Showing 201001 words to 204000 words out of 255288 words

Chapter 68 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1370

min kamar nayi wani aiki mai yawa
Cikin wani irin kararan murya tace Allah sarki, idon ta nan da nan yai kamar ya kawo kwalla,
Tace cikin kariyar murya kamar ta mai kuka uncle kasha magani ko?
Bawai magani zan shaba ai da ace zan samu wanda zai mun dan taushe a hankali , a hankali da kila bazan kara ko minti biyu ba zanyi barci,
Kai uncle inji maryam cikin wani irin murya mai nuna tausayi maryam tace,
Kasha magani za ka rage jin pain din da zaran ka sha,
Maryam yakira sunan ta cikin wani irin murya yace,
Nidai fatana Allah yasa baba ya idda nufin shi akan mu batare da ya canza shawara ba,
Runtse idon ta tayi daga i nda take tana maijin kunyar abinda yafadi yanzu din,
Kamar yasan abinda takeyi yace, Yes, ina son duniya ta sheda cewa ke din ce mata, ta halas,
Sai kuma yadan ma rai,raice muryanshi ya ce maryam kiyi hakkuri ki rike Yusuf dinki amma,
Ki gwadawa duniya cewa Furen Juji dane kamar kowa,
Addini bai ce a kyamace shi ba kamar yadda wasu ke ikirarin hure maki kunne akaina,
Hawaye ne masu dumi suka zubo a idon maryam din,
Nan da na ta ringa she,shekan kuka kamar ya fada mata wani magana na daban,
Dif ya kashe wayan shi saboda ba zai iya sauraron wanan kukan da maryam din shi ke yi ba a yanzu,
Cak ya kashe wayan ya wurgata gefen filon dake saman gadon shi, sai kawai yashiga cikin damuwa,
Tausayin rayuwar su yaji da shi da ita maryam din ,don yasan cewa tayi hakkuri sosai tayi biyayya ga mahaifinta,
Rayuwa abin tausayi ce gare su shi da maryam sam bai taba tunanen cewa zai so wata mace irin yadda son maryam din yashige shi haka a lokaci guda,

Tafe a motocin su sun fito wani kauye kallon wasu irin shanaye da Sonny din ke so,
Yusuf sai sauri yakeyi don su karasa wani kauye mafi kusa don su samu sallah jumma,a,
A wani massalacin kauye da yacika makil da jama,an musulmi suka parker motocin su,
Don su samu gabatar da sallah su ta jumma,a a garin,
Sonny kawai suka bari a motar inda yake kallo yadda kowa ke sauri don kada a wuce shi,
Abinda ya kara bashi mamaki shine da mai, arziki da talalka duk guri guda suke tsayawa su hada kafadar su,
Har zuwa lokacin da suka idar yana kallo yadda mutane kebawa juna hannu suna musabi,a,
Sai bayan sun shiga motocin su har sun yi nisa ga tafiyan su ne Sonny ya jefowa Yusuf tambaya, cewa,
Yaga duk guri guda suka tsaya sai mutun guda dake a gaban su,
Tokin motar shi yake yi a hankali batare da yace mai uffan ba,
Sai da suka danyi nisa kadan kamar ba zai yi magana ba sai yace wa Sonny din batare da ya kalle shi ba,
Addinin mu addini ne mai bawa kowa yancin shi batare da nuna bambanci ba ga komai,
Sonny din yace O, I See,
Harzuwa lokacin da suka kai cikin gari a gajiye daboda nisan kauyen da suka tafi,
Inda Sonny din yai ta hotuna da shanaye da fulanin rugan
An kai shi gurin wasan dawakai inda Sunny din duk yarude saboda yadda yaga dawakai lafiyayyu sun koshi sai harbin iska suke yi,
Washe gari ranan Sunday aka kaishi Church inda mahaifin Yusuf tare da, sauran members suka ji dadin zuwan shi gurin su,
Yai masu kyauta ta bajinta inda sukai ta ihu suna cewa praise the Lord,
Tare da,shi suka kwashi rawan su a wanan satin inda shi bawai abinda sukeyi ya damay shi bane,
Sai Sonny yafidda rayuwan cewa zai kara ganin maryam kafin yabar garin ,
Don ya fahinci Yusuf bai ra,ayin haka a rayuwan shi sam, hakan yasa shi fita zancen kwata kwata,
Duk da yaso ace sun wuce batare da ya kai bakon nashi gurin Anty nashi ba amma sai yaga rashin dacewan hakan,
Hakan yasa shi biyawa dashigidan bayan sun dawo wani kauye wurin kallin yadda suke noman su a,local, way ,
A kofan gidan suka dan tsaya inda yusuf yai ta rafka sallama sai zuwa can yaji muryan matar gidan ta karba mai,
Kusan a tare suka shigo su uku gidan shi da Sonny da Jibrin,
Anty ce ta tare su cikin kwaliyan wasu shadda kamfala dake ajikin ta,
Sam maryam bata,san da shigowar su ba tana saye cikin dinki atamfa buje da riga da,sukai mata dagwas a jiki,
Yusuf naganin ta ahaka wani irin kishi ya ziyarci zuciyar shi ya rufe mai idon shi,
Saidai bai bari sun fahinci halin da ya ke viki ba saiyadan basar da hira da antyn shi,
Shiko Sonny yana ganin maryam sai ya shiga washe baki yana mai kokarin jan ta da hira,
Sanin halinta ya dan sa Yusuf sake dan jikin shi don yasan irin hanlin miskilancin maryam din,
Dan wake da mai da yaji sukayi don suci don haka,shima Sonny ya zauna ya kwashi wanan girkin har yana akaro mai,
Sai kuma daga baya hira so sai sukayi indayake tambayar su akan musulunci su dan bashi bayani,
Banda Yusuf wanda ke charting da maryan a lokacin,
Yana fada mata irin yadda yaji lokacin da suka shigo gidan,
Sonny ya koma bayan irin dibin alherin da yaiwa mutane taban mamaki,

