Showing 33001 words to 36000 words out of 255288 words
Chapter 12 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete
Maganar shi yasa maryam gane cewa yana cikin motar wace tun shigowar ta motar kanta na gefen glass tana mai kallon waje,
Dammmm sautin da kirjin ta yabayar ke,nan a lokacin da taji muryan shi a motar yana cewa,idan ka sauke su mu wuce uguwar JANKIDI pls, zanje inga Abdulsamad,,,
A hankali kwance yake maganar batare da ya kalli cikin motar ba gefen KB din,
A,kofar gidan su Maryam, din suka para tsayawa don su sauke ta,
Daidai lokacin Assalam yadan fito ta wajen gidà yà na kallon motocin a ke wuce wa
Kokari takeyi ta balle murfin motar daidai lokacin da Joseph din ya dan dan,na gurin da duk security din motar suke,
A lokacin kuma Maryam ke fadi cikin siririyar murya,
Nagode, ta furta a hankali ta yadda ba wai lalai ne wani yaj abinda tace ba,
Hannu kawai shima yadan dago mata alamar ba matsala,
Da gudu Assalam yazo ya rungumay mata yana oyoyo little mummy, dan jakar hannun ta yake kokarin karba daga hannun ta,
Sai a lokacin yai arba da Joseph wanda ke a gaban mota zaune,
Sake jakar yayi ya sheka da gudu gurin motar yana washe bakin ganin Joseph din,
Juyawa maryam tayi abinta batare da da tasaya koda kallon su ba
UNGUWAR JANKIDI, wani unguwane acikin kwantagora, inda wane abokin sanar mahaifin Joseph yake zaune,
Emeka ake ce mai ,,,kusan tare sukazo neman kudi agarin, tun suna matasa,
Saidai Allah da ikon shi , cikin wani watan Azumi, sai kawai aka wayi gari wurin wani tafsirin marance da ake yi, Emeka ya kawai sai ga Emeka yace yazo ya musulunta ne,
A ranan yakarbi musulunci a hannun babban malamin dake wa maza tafsir, a kusa da gidan sarki,
Ranan duk wani IBO da ma sauran Christies hankalin su ya tashi sani cewa kowaye Emeka da sukayi,
Duk wani hanya dazasubi don suga cewa sufitar dashi a cikin musulunci abin ya faskara garesu,
Har kudi suka hada mai uban yawa suka kaimai wai yadawo cikin su amma sam yaki karba,
Daga baya da sukaga yaki sai suka fara shawaran yadda zasu cuta mai har ya karaya, yadawo masu,
Wuta suka fara sama shagon shi a tsohuwar kasuwa inda shagon ya kone kurmus,
Da sukaga baizo wurin su ba sai kuma wani dare suka turo har gida aka sace duk dan abinda yasaura a hannun shi suka gudu,
Yan kwamitin su sukazo mzi da makuddan kudi suna mashi tayi akan yadawo cikin su,
Amma san Abdullsamad yaki dawowa, yace shi ya shiga kenan,
Maimako yan uwa musullumai su tausaya mai su mai tallafi ko wani gudun mawa sai kawai aka shere shi nan,
Ganin wahala yai yawa yasa matar shi gudu tabar shi ta koma kasar su, inda takoma ma Christian din ta,
Tabarshi nan tare da yaran shi ma,za uku, suna ta buga,buga,
Yanzu har takai ko suturan sawa baida shi dan gidan shi rabi ya zube baida kufin gyara saifai kawai Allah ne ke rufa masu asiri su samu abinci,
A haka ya auri wata musulma ma sanar saida shinkafa a bakin kasuwa,
Yakan je gurin Mr Ema jefi,jefi in abin yadaure mai da yawa,
Saidai duk sanda yatafi zai dawo da tarin bakin ciki a zuciyar saboda irin yadda Mr Ema kan ta sake mai maganganu,kuma duk kyautar, da zai mai bawanda zai amfana dashi bane, daga dari biyar tsanani dubu biyu,
Rigar shi duk ta yage yage a baya, hakana yake sawa yakoma kamar mahaukaci,
( Allahu Akbar munada wanan raunin wallahi musullumai bamu tallafawa wa yanda suka tuba yanzu,,,,,,,)
