din sama, sama,
A hankali ta bude idon ta a dai,dai lokacin da takejin yana cewa anty yanzu zan tafi Abuja don an bugo min waya yau da safe cewa, Pipkin bai da lafiya,,
Kuma yaron bawai ya wani saba da sabuwar nani din shi ba,ne,
Don kusan zuwan Naimat, nan ne na dauko matar daga kauyen mu,daga haka sai,
A hankali kuma taji dan she,shekar kukan Naimat a bayan ta,
Cikin idon barci maryam ke kallon Naimat din inda a hankali tadan mike zaune,
Inda Naimat take zaune take kallon ta, wacce ke kokarin goge hawayen dake sin,tiri a idon ta,
Ganin maryam din ta farka,ne yasa ta juyowa inda take zaune suna fuskantar junan su,
Hannun maryam tariki a cikin kuka ta nace wa maryam din,
Maryam ina son yaron nan, bana son ya mutu wallahi,
Saboda na,sha wahala sosai akan shi zaman da, da ,ni akwai wasu muhinman abubuwa da nake tunawa, akai,
Maryam wace ido kwai ta kura mata a cikkin mamaki, take kallon, Naimat din don sam bata fahinci inda maganar ta ya dosa ba,
Sai kuma hankalin ta ya,koma falo su, inda taji Anty Dije na cewa bazan bari kabi hanya baka karya ba Yusuf kabari ko cooker,oth ne a, dan dama ma,ka
Daga Saman gadon tai ko,karin saukowa a lokacin kafin ta idda sauka taji muryan Anty cikin daga murya tana kiran ta,
Sam ta mance cewa kayan barci ne ajikin ta don haka ta nufo falon da sauri,
Riga da wandon kayan barci sabon kitson da akai mata na wevin "yan ritsi,ritsi, sunyi lub, lub a kanta , gwanin sha,awa,
Da sauri ta iso inda anty ke tsaye dauke da yaron ta,
Shi ko sarkin lakewa a jikin uwar shi, a hannnu, ta yake dauke yana son shan nono, yanzu
Itama Anty sai yanzu tasan cewa kiran da tai,ta kwadawa Maryam din yasa ta rudewa cikin barci ta fito a haka,
Zanin da ta jawo don ta dan daura a sama take kokarin daurawa akai tana fadin gani Anty,
Da sauri ya kara waro idon shi waje don sak kalan kayan da yaga mai cikin da yai mafarki ne dasu da asuba,
Don Allah hada heater ki dama wa Yusuf cookeroth da,sauri pls, inji Anty Dije,
Sai a lokacin maryam wace tagama daura zani saman kayan barci ta, ta kai kallon ta inda yake tsaye tace ,
Ina kwana a hankali,
Shima dai ansa mata yayi cikin rashin walwala da sauri maryam ta nufi hanyar zuwa kitchen, din
Wani irin mugun bugun zuciya yaji mafarkin ne ya fado mai a ran shi,
Kafin yan mintina har ta hado mai cikin wani bowl mai dan fadi tazubo mai saboda yai saurin shan iska,
Anty Dije ce tace dan juya mai ya sha iska don Allah kada ya makara,,
Fuskan shi a hade kamar wanda bai taba dariya ba a rayuwan shi,
Wai waye Pipkin din nan ta ke tambaya a cikin zuciyar ta,
Dukawa tayi daniyar tafara motsawa mai orth din,
Wani kamshi ya daki hancin shi wanda saida yadan kara kallon ta ta wutsiyar ido,
Mamaki yaji don yasan daga barci ta tashi tafito amma kuma take wanan kamshin haka ?
