Showing 168001 words to 171000 words out of 255288 words
Chapter 57 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete
dama saboda baida ado da yawa so sai,
Kai ya daga ya kalle ta da mamaki don jin cewa ra,ayin su yazo daya, da ita,
Saboda tun da aka zube zanuwan idon shi yake akan wanda ta zaban
Har zata juya don barin gurin saboda rashin sanin ko may za su yi da zannuwa haka,
Muryan mutumin taji yana cewa zan,nuwan ai kudin su kaza ne,
Dan juyowatayi tace wa mutumin kai malam fadi gaskiya yaushe kudin su ya kai haka,
Jibrin yace wa maryam ta fada masu kudin kayan a takaice maryam tafada masu
Amma kuma sai tace sai dai in har zasu bashi yadda yace ne saboda tai mako,
Dariya duk suka agurin ban da Yusuf wanda dan murmusawa yayi inda ya bukaci mutumin da ya bashi turmi talatin,
Yace idan basu isa ba zai kirashi ya karo mai,adadin yadda ake so,
Daga haka mutumin ya kwashe kayan shi ya tafi yana mai zabga masu godiya,
Inda maryam take ya dan kalla yana mai cewa ki kwashe su ki adanawa anty kafin ta dawo,
Mamaki takeyi zuciyar ta,ace kaya masu yawa haka kuma kala guda,duk, za,a saye, koma na may ye oho,
Sai kawai ta tsinci muryan Yusuf yana cewa duk wace tazo muna wanan farin cikin za a bawa
Cikin mamaki tadan kalke shi kamar zatayi masu magana sai kuma ta bi umurnin shi tafara kwashe kayan zuwa saman wani kujera,
Hira yaci gaba dayi shida Jibrin inda maryam takoma daki ita da yara har zuwa dawo wan su Anty dije,
Bayanin da Yusuf kewa Anty Dije inda take sauraren shi a cikin mamaki,
Turmin zani atamfa da kudi dubu biyar yabawa ko wace mace da tazo sha,anin bukin,
Bakaramin mamaki Anty tayi jin wanan irin kyautar da yai wa mutanen ta,
Don haka daya bayan daya ta dinga aika masu da alherin su gid kuma tana,sheda masu wanda ya basu,
Ta aikawa iyayen mijin ta dashi da kuma, nata,uwayen
Hakan ne yabawa baba daman kara tunawa da zancen shi na son ya hada zuri,a da wanan yaron,
Saidai yasan cewa mutane zasu zarge shi da cew saboda abin hannun shi Yusuf din ne yake son yin hakan, ,
Amma dai shi in son samu ne yana mai son wanan abin ya tabbata,
Bayan buki da kwana biyu Yusuf ya shigo gidan Anty inda ya samay su gaba daya zaune a falo,
Ya saye cikin wata wagambari,mai ruwan sky colour, sai agogon da ya,daura, a hannun shi,
Hular kan shi baka ce sai takalman kafar shi bakake, sai kamshin da ke tashi,
Ganin su gaba daya afalon har mijin Anty wanda ya,shigo garin bayan kwana daya,wuce,
Wani irin nauyin su Yusuf din yaji ,,inda yai, kamar ya koma baya,
Amma sai mijin Γnty din yace mai haba dai kai,ko shigo mana,
Yace haba dai Yusuf kamar wani bako can idan baka sake jikin ka ba har yanzu da Anty naka sai zuwa yaushe ?
Maryam dauko mai cup mu karya tare, inji mijin Anty Dije yace wa maryam din
Yusuf wanda kan shi na kasa bai daga ba yace wa mijin anty ai baya son tea so,sai yafi da, son ya sha kunu, shi,
Da mamaki yake kallon Yusuf din inda yace kai kan iyalinka sun huta, gaskiya da wahala,
Sai kuma yai saurin kai kallon shi ga Yusuf wanda ke shirin zama a lokacin yace
Ya maganar zancen da Dije tace baba yai maku ne kai da maryam, naji shiru mana,
Maryam wace a lokacin tana kokarin zuba mai kunun shi na gyada dake a cikin jug a cup
Wani irin kallin mamaki ta aikawa Anty nata dashi wace itama dai mijin ta take kallo,,
A hankali takai kallon ta ga Yusuf wanda shima kokarin sauke kai kasa yake yi,
Jin gurin yai tsit ne yasa Illiya dagowa yai wa kowa kallon mamaki kai tsaye ya fara magana,
Mijin Anty Dije ya kai kallon shi ga Yusuf din wanda kan shi ke a duke yace,
Yusuf mu ba,zamu so, ace baku shirya dajuna ba kai da maryam ,
Sabo irin yadda muke tare da kai a matsayin dan uwa daga cikin mu,
Don dai ita maryam nasan cewa bazata kyatare zancen mahaifin ta ba,
Da sauri ta kara kallon mijin yar ta don jin abinda yace a kan ta,
Don Allah ya Illiya ka taimaki rayuwata kasa baba ya janye wanan zancen,
Wanda yake kokarin kwace min daga farin ciki na wanda nake kauna
Wanan furuncin nata na karshe yasa,duk kan su kura mata ido,
Yusuf wanda ke dan motsa kunu a cup ya ansa da cewa tabbas maganar maryam gaskiyane,
Tunda tana tare da wanda take son tun da dadewa
Kaga bai dace ace an rabata da wani ba dan wani,
Wanan maganar da Yusuf yayi ta karshe shi ya,bawa mijin anty tausayi so sai
May maryam ke nufi da cewa a bawa baba hakkuri sam bai taba zaton haka daga gare ta ba sam,
Don haka cikin tsawa yadaka mata cewa baki da hankali a she maryam ina maki daukar mai hankali, ?