Mama manja ce ta fadawa Joseph cewa yana bukatar taimako sosai saboda sani da tai ma iyayensu tare a da,can,,,
Yai mamakin jin cewa har yanzu Emeka Abdullsamad yana agari batare da yasani ba,
A hankali suke gangaro da motar su zuwa cikin unguwar wanda akasari duk tsofafin gina ne a gurin,
Zaune suka hango shi saman wani tsohon icce dake kofar gidan shi ,
Cikin wata tsohuwar rigar atamfa duk ta kode ga farin gashi duk ya dan cika mai fuska,
Yana zaune kai dagani kasan cewa yana cikin halin hau ula,i,,,
Har suka faka motar su baidago kai ya kalle su ba,
Saicewa yakeyi a fili Subbahanallahi, Walhadullahi Allahu,Akbar,,
Sallama KB yamai daga inda suke nufo shi ya karba masu tare da daga hannu har saida yakai aya, tukun,
Sam bai gane Joseph ba a lokacin saidaga baya bayan ya mika masu hannu sun gaisa, duk da kallon mamakin da yake masu namay yakawo su gurin shi,
A fuska yadangane Joseph din cikin yare yai mai kirarin gidan su,
Inda Joseph din yadan duka agaban shi yai mai yar gaisuwa irinta al,adansu
Abdullsamad yadan bugi kafadar Joseph din alamar ya karba mai gaisuwa,,
Joseph yace mai baba kana garin nan shine kashige haka shiru, ,,
Murmushi yayi yadan mike ya ciro wata tsohuwa ashirin a aljihun shi yana kokarin zuwa wani shago xuwa sayo masu pure water leda,
Cikin sauri Joseph yace mai a,a yabari kawai ,acikin nuna damuwa da kulawa yace ma Joseph kabari in shayar daga kai daga cikin dan abin da nake dashi pls,
Yanamai daga hannu alamar ban hakkuri agare shi,
Dole badon sun so ba yakarbo masu ledan ruwa, gida biyu yadawo katakata cikin sauri ya mika masu,
Sukaiyi mai godiya Joseph wanda ke ji alokacin kamar ya zubar da hawaye don tuna kowaye Emeka,
Yace mai ina sauran yaran shi suke, nan yake sheda masu cewa, mutum uku suna nan tare dashi,
Saura kuma sunan can garin su tare da maifiyar su,
Dan shiru ya biyo baya duk kan su kowa da abinda yake anyanawa acikin zuciyar shi a lokacin,
Joseph ne kauda shieun take cewa yaso koda zai samu ganin yaran koda mutum guda ne daga cikin su don yana son suyi wani yar shawara, nobar wayan babban ya basu, wanda uban yace yana koyon sanar Carpenter ne yanzu,,,
Kudi yabashi dubu hamsi yace mai nada wani sati zaiga sako in ya koma,
Sundanyi hira kadan sannan sukayi sallama, dashi suka barshi, cikin tausayawa da irin halin da yake ciki a yanzu,
Ganin wana bawan Allah yasa zuciyar Joseph a cikin wani irin
yanayi, wanda ya hanashi sukuni,
Kasancewar yau jumma,a ne mutane sai haraman zuwa massalaci sukeyi gungu,gungu mata kuma suna gida sun chaba ado kamar sallah,
Gidan Ànty Dije ma ba,abarsu a baya ba don daga manyan har yaran cikin kwalliya suke suma,
A,wasu gije har abinci akeyi ta musanman don farincikin da darajan wanan ranan,
A wasu giden masu dan hali kuma zakuga ana ta rabawa yara dan abin sadaka wasu da safe wasu kuma sai bayan ansauko daga jumma,a,
A lokacin da kowa ke ta haraman zuwa sallah jumma,a daidai lokacin ya shigo gidan na Anty,
Wanda a yanzu duk sun saba da irin zuwan shi sun,san cewa inhar yana gari to baida gurin hutu sai guri su
Saboda har cikin ranshi yana son yananyi irin na antyy Dije
Don mace ce wadda tasan kanta dama duk wani wanda yake tare da ita,
Alwala maryan keyi da buta a yar tsakar gidan su inda Assalam ke tsaye wai yana jiran tayi tabashi,
Muryan Maryam din ne ke cewa kai Assalam wazai kaika masallacine wai tunda Daddy baya gari
Joseph yanuna da hannu shi yace da Uncle zamu tafi ma na, ko uncle,?
