Showing 138001 words to 141000 words out of 255288 words

Chapter 47 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1368

masu sai anjima ta wuce zuwa ciki abinta
Zuciyar ta fam da magana takama hanya, sai muryan Jibrin taji a bayan ta yana cewa tazo ya sauke gida,
Kai ta girgiza acikin murmushin karfin hali tana cewa a,a ka koma gurin ya Yusuf don kada a barshi shi kadai,
Ba musu jibrin ya koma amma Yusuf din yanuna mai cewadan Allah yaje ya kaita kawai ai yaji sauki, ko,
Jibrin yana fitowa ya hango har maryam ta hau mashin sunyi nisa da tafiya ko,
Tsab maryam ta labartawa Anty abin da ya samu Yusuf,
Sai,dai ta boye wa antyn zancen da taji shi da jibrin su na yi,
Saboda ganin Ejoma a guri duk da dai dama bawai fada zatayi ba,
Da su Anty zasu koma sam Maryam taki yarda ta kara bin su,
Don haka ita kadai ce a ka bari a gida lokacin don duk yaran su bi su,
Wanka tayi tai sallah la,asar tare da fara gyara masu gida,
Don daga Anty har maryam basu kaunar ka,zanta sam a rayuwar su,
Shiyasa koda yaushe zaka samu gidan tsab a cikin gyara ga kamshin turaren wuta yana tashi,
Abinci tai masu lafiyayye tuwon farar shinkafa da miyar taushe, yaji busashen kifi,
Har tagama ta sawa kowa a cooler su Anty basu dawo ba sai zuwa yamma suka shigo agajiye,
Take cewa maryam ai Jibrin ne yawuce abinshi bai dawo daukar su ba,,
Taji dadin girki da tasmu maryam ta idar don hakane duk inda zata in har maryam na gida bata shakar komai a fanin girki da sauran harkan kula da gida,
Sai zuwa dare Yusuf yasamu yadan lalaba yashigo garin don ya mike kafar shi,,
Direct gidan Anty dije ya fara zuwa duk da yaso yatafi gidan Abdulsamad akan zancen musuluntar da Ejoma,
Wasu yadine farare masu laushi a jikin don har zaka iya gani yar far singlet din da yasa ta ciki,
Duk da yaramay sai dai har yanzu hasken shi yana nan bai dushe ba,
Yanayin shi kawai zaka kalla kasan cewa bai jin kwarin jikin shi still,
Maryam ce aka umurta da tayi serven din shi a lokacin,
Duk da a rayuwan ta bataso ba don har tana shirin kwanciya a lokacin,
A sanyaye take yin komai yana zaune tare da Assalam suna hira,
Cikin murya irin ta, marasa lafiya yace maryam,
Juyawa tayi a hankali tana kallon su, sai yanzu taga irin yadda ya kara zabgewa da kyau,
Yace may yasa dazun nace kada ki hau mashin kika hau,
Maryam i hate inga mace a saman mashin wallahi,
Baki taturo gaba irin nuna ina ruwan ka to da ni da har zaka samin ido,
Batare da ta kalle shi ba ta ce mota gareni da zan daina hawan mashin,
Ai nima nasan mutunci na kuma har kullun ina kokarin kare kai na,
Cikin sake wani malakacin murmushi yace,
Mota kike so maryam ?
Sai da takalle shi da kyau tace,
Ai don ina yar talakwa ba zan debe rai ga rabo ba ko
Waya san gobe banda Allah,
Kan shi yadafe kamar wanda ya ji ciwo yace,
Ho, ho ho ho maryam wa ya fada maki nufina ke nan,
Da talalka da mai arziki ba duk Allah ne yayi su ba ?
Allah yana ba wa wanda yaso ba don wani dalili ba ,
Yana kuma hanawa wanda yaso ba don wani ya kishi ba,
Sai da ta kau da kai gefe tace,
A wurin wasu ke nan, da sauri ya ce subbahanallah,
Ido ya zuba mata yana mai langabar da kan shi kamar maraya,
Ya ce nidai don Allah alfarma nake nema a gurin ki sam bana son,,,,,,,,
Karasowan Anty Dije ya hana shi karasa zancen nashi,
Zama tayi a can saman dayan kujerar lokacin da maryam ke kokarin tarfa mai man shanu a cikin miyan da ta zuba mai,
Wayar shi tai kara maryam tai sauri daga kai ta dube shi, daga inda take,
Cikin harshen IBO yake magana Abdulsamad ne ke tambayar ko zai samu shigowa
Yadan bashi ansa a ta kaice kawai,
Sai kuma yai shiru yana sauraren shi sai daga bisani ya amsa da to cikin hausa,
Kashe wayan yayi a lokacin maryam na kokarin, barin gurin yace mata atashi lafiya,
Maryam na shiga daki ta samu Ejoma tana kokarin gyara masu gurin kwanciya,
Ce mata tayi ta kwanta kawai ita zata hau kushin kamar jiya,