To ki san da sanin cewa indai babane iyakar maganar shi ce ya fada ba wai zabi yabaki ba,
Don ma dai kawai Yusuf din ya kasan ce shi bako ne daga cikin mu dakin ga aiki da cikawa,
Hawaye ne ya fara silalo mata daga fuskan ta tana sharewa a hankali,
Mijin Anty Dije yace ina ma wanda kikewa ikirarin cew kina dashi din yake, ?
Maryam wacce saboda haushin irin yadda mijin yar ta yai mata a gaban Yusuf kamar wace ba tada gata,
Yasa ko kallon shi ba tayi ba takama hanyar zuwa dakin takawai tana mai share hawaye,
Tukin mota yakeyi amma hankalinshi na ga magganganun da sukayi da safe a gidan Anty Dije,
A hankali ya shafa fuskan shi da tafin hannun shi,
Inda ya hade wasu miyau masu daci da suka tsaya mai a bakin shi,
Har ya isa garin Abuja maganar taki fita mai azuciyar shi,
Bai huta ba ita kuma maman Choima ta haushi da fada akan cewa ya cuce su da ya aurawa Ibrahim da Naimat,
Don may ya musuluntar da ita batare da sanin iyayyen ta ba,
Dukan shi tsohuwar ta shigayi da hannun ta bibiyu tana mai yin kuka da ihu,
Ganin zata iya bata mai lokaci ya sa shi janta a hankali zuwa dakin ta inda ya zaunar da ita a hankali saman gado yana mai ce mata ba gaskiya bane,
Tace mai ai Samuel ya zo bayan baya nan yake sheda mata abinda ke faruwa,
Sai da ya samu yadan lalabata ya wuce zuwa dakin shi,
Rigar dake ajikin shi ya sabule gaba daya tare da jefata saman gadon shi,
Shima fadawa yayi tare da lumshe idon shi yanamai karanto Subbahanallahi, Walhamdullahi Wallahu ,Akbar,
Har zuwa lokacin da yaji zuciyar shi tai mashi sanyi,
Sannan ya mike zuwa bathroom don yadan watsa ruwa, ko zai ji sanyi a rayuwar shi irin yadda yake ji,
Sai bayan ya fito ne yana,saye da wata jallabiya mai ruwan milk, colour,
Yana dan goge ruwa a kan shi wayar shi tafado mai a rai,
Sai a lokacin ya tna cewa yasa ta a silent tun yana hanya,
Da sauri yadauko wayar yana dibawa, kirane kusan talatin da wani abu,
Inda akasarin su duk kurane daga anty Dije sai kuma sauran friend's da abokan aiki,
Kiran karshe dayagani shi ya bashi mamaki don sam bai yi zaton ganin kiranta ba a wanan lokacin,
Ba kowa bace illa maryam da mamaki yake kallon sunan nata yana mai tambayar kan shi ko may take so dashi har takira shi,,
Wayan ya ajiye inda yanufi gurin da sallayar shi take yana kokarin shimfidawa,
Karar wayar shi ce ta katse shi a lokacin don ya mai da ita da karar ta,
Anty yagani rubuce a screen dinwayar tashi alamar itace ke kiran shi,
Dauka yayi amma sai ta haushi da masifa tana mai cewa ina ya shige haka tun da safe take neman shi bata samun shi,
Nan yake sheda mata cew yana Abuja kada ta damu,
Cikin kwantar da murya tace Abuja Yusuf ?