Yana mai tambayar shi, cikin azama,
Yace mai eh Assalam, tare zamu,
Maryam wace ke kokarin wanke kafar ta ta waiga da sauri takalli inda Joseph din yake,
Muryan Anty Dije ne ke cewa, kai Assalam kabar uncle ya huta pls, kabari har Daddy ya dawo sai ya kaika,
Kuka yaron ke kokarin yi alokacin ciki sauri Joseph yace No, bar shi inkaishi mana anty,
Buta yaron yadauka yafara alwala kamar yadda manya keyi,
Ba abinda ya fadowa Joseph a rai sai zuwan su jereselem, da kakar shi,
Inda sai kayi kusan duk wasu abu da musullumai keyi na ibada,
Gashi Assalam karamin yaro wai har yasan cewa zai gana da ubangiji yayi tsarki,
Muryam Assalam ce takatse shi yana cewa nagama uncle, mutafi,
Ga mamakin kowa mikewa Joseph din yayi yakama hannun yaro
A hanya yaga wasu idon sani yafarka motanisa yabasu yaron yace suje dashi
Ana tasowa suka kawo mai shi yatada mota yajuyo tun ba,a tashi ba,
Kayan su fruit yadan tsaya suka saye a hanya sanan suka karaso gida
Daga Anty har maryam sun matsu suji ya akayi da suka fita, tare zuwa masallaci da,Assalam,
Kayan fruit din suka shigo dashi nikiniki a cikin ledoji ,,
Maryam wace tafito cikin kwaliyar ta ko kallon su batayi a da suka shigo gidan,
Da kanshi ya nufi har gurin fridge ya aje kayan a hankali daidai lokacin Anty Dije ta sallamay tafito, daga daki
Yadda taga Maryam tayi mai sai kawai bataji dadin hakan ba,
Daki ta shige abinta don makada asata wani aikin,
Dakun Anty ta fado rai bace sanan tahau surfanta da sababi,
Maryam ta bude baki da zumar yin magana hannu Anty tadaga mata alamar batason jin komai daga gareta,
Tace baki da hankali ko wayo zance inba wqutaba yazaki nunawa mutumin da ake fatan shiryuwan shi haka a fili,??
Gaskiya ki gyara hali Maryam don kowa ma haka kike masu,
Kada ki kore min jama,a pls,
Maryam batace komai ba don tasan cewa yau ta batawa Ànty Dije rai sosai don batai mata fada haka gaskiya,
Murya na rawa tace don Allah kiyi hakkuri anty bazan karaba insha Allah,,,,,,
ZEEEE MAKAWA,,,,,,👏👏
[2/20, 10:09 PM] +234 806 595 8685: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
1⃣6⃣
ZAINAIB IDRIS MAKAWA
Zaune take a bakin gadon da ke cikin dakin su tai tagumi da hannu guda,shiru tayi sai tunane takeyi
Don tunda take da anty bata taba ganin fushinta ba sai yau,
Yau din ma akan wani bare kafiri , wanda ba musulmi ba ma,
Wai may yasa za,a dinga takurawa rayuwan tane haka akan sai ta yi abinda zuciyar ta bai son aikatawa,
Motsin da taji shi ya sanya ta dago kai da sauri don ganin ko waye shigowa, dakin,
Anty Dije ce tashigo dakin tana rike da wani dan ledar mai nuna tambarin shago ajikin shi,
Yar kujerar dake dakin ta zauna a hankali, tana fuskantar yar kaunar nata wanda tun dara bata fito ba,
A hankali Maryam din ta dago kai karo nabiyu takara kallon antyn nata, sai kuma ta sunkuyar da kanta kasa tana kallon kasa,
Cikim natsuwa Anty Dije ta fara magana maryam don nai maki fada yau shine kike fushi,
Kinfi son in barki ki dinga yin abinda bai dace ba ko yau she, ?
Dago kai maryam tayi da niyar yin magana suna hada ido dayar nata,sai kuma ta kasa fadin abin da tai niya,
Indan har kinga cewa wullakanta dan adam na da kyau sai kici gaba,
Tanafadar haka tamike tana cewa sai kizo ki ci abinci in kinga dama,
Dago fuska tayi caba caba da hawaye, ta dubi yar nata tace,
Murya kasa kasa tace nifa ba fushi nakeyi ba anty,
Fuskan Anty kumshe da murmushi tace Allah ya kyauta amma dai gaskiya ki gyara hali duk wanda zo gidan nan sai yai min korafi akan halin nakasa irin naki maryam,
A dan tsorace ko mamaki tadago fuska, takalli yar uwan,
Kuka tajeyi a hankali irin na bantausayin nan tace yanzu anty nice mutane kewa korafi,
A ranan wuni zungur maryam tayi a daki tana ta faman fushi da kowa don har Issalam mutumiyar ta bataga fuska ba,,,
Tunda safe tafito itace farkon fitowa tsakar gida tafara shara da kokarin dora masu abin kari kamar kullum,
Saida anty Dije tagama duk abinda takeyi san nan ta fito waje tasamu yar uwar ta tana
Sun gaisa kamar wani abu bai faru ba a tsakanin su,