Bayan yakoma sauth korea ne Yusuf yai mai waya don yaji ko ya sauka lafiya,
Anan suka dinga hira sai kusan karshe ne Sonny yake cewa Yusuf ai tun da yadawo zancen da sukaui na cewa ya canza addini zuwa ta islama gaskiya yashiga zuciyar shi,
Yaji kuma zai koma din amma on one condition zai koma,
Yusuf cikin jin dadi dafarin cikin jin cewa Sonny zai shigo Islama yace ,
Yace cikin karagi ya fada mai ko manene wan condition din,
Sonny yace yana rokon shi alfarma da yabar mashi maryam ya aura, don ta taimaka mai gurin fadakar da addinin shi,,,,

ZEEE MAKAWA YELWA
[4/28, 5:40 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
8⃣1⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI

Ina, rokon Allah Ya saukar da Albarka, Alkhairi,Falala, Wadata, Ni'ima, Gafara, Rahama, Lafiya mai amfani, Kwanciyar Hankali a garemu da Zuri'armu, da Musulmai Baki dayan mu Masoya FUREN JUJI,,,


Yusuf wanda ya kai wani lokaci agurin da yake zaune ba tare da ya motsa ba
Saboda mamakin maganar da Sonny din yai mai yan mintituna kadan da suka wuce,
Hamdala yai ga Allah ubangiji subbahanahu, Wata,allah,
Da ya kaddarace shi da ansa kalman shahada yafitar dashi daga cikin kafirci,
Idan ba halin rashin imani a zuciya ba may zai sa Sonny ya tunkare shi da wanan zancen,,
Na jahilci watau badan Allah zai musulunta ba ke nan don biyan bukatar shi ce kawai,,
Wanan maganar yasa tunawa da wani Christian dan church din su wanda,
Yai ridda har sau uku saboda jahilci inda ya zama Christian sai ciwo ya wuce daga jikin shi,
Idan ya koma musulmin shi sai ciwon yadawo mai sosai fiye da farko,,
Sai in har ya koma Christian zai samu sauki acewan shi wai a church ne saukin nashi yake,
A haka har ya mutu cikin Christiatanci, batare da ya farga da cewa taimo yaje samu daga yan churches da kulawa fiye da zaman shi a cikin musulmi,

Wani irin ajiyar zuciya Sadiya tayi bayan tagama jin labarin da fauziya ke fada mata,
Akan irin alherin da Yusuf tare da abokin shi sukayiwa mutane a ziyaran da suka kawo,
May Yusuf ke nufi da ita ne yanzu, sam babu ita ke nan acikin tarihin rayuwar shi,
Wanan abin yai mata ciwo duk da tasan cewa kanin mahaifinta ne yai mata silar wanan sherin,
Tabas yazama dole tamike tsaye ta san abin yi kafin wankin hula ya kai ta dare,
Tamike tsaye tana gyara gyalen da ta sabalo a wuyar ta,
Tana cewa kwanan nan zai dawo gare ta don ba laifin ta bane ai da zai dauki tsana ya sa mata
Ita har gobe tana so shi don haka bazata iya hakkurewa da shi ba, a rayuwan ta,
Ta,dan ce a hankali tabbas sai ka dawo da kafan ka, nice dai matar taka, don ka sani,,