Kai wanan yariyar akwai tsabta da yawa idon shi ne ke kallon yadda har an gyara ko ina na gidan ko kamar ba,a bata ba,
Muryan maryan ce mai magana cikin sanyi take cewa
Ya Yusuf addu,an samun lafiya za ai mai kasan ciwo bautan Allah ne both babba da yaro,
Amma duk da haka akwai wasu magani da mukewa yara amfani da su sai ka tafi mai dasu adinga mai amfani dashi a gani,
Mikewa tayi don ganin kunun yai dan sanyi saboda tasan cewa baya shan abu mai sanyi shi,
Dakin Anty ta shiga sai gata tafito da kwalaben magani a hannun ta,
Kara durkusawa tayi gaban shi tana mai bayani guda guda yana dan kurba kunun dake a hannun shi vikin cup a hankali,
Idon shine suka sauka a gaban rigar barcin ta waiyazu ;billah
Da sauri yakau da kan shi gefe har takare mai bayanin cewa wanan man
Habbatussauda ce, wanan, Zaitun ne, sai kuma man Albasa a dinga hadawa da pure zuma,
Takare maganar nata da ce wa a hankali Allah ya bashi lafiya,
Ameen ya ce cikin jin dadi da irin nuna kulawar da tai mai,
Sai alokacin ta juya gurin da Anty Dije take zaune tana shayar da danta tace
Anty idan zan fita atuna min in sayo wasu a aje dan Allah,
Mamaki yaji cewa sayen maganin ma sukayi ashe,
Bai wani dauki lokaci ba ya mike yana kokarin gyara jikin shi inda yadan takure,
Naimat ce tafito, cikin damuwa duk da tayi na mijin kokari gurin saita kan ta saboda kada agane cewa tayi kuka,
Maryam wace ke tambayar Naimat a cikin kashe murya,
Pipkin din yaron waye shi ?
Murmushi kawai Naimat tai mata, batare da taba ta ansa ba,
Γnty Dije ce tace ke baki san yaron Naimat ba Abdulrahaman,
Wani irin kallon mamaki maryam kewa Naimat daga haka Yusuf yai masu sallama ya tafi,
Yusuf tuki yakeyi shi kadai a cikin mota sai sharara gudu ya ke yi,
A cikin nishadi yake tukin shi hankali kwance sai dai kuma zuciyar shi tana gurin da yake, tunane
Sai,dai a kai, akai, yana dan duba agogon hannun shi, sai kuma ya daga kai yadubi, hanya,
A gaskiya a yadda ya samu yaron yana jin jiki sosai,
Saboda duk da ya samu yana barci amma jikin shi gadau yake da zafi,
A hankali ya duka a gaban yaron yana mai dan taba mai jiki a hankali,,
Wayar shi ce tai kara alamar kira ya shigo mai, a lokacin,
Batare da ya mike ba daga inda yake yadauki wayan
MARYAM BLACK yagani a rubuce wani irin murmushi ne yadan subuce mai,
Assalamu Alaikum, tace cikin yar siririyar muryan ta,
Ansa mata yayi da wa,alaikissalam ,
Maryam na barku lafiya,
Ya Yusuf ya hanya ka kusa isa ko,
Ina gida Maryam,
Yana jin ta tana cewa yai har ya isa fa,?
Muryan anty yaji tana cewa Yusuf wallahi ka rage wanan yawan gudun naka fa,
Maryam ya ambaci sunan ta, cikin wani irin murya,
Naam ta ansa mai itama cikin rudewa da jin irin kiran da yai mata,
Ya maijikin tace mai cikin sanyin murya,
Nasamu yana barci, amma dai jikin shi da zafi sosai wallahi,
Ya Yusuf kasamu kyale ko towel, kasa a ruwa ka din ga tai maka mai, dashi kana dan goge mai jiki dashi,
Jikin zai mai sauki idan an gama saika bashi wanan man albasan da sauran su ya sha,
Sai kuma tai shiru bata kara cewa komai ba daga hakan jun shirun nasu yai yawa shiyasa yakatse da,cewa abashi Anty,
Zaune yake a bakin gadon da ruwa da wani farin towel,
A hankali ya ke matse ruwan da towel din ya kwaso,
Yana dan mannawa a jikin yaron dake kwance a saman gadon shi,
Nani Antonia ta na tsaye gefe guda ta dan rakube a bango tana kallon abin da yadace ace itace tayi amma sam rudewa ya hana ta yi tun farko, don da ace tayi da jikin yaron bai kai haka ba,
Sannu a hankalo ya bude idon shi ,ba su sauka ko ina ba sai a,saman fuskan Uncle din shi,
A hankali ya ce uncle, sai kuma yai dan murmushi,
Wani irin tausayin yaron nen ya kama shi yaro mai kyau ga wayo amma ace wai ya tashi babu uba,
Kai mutane ba su da tsoron Allah sam, ka haifi yaro sai kuma kaki shi,
Yanzu badon Allah ya nufi yaron da,zama gurin shi ba da