A tare suka kara aikin sanan maryam tai wa yara wanka kamar yadda ta saba yi,
Tuki yakeyi akan hanyar shi ta zuwa Lagos gaba daya hankalin shi naga tunanen Assalam
Yaro karami ya iya yin alwala batare da ankoya mashi ba,
A hanya ya tsaya yaiwa kakar shi da Ejoma da suke zaune tare da shi a gidan shi na Lagos,
Tsaraba, a wani dan kauye da ake tsayawa kafin ashiga garin, lagos,
Tunane ya cigaba da yi na yadda zai, yi da mahaifin shi,
Don kwata,kwata baya son zancen kakar su a rayuwan shi,
Wanda shidai a iya zaman su yasan cewa mutumiyar kirki ce ita,
Ya iso gari lafiya saidai yasamu G/ma bata jin dadin jikin ta,
A yadda Ejoma ke fada mai tun wucewar shi kusan sati ke nan G/ma bata jin dadi amma ta hana a fada mai, wai don kada yadamu,
Wanka yayi ko abinci bai tsaya yaci ba tashiryo cikin waso kananin kaya sai kamshin turare ke tashi
Mama dake zaune saman kujera two siter yazo inda take ya zauna asaman hannu kujerar da take yadan rankafo kanshi saman kafadar ta kadan
Yana tambayar ta a hankali ki may ke damun ta sai ce mai tayi batajin komai ita,
Cikin dabara Joseph ya lalaba yar tsohuwar suka tafi asibitin da yake zuwa,
Likita ya dibata da kyau inda yace ba wani abu damuwace ke da munta kawai sai dai yadan rubuta mata yan magananuwa don tasha,
Bayan sun dawo gida dakanshi ya hada mata tea mai kauri ya hada da maganin ta yakaimata,
Zaunawa yayi gab da ita yana dan bata a hankali har tadan samu tasha,
Alokacin yadan mike tsaye da niyar barin dakin don yaje yadan huta, saboda yana tare da gajiya,
Hannun shi mama ta riko da sauri ya jiyo don yasan cewa da magana kenan,
Komawa yayi ya zauna gab da ita saida suna fuskantar juna a wanan lokacin,
Fuskan yar tsohuwar fam da damuwa tace My child something bad wan happen to you,
Joseph yadan kamo hannuta ya hade cikin nashi yana yar murmushi yace,
Mama nothing will happen to me just cool your mind pls,
Tace it ,will ,my son
I see am in my dream,
Dariya yakari yi mata yana mai rungumota zuwa jikinta,
Kalamai masu kwantar da hankali ya ke mata don yaga cewa ta saje zuciyar ta,
A hankali ya mike ya kamata zuwa kan gado ya kwanatar da ita tare da jawo bargo ya rufa mata,
A,hankali yabar dakin yana mai rufo mata kofar dakin,
Saidai may yana fita daga daki sai kuma maganar mama ya dawo mai sabo a zuciyar shi,
Fridge ya nufa yabude yadauko giran ruwa mai sanyi ya dan kwa kwada,
Hakalinshi a tashe don yasan cewa akwai abinda ke damun mama din saidai ba zai so ji ba don shi bai yarda da camfi ba rayuwan shi sam,,,
Maimakon ya shiga dakin shi kamar yadda yai niya sai kawai yasamu kan shi dazama saman daya daga cikin kujerun dake falon,
Yakai wani lokaci a gurin zaune yana tunane shi kadai bakajin karar komai a falin inbada na,urorin daje ta aiki a cikin falon,
Azuciyar shi yake tunane don yasan cewa maganar irin su mama ,g tasu al,adan ba karamar magana bace,
Da wuya su furta bai faru ba, to amma shi gaskiya har yanzu bai yarda da zance tsafi ko kuma wani believe ba can,
Yakai wani lokaci gurin zaune yana iya na,zarin shi akai,
Daga karshe dai ya mike jiki ba kwari ya shige don ya kwanta,
Abakin gado yake a cikin shigar shi ta kayan barci bayan yagama komai, ga irin al,adan yakeyi kafin ya kwanta,
Bible ne rike a hannu shi gwiwowin shi suna kasa kan shi a saman gado idon shi a rufe yafara jero addau,oin da yasaba yi kafin yashiga kwana
Saidai wanan karon ya dan sauya addua,n shi bakamar yadda yasaba ba,
A hankali ya mike zuwa kwanciya saida a lokacin kuma watan shi tai kara alamar sako ya shigo mai,
Samuel ne ke sanar mai cewa Dad na fada dashi cewa anfada mai wai Joseph din yatafi gurin Abdullsamada
Mamaki yayi so sai dajin haka don haka sai yai alwashin cewa daga wanan karon ba zai kara, daukar zance Dad ba na hana shi yin alheri ga duk wanda yaga dama nan gaba,
Abdulsamad wanda ko ganisa mutum yayi bai san shi ba,a da dole ya tausaya mai,
Balle shi da yagirma a gaban shi
Shi agare shi may,ye amfani samun mutun ace bai iya taimaka wa na