A hankali gudu yake shararawa saboda yana sauri kada rana tai mai bai isa da guri ba,
Ganin ya fara hangen garin Kano' din yasa shi dan rage gudun da yake yi,
Next kauyen da zai iya sada shi dagarin kano din yaga dan dan,dazon mutane a bakin titi ga wani mutun tallabe a jikin wasu matasa, su biyu,
Duk motocin dake gaban shi sun wuce batare da sun tsaya ba,
Tun daga nesa idon shi yahango mai abinda ke faruwa sai dai zuciyar shi tabashi ce inda muggan mutane ne baizaiga wanan taron ba acikin gari haka,
Yusuf, wanda ke cikin motar shi yana tafiya a hankali, yazo gab dasu ya tsaya,
Baka jin komai sai kiran da ke tashi a motar da kamshi da sanyin A,C,
Kafin ya sauke glass sai,ga wani dattijo mai farin gashi jefi,jefi akai yadan leko shi,
Yace dan Allah malam ka taimaka muna da wanan bawan Allah zuwa cikin gari asibiti za a kai shi,
Ba musu ya bude masu security din motar sai motar ta bude,
Har zasu shiga sai yaji muryan wani daga waje gurin mutanen yana cewa kai amma dai ku baku da hankali,
Kuga mutum haka cikin wanan irin motar shine har zaku tare shi batare da,kun san kowaye ba,
Kudibafa ku gani lafiyayen mutun yafito neman kai kamar makafi kun wani fadawa har kai uku,
Murmushi Yusuf din yayi kawai sai,da yaga alamar cewa sauran mutanen sun dan tsurata da zancen mutumin,
Saida ya lumshe idanun shi sanan yace masu , duk da ba,a gane macuci a fuska,
Ni saboda Allah da Annabi zan taimaka maku amma fa idan kun yarda,
Tsakanin su aka dan yi jimm sai wani daga cikin diyan mara lafiyan yace Allah ya tsare ku gyara mu shiga kawai,
Tafiya yake yi dasu a hankali yadan yi yana waigen tsohon dake ta Nishi sama, sama,
Tambayar su ya yi wani asibiti ne zaku kai shi, ?
Nan suka fara muhawaran asibitin da ya fi saukin ganin likita, da kuma saukin kudi,
Don haka, Yusuf yace may ke damun baba din ne. ?
Yaron nashi wanda alama ya nuna cewa shine babba daga cikin su yace,
Yau kwana biyu bai fitsari bai bahaya,
Subbahanallahi inji Yusuf din cikin dan rudewa,,
Yace akwai wani asibiti ne da kuke ganin ya na da kyau mu tafi can,?
Ganin cewa mutanen kauyawa ne yasa shi dauko wayan shi,
Noban Alhaji sambo ya kira yana bincikan shi ba bata lokaci yai mashi kwatance,
Basu wani shawuya ba ga kwatancen da akai masu,
Yusuf wanda yazo kano harkan business din shi sai gashi ya buge ga zirga,zirgan asibiti,
Dashi akai komai, har zuwa lokavin da likita ya zo yadiba tsohon dake ta kugin wahala saboda azaban da yake sha,
Dubu sittin da yan kai likita yace su fara bayarwa tukun ,
Zasu tsaya inda,inda Yusuf ya jawo yan dubu, dubu daga aljihun rigar shi ya mikawa likitan,
Ba a fi wasu yan mintoci ba aka jaye mai komai yasamu sa, ida,
Gado a,kabashi don haka Yusuf din ne yakara biyan sauran kudaden da ake bukata,
Tun safe sai zuwa bayan sallah azahar ya samu kan shi,
Sai, a lokavin yashigo dakin dakin bayan ya gaishe su a mutunce sanna ya gusa gurin tsohon da yaji suna kira da malam yai mai sannu ya jikin, ?
Malam din yadan dago kai, zuwa gurin da Yusuf yake tsaye daga gefen shi,
Hannun shi yadago a hannkali ganin may yake nufi ne yasa Yusuf din saurin mika mai nashi hannun,
Yarike hannun jimmmm har zuwa wani dan lokaci bakin shi kawai zaka ga yana motsi,
Sunan shi ya tambaya yace mai Yusuf yake, sai tsohon ya dan gyada kai alamar gamsuwa,,
Kokarin wucewa yayi bayan yai masu sallama, daya daga cikin su ne yai a,zancin karban nomba Yusuf din da sunan zasu kirashi suyi mai godiya daga haka yai masu sallama, ya nufi gurin da zai sauka,,,,,