Kwana biyu tsakani ranan jumma,a aka musuluntar da Ejoma,a cikin massalacin jumma, ta garin kwantagora,
Sosai Anty tai ta aikawa mutane da abin sadakar da sukayi don musuluntar nata,
Kafin marance yayi saiga kungiyar Iyamurai sunyo tsinke zuwa gidan Abdulsamad wai zasu kona,
Su kuma matasan gari sukace wallahi suna sa ma gidan wuta sai sun kashe ko wani IBO dake a garin kuma su kona su,
Saida aka kai su gidan masu gari suka ja masu kunne so sai,
Duk basuga laifin Yusuf ba saboda shi yana da kudi, kuma mahaifin shi nada su,
Abdulsamad bawan Allah suka lekewa kawai, kamar zasu cinye shi danye
Amma shi ko a jikin shi don kawai Allah ya tsawa ba wai wani ba,
Maryam ce ta shirya Ejoma wace yanzu ta koma Na,imat,
Dinkin riga da zani da hijab tasa tare da yin kitso irin na hannin na hausawa, musulmai,
Sosai suka koya mata yadda zatai wanka da sauran abubuwa,
Sai faman washe baki take yi tankar wace akaiwa bushara,
Itama maryam din a cikin wasu koren atamfa super wax take, an masu dinki na half gown, da wani shara sharan gyale da bai hana ganin dinkin nata a fili,
Sai set din wasu dan kunnen na fashion masu kyau da daukan ido,
Ganin bazasu samu shigowa yau ba saboda zirga,zirgan da sukeyi yasa anty cewa takai masu abincin su,
Idan akwai abin da maryam tai hating to wanan aiken don ita aganin ta ai su yakamata suzo su dauka tunda suna da abin hawa, ai
Amma ta ya za,a dinga turata kai ma kato wanda baida mata abinci haka,
Kamar tasan tunanen da maryam keyi sai kawai taji tace mata kutafi da Assalam ko,
Tun daga wajen gidan zaka gane cewa bashi kadai bane a gidan,
Saboda abin hawan dake wajen gidan fiye da guda,
Da sallamar ta tashigo gidan dauke da kulolin abinci masu girma,
Idon su kyam a kan ta har sai da ta dan ji kunyan kallon da suke mata,
Kan ta duke a kunyace ganin yadda suke kallon ta, ta wayance
Yusuf ne yace ke ce tafe da ranan nan maryam karaso mana,
Direct gurin da dining table din tanufa don ta aje kulolin,
Ko may kuma ta tuna sai taja burki ta tsaya wanda hakan yasa shi yin ajiyar zuciya,
Daidai gurin gefen kujerun ta aje kulolin kawai sai ta mike,
Maida kallon ta tayi a kan su tace cikin taushin iji Anty wai akawo maku anan,
KB ne yace tab ai mukn yau sadiya ta cika muna ciki fam da kayan zaki,
Da gagawa Maryam ta mayar da duban ta ga Yusuf,
Wani sanyi maryam taji gwiwar ta yayi da kyat ta dan mike gami da kakaro wani murmushi tace ,
Au ashe ma kun ci abinci Anty ko tana can duk ta damu,
A sake yace mun ci ko sunci ki zuba min pls don ni yanzu nake da niyar zuwa inci a can,
Kamar da gayya Maryam ta cika mai plate dam da abinci da yaji naman rago,
Sai da yadan daga kanshi ya kalle ta ya kalli abincin sai kuma ya mika hannun shi yakarba,
Gurin karba yai kamar hankalin shi na gurin Assalam sai ya hada da hannun ta ya rike,
Cikin sauri maryam taja baya da abincin ya bare mai a jikin shi,
Batai wani dadewa ba tacewa Assalam su tafi amma sai Yusuf ya ce mata
Su jira shi har ya kare cin abinci sai ya sauke su gida da kan shi,
Zamu iya zuwa ai mai mashin na waje yana jiran mu tace mai,
Abincin dake a gaban shi ya ture gefe ya ce mutafi na sauke ku kawai,
Wani kallo maryam tai mai ta tsura mai idanu sai kuma ta mike ta fadin Assalam mutafi,
Tariga kowa fita don shi ya tsaya daukar key sai muryan Jibrin yaji yana cewa
Something is fishing somewhere,,
Kamar ya tsaya yai mai magana cewa bai son haka kada yarinyar ta raina shi,
Sai kuma dai ya sa kai kawai ya wuce don idan ya tsaya zasu iya hawan mashi,
Shi ko sam baya son haka, don bai so ace gurin zuwa gidan shi wani abu ya samu yar mutane,
Duk da yasan cewa biyayya ne kawai ke sa tana daurewa tana mai abu saboda Antyn ta,
A kofar gidan ya samay su tsaye suna jiran shi sai dai fuskanta a cikin damuwa yake,
Gaba take zaune a tare da shi Assalam yana baya zaune yana ta wasan shi,
Murya kasa,kasa yace, may yasa baki fadawa Anty zancen da kikaji muna yi da Jibrin, ba ranan, ?
Saida tadan juyo ta dube shi sai kuma ta juya gurin window motar ta mai da hankalin ta ,
Kamar bazata bashi amsa ba sai can tace, saboda maganar bai shafe ni ba,
Kuma ban san ko may ke faruwa ba sai kawai in sa kaina aciki,
Wani irin hucin iska mai zafi ya furzar da ga bakin shi,
Yadan daki sitiyarin mota da hannun shi sai kuma ya numfasa,
Daga haka bai kara cewa komai ba har zuwa lokacin da suka tsaida motar su kofar gidan,,,,,





