Showing 51001 words to 54000 words out of 255288 words

Chapter 18 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1743

na,ura, dake ta shi cikin make,ken falon
Wanda komai da ake bida na hafuwar falo ya hadu,
Jin shirun da wurin yayi zakai tsan manin cewa ba kowa acikin gidan alokacin,
A, hankali yake dan tafita saman walking exercise machine din shi yanayi yana goge dan zufan da ke tsiyayo mai a goshin da wuyan shi,,,
Sanye yake da wani bakin wandon roba har kasa mai dan ratsin fari a gefe, sai, bakar singlet maikama da wondon wanda baida hannu,
Wayan shi sake gefe guda ne tai kara a lokacin badon yaso ba yasauko dan daukar wayan
Anty Dije yagani baro,baro a screm din wayan, shi,
Yai mamaki kwarai da ganin wayar ta da sassafen nan don bata taba kiran shi irin haka ba ,,
Asanin shi madai shine mai kiran Anty din indan har yana da bukatar magana da su,,,
Yana goge zufan jikin shi yana kuma mamakin kiran da safe hakan ga,
Jiran wayan yakeyi ya katse saiya kirata da kan shi don haka yakewa mutane da dama,
Kiran farko Anty dije tadaga wayar anata bangaren,
Cikin dassashiyar murya ta ke mai magana Joseph gamu asibiti da mutumin ka yau two days kenan,
Cikin daga murya ya ce what, Assalam baida lafiya har two days ban sani ba,
Tace wallahi muna ce ko abin baikai haka ba, shine, yasa ban fadama ba,
Yanzu ma shike tace wa wai baigan ka ba shine yasa yana buga ma,
Wai, May ke da munshine Anty, Anty tace yadawo daga school da zazzabi ,
Shine daga baya ya abin ya koma mai combustion, fever,
Cikin matsanacin tsoro da firgici, ya furta O God, da sauki dai yanzu ko, Anty tace eh to yau dai abin bai buga mai ba, gaskiya,
Assalam din ne akabawa wayan cikin dasssashiyar murya irin ta marasa lafiya yake cewa uncle, zan sha Keisha sweet, da apple juice,
Wani iri Joseph din yaji a lokacin don yasan cewa yaron baida lafiya a yadda yaji muryan shi, cikin waya,.

Joseph baisan cewa ya shaku da yaron ba sosai, sai yau din
Don haka, yinin ranan haka yayi shi cikin rashin kuza,ri don ji,ya keyi kamar ace yana agarin shima, a,lokacin don yaga yanauin yaro,,
Gashi yai ta kiran su amma nobar nasu baya shiga,
Sai zuwa dare yasamu layin, nasu, yashiga nan yakara tambayar su ,lafiyan yaro aka ce mai da sauki,,,
Jin haka yai tunane don yasa irin halin hausawa musullumai, duk irin halin da suke ciki sai suce ai da sauki,,,
Don haka ya yanke shawaran tun da safe yakama hanya kawai,
Don haka ya kwana dashirin tafiya, duk wani abinda zai bukata don tafiya yai ready din su,
Karfe shidda na safe ya bar garin Lagos zuwa kwantagora batare da,ya fadawa kowa ba, cewa ga shi tafe,
Ganin cewa tun jiya batai wanka ba yasa ta cewa maryam tazo ta zauna da yaron
Ita zata tafi gida tadan watsa ma jikin ta ruwa ko zataji dadi,
Lafiya lau suka rabu da Anty Dije, Assalam din na saman gado yana,dan wasa da wayan Anty,
Saida zata wuce takarbi wayan a hannun shi, a, lokacin yaron yadan kai kanshi saman filo,
Maryam da hankali ta ke ga wayar ta batasan cewa yaron na cikin wani hali ba,,
Wani irin kakari tayi yaron nayi ashe hakoran shi ne ke hadewa, yana bada wani,irin kara
Cikin matsana cin tsoro da firgici maryam ta mike tsaye, ,da gudu ta kwasa tai hanyar waje cikin rudewa,
Karo tayi da mutum yana kokarin shigowa dakin,
Kamar daga sama ta ganshi tsaye kofar dakin a lokacin ,
Cikin rude take kurma ihu tana ce mai ya mutu, tana nuna inda Assalam yake kwance cikin mawuyacin hali,
Gurin gadon yayi da sauri, ya dago yaron dake ta faman karkadawa,
Daukan shi ya yi din rudewa zuwa office din doctor,
Maryam na bishi a baya cikin wani iri tashin hankali,
Duk saurin da takeyi kamar mai gudu baisa ta cin masu ba,
Karban yaron sukayi suka cewa Joseph ya fito waje, ya tsaya,
Maryam na ganin yafito batare da yatmron ba takaraso da guda tana ce mai ya mutu ko ?