Kwance take saman gadon ta tana barci amma sai juye juye takiyi daga kwancen, da take din,
Gudu take tayi a,wani bakin daji mai duhu da kuma, sarkekiya,
Rigar barcin dake saye a jikinta shine saye gareta a cikin mafarki,
Gudu kawai takeyi sai wasu halittan da bata taba ganin irin su ba ke bin ta a guje,
Hakin da takeyi agudun shine ya baiyyana afili tana ta juye juye,
Tana gudun tana cire wanan yagwagen dake sarke mata hanya da jikin ta,
Bakin wani rami suka kawo ta inda taja ta tsaya guri guda,
Gani cewa wa, yanan halittun sunyo kanta gadan gadan yasa maryam din kara hannayen ta biyu ta rufe jikin ta zuwa fuskan ta,
Tare da furta Innalillahi cikin wani irin murya mai karfi,
Wanda har mueyan yakai dakin da Anty dije take tare da dan ta Abubakar da maigidan ta, da yazo kwana biyu da suka shige,
Wanan sautin da Anty Dije da maigidan tasuka ji na maryam shi yasa su taso cikin sauri zuwa dakin da maryam din take kwance,
Jikin ta ya jike kamar wace akaiwa yayafin ruwa akai,
Jin karan bude kofan su anty yai daidai da saukowan ta saman gado da karfi ,
Inda tayo kan Anty nata cikin kaduwa tana kokarin shigewa jikin ta a tsorace,
Hakalin Anty Dije ya tashi matuka saboda irin halin da, ta ga kaunar nata a ciki,
Don haka sai ta rugumay maryam din a jikin ta inda take ta maida numfashi guda guda a tsorace,
Dakin suka fito da ita zuwa falo inda sukabar mijin na Anty yana yan dube dube a dakin kamar wanda ke bidan wani abu, a dakin,
Kusan a nan suka karasa kwana falon inda har da yaran suka kwaso zuwa falon,
Dakyat suka ga safiya da maryam din saboda irin halin firgicin da ta shiga ciki a lokacin,
Tun a massalaci gurin sallah Asubah mijin Anty ya shedawa baba abinda yafaru da maryam din a daren jiya,
Gida baba ya koma ya gyara shiryawa ta re da zuwa gurin, wani aminin shi malami ne,
Malam na, Ngaski, inda yai yan abubuwan su na malamai,
Daga karshe ya danyi rubutu yasa a cikin wani leda yace abata tasha zata samu barci,
Hakan akayi kuwa don dai maryam din ta samu barci sosai har da kuma zafin da jikin ta yayi duk ya rage,
Sai zuwa kusan la,asar tasamu tadan mike, ruwa ta watso a jikin don takara jin karfin jikin ta,
Bayan ta dawo tasamu anty ta hada mata abincin ta ,
Saida tai sallah sanan ta samu guri ta zauna tafara dan tsankwaran abincin a hankali,
Mafarkin da tayi ne yafado mata a rai irin yadda tai ta gudu acikin wanan bakin daji,
Siffofin wa yan nan miyagun namun dajin da tagani su yo kanta yasa ta saurin zabura da karfi tankar a lokacin ne abin ke faruwa,
Anty ce cikin fadar Wa,iyazu Billah, maryam ki dinga karanto addu,a a bakin ki pls,
Hakan yai daidai da shigowan baba gidan wanda yake dauke da wani bakin leda a hannun shi,
Anan ne yadan murmusa yace Allahu Akbar watau duniya abin tsoro ne Dije,
May Maryam ta tarewa mutun da har zai sata gaba haka yarinyar da naga bama fita takeyi ba,
Karbi wanan maza bata tashanye kuli guda gaba daya yanzu ta, shafa sauran ajikin ta,
Dayan kuma da dare idan zaku kwanta sai ki bata Allah ya kyauta,
Duk sukace amin alokaci guda tare da karban kullin suna budewa
Mahaifin nasu ya dan kalli yar tashi wace take hankali a tashe duk ta wani ramaywa a lokaci guda,
Yadan gyada kan shi alamar takai ci acikin zuviyar shi fam,
Addu,oin tsari ne ya kara nanata mata idan zata kwanta tare da cewa insha Allah zata daina ganin abinda take gani, kuma Allah zai kare ta daga duk wani maisheri,
Daga haka ya mike zuwa yai madu sai da safe,

Yusuf wanda yake masaukin shi zaune ga abincin da aka kawo mai ya sa agaban shi amma yakasa cin komai,
Tunane duk ya addabi zuciyar shi kamar yai ihu ko zai samu relief a lokacin,
Sakon da Sonny ya kara turo maine akan zancen yana son musulunta am.a sai idan Yusuf zai bar mai maryam a matsayin gift din shi na shiga musulunci,
Wani irin nisawa yayi tare da runtse idon shi da suka kada mai sukayi jajir alokacin,
Kara bude su yayi inda ya kurawa labulen dakin ido kamar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login