ZEEE MAKAWA
[3/24, 2:22 PM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
5⃣8⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

Allah ya karawa Annabi daraja,
Ya Allah ka daukaka musulunci
Ya Allah ka sa mudace da Rahaman ka,
πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘


Duk yadda mutum ke tsan mani hankalin yan church ys tashi sosai,
Hakan yasa suka mai da hankali sosai wurin jawu hankalin mutanen su da cusa masu ra,ayi
Daga can gurin shugaban nin su sai suke ganin cewa ai wani sakacine da dama mutanen suka bayar,
Shugaban Catholic churches gaba daya na kasa ne da kan shi ya sauka garin na kwantagora,
Sai da ya je gurin maimartaba ya kai gaisuwa
Inda ka basu dokoki kamar yadda ake wa kowani irin shigaba na addini don gudun tayar da tanzo ma ko wani tashin hankali,
Bayan sun koma church ne suka zaune yin mintun din su na shuga ban nin su,
Idan zakaji irin kudin da suka ajewa jama,an kasar ta kwantagora da kewayen ta sai mutun yai mamaki sosai,
Badon komai ba sai don kawai su ja ra,ayin masu raunin ima zuwa gare su,
Da kuma wa yan da ake ganin cewa sun karkata ne kila don talauci, zuwa cikin musulunci,
Sunyi rabon mashi,mashin da ke kuna hawa da na dinki ga mutanen kawai
Inda hankalin mutane sosai ya irin wa yanda basu da addini suka dinga shiga kungiyar su,
Father da kan shi ya shirya yadda za,a tunkari Yusuf, da Abdulsamad,
Yana zaune a cikin office din shi yana breakfast,
Cup ne mai dauke da ruwan shayi masu zafi yake korawa a hankali,
Don shi al,adar shi ce,shan tea mai zafi har ya dan kona baki,
Amma shi agare shi saboda sabo da zama kasar America yasa bai jin zafin
Dan tiririn ruwan na tashi saman cup din yana yi sama,
Yayin da sanyin AC ya gauraye office din duk safiya ce yanzu rana bawai wani yi,
Sakatariyar office din shi ce ta shigo da sallamar ta ,
Kallon ta yayi da cup din tea din shi a hannu ya ce, yadai Helen,?
Cikin dan rusun nawa tace boss kayi baki fa ,
Haka kawai yaji gaban shi ya ba da damm, to wasu baki yanzu zasu zo mai a wanan lokacin kuma baida appointment da su,
Sai kuma zuciyar shi ta nasa mai cewa kila wasu masu bukatar wani abune,
Yace wa Helena tace su shigo,
Helen tace da har na ce su koma kawai tunda basu da appointment da kai,
Don na lura ba harkan business bane ya kawo su don sun min kama da masu preaching,
Wani tsawa yadaka mata ya katse mata dogon zancen da take ja dashi,
Ya ce ki ce su shigo nace maki
Umurni na baki ba wai uzuri ba pls, ki kawo min ba , bayan kin fada masu cewa ina ciki ko,
Don su ga na yi masu wulakanci na hana su gane ni ko,?
A yadda Yusuf yai maganar cikkn tsaw yasa Helena, jin tsoro, da sauri ta fita zuwa yiwa bakin iso,
Ba ai wani bata lokaci ba sai gata da bakin sun shigo a tare tana masu iso,
Yana kokari a je cup din tea din shi a lokacin suka hada ido da Peter wani class mate din shi tun primary a kwantagora,
Yanzu Peter yana aikin banki ne a Enugu, amma dai iyayen shi suna zaune still a nan northern Nigeria,