Innalillahi wa,ina alaihi raj,un take ta na,natawa cikin tashin hankali,
Waya ta dauko daga cikin yar pos din hannunta tana kokarin kiran layin Anty Dije,
Joseph wanda tun fitowar shi yake jingine da bangon dakin likitan,.
Fuskan shi murtuk, kamar bai taba farinciki ba, yana mai kallon sama,
Ganin tana kokari kiran layin wayar, Anty Dije ne yasa shi yi mata magana akaro na farko tun zuwan shi,
Yace "pls don't call dem,,
Wani kallo tai mai na baka da hankali,
Daurewa yayi cikin jin haushi yace may zaki ce masu,
Mamakin tambayar da yai mata tayi amma cikin dakewa ,
Tace in fada masu cewa yarasu, mana,
Ido yazoro waje yace waya fada maki cewa ya rasu da zaki fada masu,
Cikin mamaki take kallonshi don sam bata fahince shiba saboda rudewan da tayi,
Fuskan shi a,daure yace mata suna dibashi ne
Shiyasa na fito nan gurin har su gama aikin su,tukun,
Wani irin ajiyar zuciya mai sauti maryam tasake tana mai furta Alhamdullah,
Kafin wanin su yakara wani magana a,ka turo kofan wata yar nurse ce ta miko mai wani takarda tace ance kayi sauri ka sayo wanan,
Cikin sauri Joseph ya wuce sayen maganin sai a lokacin maryam dake tsaye tun dazu cikin tashin hankali takai zaune saman wasu kuherun karfe da akajera akofar dakin likitan,
Jafin yadawo aka fito da yaron zuwa dakin da yake da farko saida da alamar barci yake yi,
Da Joseph zai dawo saigashi da kayan tea manya,manya gwangwani da kuma kayan shaye shaye,
Nan ya zube kayan yadan je bakin gafo gurin yaron yadan dade tsaye yana kallon shi sanan yadan juya inda maryam take yana ce mata,
Idan ya tashi ki hada mai tea mai kauri pls sai a bashi maganin nan,
Zadu dawo zuwa dare sukara mai allura, amma dan Allah ku bashi tea ko kunu yasaha, sosai pls,
Daga nan ya juya yabar dakin cikin tafiyar shi ma kama da ta yanga,
Sai a lokacin maryam ta nisa tana mai kara mamaki da irin rayuwar wanan mutunin,
Allah ya sa yagane gaskiya tace daidai lokacin da tamike ta dan fara gyara kayan da suka wawa,tse adakin,,,,
Sallah tai haraman yi don har lokaci yadan gwauta, bata samu yi ba saboda rudewa,,,
Sai zuwa tara na dare Anty Dije tadawo inda tasamu Maryam zaune gab da Assalam ta kura mai ido,
Tunda tashigo dakin hankalin ta, na gurin su don yadda taga Maryam din a lokacin,
Kayan da tashigo dashi a hannunta taje tana tambayar Maryam maynee, halan naga kin wani kura mai ido
Maimakon Maryam tai magana sai kawai tasa kuka wi,wi,wi,
A rane anty ke kara tambarya ta wai may akayi,
Kuka yaci karfinta takasa magana,balle tai mata bayani,
Jin anturo kofan dakin yasa Anty waigawa don taga kowaye yashigo,
Joseph tagani yana sagale da yar jarket din shi a kafadar shi,.