Abuja ka koma baka fada muna ba may yafaru Yusuf kawuce yau ba sallama haka,
Murmushi yai mata a karo nafarko yau tun xa gari ya waye mai,
Yace ba komai Anty tafiyar ce kawai ta riskeni a haka,
Shirune yadan biyo baya batare dakowa yai magana ba daga cikin su,
Kashe wayan yaji tayi abinda bai taba faruwa ba ke nan a tsakanin su,
Yana kashe wayar kamar hadin baki kiran maryam na shigowa
Amma sai ya share kiran nata kawai yatada sallah shi abin shi,
Ya dade a zaune yana lazumi inda yake ta kai kukan shi ga Allah akan Allah yai mai mafita, da kuma zabi na alheri a rayuwar shi,
Ya mike don ya kwanta ko zai dan samu barci yadan huta,
Ya kwanta kamar minti biyar yaji kira ga wayar shi kokarin kashe wayar yakeyi a daidai lokacin da yaga sunan maryam again a saman wayar,
Kamar ya share ta saidai yadaure ya dauka saboda time din da agogo ya nuna mai nadare,
Muryan taji a cikin wani yanayi tana mai ce mai hello,
Inda shima ya karba mata da cew wa,alakissalam,
Sai kuma tai shiru batare da ta furta komai ba,
Idon shi yadan rintse don wani irin abu da yake ji yana taso mai a zuciya,
Yana niyar kashewa ne yaji muryan ta tana cewa Uncle dan Allah ka taimaka min agurin baba ka fada mai gaskiya cewa ba soyayya atsakanin mu ko kadan,
Yanajin tafafi haka yakatse wayar tashi tare da rufe layin nashi yana mai runtse idon shi da suka kada sukayi ja,alokacin,,,,,,, l
SEENABU ZEE MAKAWA YAURI KEBBI STATE,,,
[4/7, 5:57 AM] βͺ+234 810 770 2287β¬: πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
FUREN JUJI
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
6β£8β£
ZAINAB IDRIS MAKAWA
IYYA KA,NA ABBUD WA,IYYAKA NAS,TA, INN,,
Dan Allah dai jama,a kuyi hakkuri dani saboda lokacina ne nake batawa ina faran ta maku rai dashi,
Bawai dole yadda mutun yake so zai samu ba,
Kuyi min Uzuri pls bawai magana daya nake ta fadi ba yadda labarin yake ne na,ke yi,,,,
πππππππ
A,A ne zaune a gaban kanin mahsifin shi suna magana acikin na,tsuwa inda yake sheda mai cewa ya gama kammala duk wani abin da yadace da ake bukata,
Ba musu kanin mahaifin nashi wanda ke shugabancin al,amarin shi.
Sai yaron duk ta bashi tausayi don shi da a ce ya na da hali ne shi da kan shi zai wa yaron alheri, da duk wani harkan auren shi,
Mutumin yace wa A,A din zai yi magana mahaifiyar shi, don ya shawo kan ta,
Da haka sukayi sallama ya bar gidan kanin mahaifin nashi,
Bai wani nisa da tafiya yakira maryam yana sheda mata cewa cikin satin nan za,a kawo lefen insha Allah,
Duk irin yadda tayi kokarin boye farin cikin ta A, A sai da ya gane har yaji tausayin su ya kama saboda irin yadda suke son junan su
Amma ga mahaifiyar shi tana kokarin raba su a lokaci guda saboda son rai,
Maryam batai kasa a gwiwa ba ta sheda ma yar uwar ta abinda ake ciki,
Maganar Anty Dije ta saurara amma tasan cewa ba wai lalai ne hakan ya yuwa ba,
Don haka sai bata dauki zancen da wani mu,hinmanci ba kawai sai ta share zancen, batare da ta fadawa kowa ba,
Kwana kamar biyu da zancen wanan kanin mahaifin na A, A ya samu mahaifin Maryam, tare da wani dan uwan su akan zancen,
Inda baba ya sheda masu cewa subari sai ya ga yarinya tukun,
Daga haka kawai,bai kara wani zamce ba amma sai may kamar sati guda da magana da wani yammaci sai ga mata dauke da akwatina, har guda uku da kit din su,
Abin ya bawa anty dije mamaki kwarai da gaske, a inda ta aika makwabtan su akakira mata wata kawar ta,
Matan sai wani yatsinar fuska suke yi kamar masu jin wari ko ka,zanta,
Da farko ita Anty Dije bata so ta karbi kayan ba don bata da masaniyar komai akai,
Amma sai wanan kawar na ta tace mata su karba ba,a haka, nan, alheri baizo ma a gida ka kore,