Sai kuma wasu mutun biyu da yake ganin kamar ya san su a da can,
Yai masu sannu da zuwa duk da bai san abin da ya kawo su gurin shi ba,
Yace wa Helena ta kawo masu abin sha, inda ya nuna masu gurin zama,
Bayan sun zauna sai gaisawa ya biyo baya inda suke ta yiwa juna ya bayan rabo,
Ganin yadda Yusuf ya koma kawai yasa suka ga yai masu wani irin kwarjini a fuska,
Saidai ya lura da cewa daga cikin su ba wanda ya sha drinks din da aka aje masu a gaban su,
Sai da suka natsu Yusuf ya juyo yana fuskantar in a serious face ya ce lafiya dai, ko nagan haka,?
kafin su yi magana sai wani daga cikin su ya fara jero addu,oi kamar yadda sukeyi a koda yaushe,
Ameen din da suke fada shima shi yake fada tunda duk addua ce ai,
Ganin yana karba masu yasa suka dan samu karfin gwiwa, kokarin fuskantar shi,
Saida suka gama wanda yafi shekaru a cikin su ne yafara magana da cewa,
YUSUF munzo ne don mu fuskanci juna da kai akan juyawa Jesus crisis baya dakayi,
Munzo ne on behalf of our members,na Catholic churches, don mu baka hakkuri akan duk wani abin da mukai maka har ka canza, religion din ka,
Yusuf ya girgiza kan shi yana cewa ni ba kumin komai ba kawai don na gano cewa Islam itace hanya madaidaiciya,
Kunga yanzu dai nakai munzalin da idan ina ra,ayin abu zanyi don kai na kawai,
Ido suka tsura mashi gaba dayan su suna sauraren shi,
Yaci gaba da cewa ban shiga cikin Islam ba sai da na tabbatar da na samu kwakawaran hujan da zan kafa wanda har yajani zuwa, cikin ta
Ni ban shiga don wani ko wata ko kuma don kwadan wani abu ba, kawai don ra,ayin kaina nashiga,
Mikewa wanda Yusuf yakira da Peter, yayi har zuwa gaban Yusuf din yadan dafa tebur din suna fuskantar juna, inda yace mai
Look Joe, daga million daya har zuwa goma zamu iya baka don kawai kadawo ma addinkn ka daka bari,,
Cikin wani murya mai kama da tsawa Yusuf yace mai ,
Na fada ma cewa badon wani abu nashiga wanan addinin nawa ba kawai sai don irin hujjojin da nake dasu akai,
Mikewa yayi zuwa wajen wani serve dake a cikin office din inda yasa wasu nombobi gurin ya bude,
Kudi ne sabbi kar ya kwaso yakawo masu gaban su wanda kallon su kawai zai sa mutun yasan cewa sunkai miliyoyi,
Yace bani bukatar kudin ko kowani abu kawai don tsira da rayuwata nashiga wanan addinin
Yakare zancen yana mai tura masu kudin a gaban su lokaci guda,
Wanan ya kalli wanan wancan ya kalli wancan,
Jiki ba kwari suka mike tsaye saboda sun san cewa sam ba riba akai,
Har sunkai kusan kofa Yusuf yakira sunan Peter yana mai ce mai i,hope for daga haka kun rabu dani kenan pls,
Ya hada hannayen shi guri daya alamar yana rokon su da sufita harkan shi pls,
Ba wanda ya kara ko juyowa suka sa kai zuwa hanyar fita,
Zuka tan su cushe da bakin ciki saboda sun san cewa sun rasa Joe din ke nan har abada daga cikin su,
Gashi kuma yayi nisa ta yadda basu iya jan ra,ayin shi ba sam,
Wani irin tsaki ya ja yace batatu kawai,
Sai bayan fitar su ne

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login