Cikin mamaki Anty Dije kallon shi sai tambayar shi,take tambayar shi yaushe iso,
Yai yar gajerar murmushi yana kojarin karasawa inda Assalam yake kwance,
Saida yakai bakin gadon yadan taba jikin yaron yaji da sanyi babu zafi kamar dazu,,
Sanan yadan juyo yana gaisawa da Anty dijen, sai alokacin ne ya jai kallon shi ga Maryam wace ke ta faman sharar kwalla,,
Ido yadan zuba mata nadan second, sai yakawar da kanshi daga gareta da sauri,
Azuciyar shi yace dazun ma dayaron ya shiga conscious, batai kuka haka basai yanzu,
Gefen gadon da yaron yake yadan samu gefen bakin gafon yadan zauna
Nan suka fara hira yadda abin yafarawa yaron tun farko,
Yace likita yace, harda typhoid, da kuma malaria ke damun shi,
Maryam wace ta dauro alwalar sallah isha,i, tazo tada sallah duk alokacin suna ta maganar assalam din,
Bayan tabidar ne Anty Dije ke cewa ki hada wanan kayan ki sauri ki je maryam kin san cewa issalam bata yarda dakowa in bake tagani ba
Ga Joseph nan sai ya sauke min ke idan zai wuce,
Gaban maryam ne ya fadi a lokacin don ita sam bata son wani alaka da zai hadata da shi,,
Joseph tashi katafi ka huta ka debo gajiyar hanya,
Anty yatafi kawai zan kira a kaini, yanzu, Anty dije tace Maryam ko da na bargida Issalam fa taki zuwa gidan su Salma,
Da dabara nasamu nakai tacan nasan cewa yanzu haka tana can tana masu rigima
Maryam zatai magana anty tace don Allah tashi ya sauke ki kada dare yakara yi,
Wayan maryam din ne yai kara aloacin cikin murya mai shakewa ta ce, Assalamu Alaikum,
Ido Joseph na akan ta don ya nason subar asibitin don yaje gida kafin maihaifin shi yashiga barci,
Cikin shagwaba taje cewa gata nan zatabar asibitin zuwa gida yanzu,
Tunda suka fara hanya ba wanda yai wa dan uwa magana
Sai shine ma yai dan magana cewa ta danyi hakkuri yasai wani abu a kingays super market,
Batare da yaji maitace ba yabude motar yashige abinshi,
Kara kiranta A,A yakarayi a karo na biyu yana maice mata yana son ya wuce don badadewa zaiyi ba,
Gashi Joseph kuma yasa security lock ya kulle motar don kada sanyi A,C ya rage,
Batare da ta ganshi tafe ba. Dan guntun tsuki tayi daidai lokacin da yabude motar zai shigo,,,
Ledoji ne birjit a hannuwar shi yazube su a gefen shi,
Suna karasawa A,A, natada motar shi daniyar zai wuce abin shi,
Ganin su ya sa yadan dakata sai dai bai san kowakeda qanan dirkekiyar motar ba haka,
A hankali ta sauko daga motar daidai lokacin da shi kuma yafara tatara ledojin da yasiyo a super market yana kokarin bude kofar gefen shi,,,,,
Cikin rawan jiki ta take saurin fita don gudun bacin ran A,A din gareta,
Dan ma,kullin gidan da Anty ta bata dazata wuto take kokarin daukowa daga cikin pos din ta,
Joseph yagane cewa hankalinta na gurin mai motar dake tsaye ya kun,na dim,light din motar,
Da kanshi ya je har bakin kofar gidan yakarbi dan makullin daga hannunta ya bude gidan,
Saida yakai duk kayan da suka dawo dashi daga asibiti zuwa cikin gidan,
Maryam wace har lokacin ta gurin mai motar tadan rankwafa suna magana dashi
Ganin cewa ba,ta,daniya barin gurin mai motar yai mata bayani cewa ga kaya nan tabawa Issilam
Yasa shi tada motar shi yana mai yi muzu horn yai tafiyar shi,
Maryam wace alokacin take cewa A,A, ya daina hadata da kafiri Arne,
Yaga tashin motar shi nan yadan mata dariya cikin barkwanci yake ce mata yau dai na hana shi tsaya wa,
Maryan wace ranta yakai kololowat baci ta wuce zuwa ciki batare da ta,tsaya yi mai saida safe ba,
Shiko A,A da gangan yake mata wanan wasan don yasan cewa tayi hating din Joseph din,
Tun zuwan shi bai hutaba akan ciwon Assalam don duk wani zirga,zirga da sayen magani yakan shi tun zuwan shi
Da har yana cewa zai dauke yaron zuwa Abuja, Turkish hospital,
Saiga shi yaji sauki sosai kamar bashi bane mai ciwo da duk yatayar wa mutane a hankali,


Kuyi hakkuri pls ba yawa yau


ZEEE MAKAWA
[2/20, 10:35 PM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
2⃣3⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA,,,


Wanan watan Azumin haka su,kayi shi rabi badadi saboda ciwon Assalam,
Don bawanda yasa yaron zai tashi, amna sai gashi yasamu sauki,
Joseph duk hankalin shi ya tashi zaka dauka wani babbane ko dan uwan shi baida lafiya, haka,
Da kan shi yake zuwa yai wa Assalam komai daga wanka har shan magani da cin abinci,
Wanan abin yakara sa shakuwa sosai tsakanin Joseph da mutanen gidan,
Don ba wanda ya isa yasa Assalam yin wani abu in ba Joseph ya,zo ba
Duk yadda kayi yaci abu baya ci inba Joseph ya,zo ba sai,kaga jikin shi har dan rawa yakeyi,
Wanan sabon nasu yana bawa kowa mamaki musan ma idan kaga yadda,sukeyi,
Yau ko da ya shi go sun gama abinci don da, wuri suke fara aikin girke, girken su na azumi don gudun makara,
Shimkafa da miya duk maryam taga har ta,zuba acikin cooler wanda har asuba yana da zafin shi,
Don haka ta saurin zuwa yin sallah la,asar, sai jin muryan Anty tayi tana fadin kawo wa su Joseph abincin su,
Ànty sallah zan yi tukun don nayi alwala
, Kifara kawo masu mana kafin kiyi sallah,
Sai jin maganar maryam tayi wani iri, may anty nata ke nufi da fadar haka,
Amma sai tani tana cewa kin san halin Assalam yana iya cewa bazai ci ba sai wani abin kwadai,
Azuciyar maryam ta ce, watau ita don Dan ta take son yin komai akan wanan Arnen
Muryan Joseph taji yans cewa "No, tabar shi kawai bana jin yunwa, Assalam kuma fruit zan bashi ya sha,.