Ba wasu kudi masu yawa anty ta bazu tukuici ba saboda rashin sanin zuwan su a lokacin,
Su ma dai ana su bangaren su fita da,sunan Anty Dije a bakin su kan cewa ba masu wani taron arziki ba,
Can suka koma gidan suka samu shi A A din kowace daga cikin su da nata abinda tace mai akan wai bai samu diyar gidan mutunci ba,
Ga su diyan tallaka am.a suna ma mutane kallon rainin hankali,
Duk maganganun da,suka fadi a gamay da maryam din zu zafe shi a zuciyar shi,
Saida bai ce masu komai ba sai sauraren su da ya dinga yi a lokacin,
Amma yana barin gurin su ya sa waya ya kirata sai abinda bakin shi yaraga mata yana cewa wai an wulakanta mai yan uwan shi
Ita ko maryam sai hakkuri take bashi tana cewa gaskiya basu fadi daidai ba saboda tasan cewa ba halin Anty Dije bane haka nan,
Don haka sai ma taga cewa shi ai bai ga laifin nashi ba sai yar ta kawai, kashe wayan tayi tana mai mugun jin haushin matan da sukai masu wanan mugun kazafin,
Tun wanan lokacin sai bata kira A,A din ba shi kuma haka, dakewa tayi dashi,
Bayan wasu kwanaki suna zaune a tsakar gida saman wata katuwar tabarman roba zaune, suna shan iska,
Kasan cewa garin yau babu wutar ne fa zafi yai masu yawa,
Bayan sallah isha,i zaune take tana lazumi inda yaran Γnty ta ke ta faman damunta da surutu,
Muryan Baban su ne su,kaji a cikin wanan daren,
Take gaban maryam ya tsinke ya fadi. Gaisuwan baba suka fara yi suna mai sannu da zuwa,
Maryam wace bata san ko may yakawo mahaifin nasu ba acikin wanan daren,
Da sauri ta mike zuwa shimfida mai tabar don ya zauna,
Har zata wuce gurin da take zaune da farko bayan ta gama mai
Muryam baba taji yana cewa dakata samu guri ki zauna, don tafiyar ki ce wanan
Turus tayi waje guda tana mai za,zare idanun ta a lokacin,
Kanta ta sun kuyar kasa har zuwa lokacin da Anty ta ta karaso gurin,
Da ga can gefe guda ta dan samu ta zauna tana mai addua acikin zuciyar ta
A hankali ta daga kai ta kalli yar ta wace ke kokarin zama a kusa da ita
Kanta ta maryam kasa don ganin canzawan da fuskokin su yayi a lokaci guda,
Gyaran murya baba yayi kamar kullun idan har ,ai yi magana mai muhin manci
Ya,soma da adduan koran sheda da kuma fatan alheri a gare su,
Sannan Baba ya soma da cewa dalilin wanan kiran shine don in fadakar daku in fada maku abinda ba,ku sani ba yau,
A hankali maryam wace kanta ke a duke ta dan dago ta kalli su anty da baba, sai kuma ta mayar da kanta a kasa,
Baba yace maryam ina son ki saurare ni da kyau ki ji may zan fada maki akai,
Yaron nan dan gidan yan masuga da kikaturo min iyayyenshi,
Kwanakin da su ka wuce, nace su dan dakance ni akan wani bincike da nake son yi,
Kawai tun ban ai,watar da komai ba sai ga zance daga yar uwar ki cewa wai sun kawo kayan lefen su,
Sai kuma baba yai shiru hakan yasa gurin yai shiru kamar ba kowa agurin, a lokacin,
Ina son ki san cewa maryam duk da ban da komai "ya ta ba yar babyn roba bace haihuwar ki akayi kamar kowa ce "ya, dake garin nan,
Hawayen da yake bin fuskan tane tai kokarin sharewa a lokacin
Maryam baba ya kira ta da wani kakausar murya yace mata
Ina son kamar yadda kuka tsara kawo kayan ku ke da shi to haka kuma zaki, kara sheda mai cewa ya aiko wa yanda ya turo su kwashe mai,
Wani irin kuka maryam tasa mai tsuma zuciya inda baba ya ce kaiyya,
Ta yaro kyau take bata karko,
Wanan yaron da na zaba maki bawai na fasa zancen shi ba ne don kin ji cewa nayi shiru,
Duk wani bincike da uba yakamata yai wa mai bidan diyar shi nasa an min tun tuni akan wanan yaron dan gidan na masuga,,
Gaskiya ba zan iya bada diyata wanan gidan ba sam,
Saboda wasu dalilai, da nagano akan su da kuma kwata kwata ni dai bai min ba,
Kara dan sautin kukan ta tayi a lokacin