So, abar ta tayi sallah ta, kawai fitama zamuyi yau, mu dan yawata cikin gari
Ya kare zancen yana mai mikawa Assalam hannu,
Tun bayan fitan su gidan bayan maryam takare sallah sai ta share Anty kawai alamar tayi fushi,,,
Basu dawo ba sai bayan shan ruwa daidai lokacin da har da yaya Illiya most jin Anty Dije yana gida don shima yadawo saboda ciwon Assalam din, tun kwana biyu da suka wuce,
Maryam na,ganin shigowar su takara tamke fuskan ta don gudun, kara wahal da ita kan kafiri,
Juice din subo da kankana da akayi mai sanyi yadan kurba,
Daidai lokacin da yaya Illiya ke cewa Maryam, ke bazaki zo ki yi buda bakin ba
A,a ba yanzu zan ci ba inji maryam take cewa mijin yar nata, da yaji tausayin ta a,
lokacin duk da bawai yafaye damuwa da al,marin ta bane a gidan,
Don tun tana yarinya bai damu da mata wasu abubuwa ba a matsayinta na kaunar matashi wace ke zama da su,
Amma ganin watan Azumi ne ga kuma aiki, yai mata yawa har yadan ji tausayin ta ya,kamashi,,
Maryam ko tana cewa ba yanzu ba ta daga idon ta daniyar wucewa sai ki suka hada ido da Joseph,
Wanda ke kurban juice din dake hannun shi a hankali
Ga sanyi ga kuma kamshin dadi na tashi daga cikin juice din,
Suna hada ido tai wani daure fuska, kamar zata fashe, a lokacin,
A, hankali ya furta cewa may yasa ba,zaki ci abinci
Bayan kin yi azumi kada kijawa kan ki matsalar ulcer fa,
Maryam tadan kauda kai gefe guda ta tsuke fuska tace, tace haka kawai,
Tana duke tana kokarin ajewa mijin yar ta vegetable din data soya mai,
Can yai dan shiru ga mamakin maryam sai kuma ta tsinci muryan shi yana cewa amma da ko tea ne ki dan sha don ki walwale hajin ki, ko, ?
Tace ko banci ba yanzu, ba,abin da zai samay don nasaba da hakan,,
Ànty Dije wace tun farkon zancen tajin abinda kewa kana kuma tasan cewa maryam tun rana fushi takeyi da ita,
Anty tace dama kun bar ta tunda tace ba,za,taci ba ,bataci din, ne kawai,
Yaya illiya yakalli matar shi yace kina nufincewa, idan anyi buda baki batayi a lokacin ko may,
Anty Dije tace, a,a yau dai ne takejin hakan , saboda haka duk zancen da zakuyi mata bazataci ba tunda tace a,a,
Yaya illiya yaidan murmushi yace kin,san dai abin da kikai mata yau din ne,
Tace fushin da ba wani dalili takeyi kawai tunda rana,
Dariya mijin Antyn ta yadinga mata, yana mata ba,a cikin zolaya,
Daga haka sukaci gaba da cin abincin su sai kamshi girki ke tashi duk ya cika gurin,
Daidai zata shiga daki wayar ta yai kara, cikin wani irin zakin murya tace Assalamu, Alaikum,
Daga haka tashige abinta daki batare da kowa yakara jin may tace ba
Sai bayan kamar minti goma sha lokacin har anfara kiraye kirayen sallahn isha,i, wasu gurare,
Sai gata cikin wani katon hijab, tace ma Anty Dije, ciki , ciki,
Anty zandan fita nan bakin kifar gida indawo,, Anty dije tace ana shirin yin sallah zaki fita,
Shi bakon wani iri ne daba zai tsaya har a idar da sallah ba,
Takarashe da cewa kada ki dade fa maryam,
Maryam tafita abinta batare da ta,tsaya koda ansawa ba,
Ankai kamar minti goma sai gata tadawo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login