Showing 42001 words to 45000 words out of 255288 words
Chapter 15 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete
ashe,
Kai kawai ya gyada mai alamar eh, a hankali ya furta may ye amfanin hawar mashi a diya mace pls,
Maryam ko rana isa gida ta samu anty tasayo zogala, ai cikin murna ta shiga sallah kawai ta idar tafito waje don ta gyara masu zogalar,
Bayan ta yanka su albasa, da attarudu da tatasai sai man kulikuli da ta lema masu asaman takawo garin kulikulin ta cakude wuri guda sai ruwa mai sanyi da ta dauko,
Da shikafa tai niyar zubawa taci bayan ta debi daidai zamar ta asaman wani tabarma da ta shimfida don ta ci gwaben ganyen, da tayi,
Shigowar su ,suma ke nan a gidan, inda, jibrin ke gaba, wani lawal na binsa, sai Joseph tare da wani tajudeen a baya,
Shigowar ya fara rage mata dokin da takeyi nashirin cin ganyen da tayi,
Jibrin ne da shigowar su , yadan kalli inda maryam take zaune yace mata,
Ke ashe har dadi kuke ji indan kun hau irin wanan mashin din dake kusan tashi sama da ku,,,
Baki kawai maryam ta hangame cikin mamaki da maganar jibrin,
Saidai taso ta furta cewa wani abu amma sai ta kasa, cewa komai don wani irin al,ajibi jin maganar da tayi,
Don dai ita tasan cewa ba gwanar hawa mashin bace ko banza
Yau ne kawai da take kokarin ganin cewa ta iso gida da,wuri don ranan da yai yawa a garin,
Ji tayi wasu hawaye masu dumi sun gangaro mata a fuskan ta, ga wani malolon bakin ciki da ya tokare mata makogoronta,
Takai wani dan lokaci a gurin zaune takasa tashi,
Saidai tana kiyasta irin daukar da sukai mata a matsayin yar iska kenan ko,
Bataji zuwan Joseph da Assalam inda take zaune tana hawaye ba,, sai ganin shi tayi gaban ta,
A hankali ya sauka bisa gwiwowinsa, yace little mummy kiyi hakuri amma gaskiya jibrin ya fada maki,
Banza tayi da shi sai kuma wani wawan harara da ta sakar mai, har Assalam saida ya dan ji tsoro ya dan shige jikin Joseph,,
A raunane ya kara cewa kiyi hakkuri wanan ba abin bata rai bane,
Kala batace mai ba sai mikewa da tayi tsam ta nufi kofar da sauri,,,,
Ido yabita, da shi don dai shi baiga abin bata rai aciki ba,,,,,,,,,
ZEEEE MAKAWA,
[2/20, 10:26 PM] +234 806 595 8685: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
1⃣9⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA,,,
Buki sosai akayi a wanan bukin hawan Dabar da akayi don matasa masu ji da lokacin su sun halarci wanan bukin nadaukaka masarautar kasa kwantagora
Wanda ke tatare,da tsohon tarihi acikin ta kamar sauran manyar masauratar da ke a kasa shen hausa,
Anbuga a jaridu da kuma sauran kafafen yada labarai, na kasa,,
Inda bukin yasamu karbuwa fiye da zaton may karatu,
Ana gama wanan bukin da kwana biyu Joseph yabar garin kwantagora , saboda gudun fushin mahaifin shi da yasan cewa yana hake dashi,
Duk irin abubuwan da ya wakana agurin duk Mr Emanuel nada labarin komai tankar a gaban shi akayi, duk shagallalikukan
Don haka joseph ko kasan bai tsaya ba ketarawa yayi zuwa kasashen waje da niyar yatafi, yadan huta a can,
Tun bayan wanan abubuwar, maryam babu ruwanta da zancen, wani wasan da akayi
Wanda ita take gani kamar duk wanan abin bai cikin irin tsarin rayuwar ta,,
Ita bata masan cewa masu takura masu a gida, basu garin ba tun bayan bukin da gari yayi kamar zai tsage, don cinkoson jama,a
Don ganin da su tun zancen da suka ce ta hau mashi a na gudu da ita kamar wace bata san zafin kanta ,
Ita ko a nata zaton gani takeyi kamar suna ganin cewa bata san darajan kanta ba ne tunda har take hawan mashin da na miji,
Idan har ta tuna da wanan kalamin sai taji duk yanayin ta ya sauya,,
Saboda ba karamin ci mata fuska take ganun sun yi ba,
Takan yi tsuki tace wai gwano baya jin warin sa, su da suke hurda da yan iskan yan mata
Shine har zasu samata kazafi akan hawa mashi, idan bata hau mashin ba da may zatai tafiya to,,,
Wata rana da la,asar bayan Maryam ta dawo daga wani gida da anty ta aiketa karbo, mata sakon wasu kaya da aka turo mata ta daga kano,gurin wata mata,,
Don yanzu Anty tana dan taba business irin da matan gida ke dan yi,
Domin kariyar mutuncin su saboda hana, bani bani gurin maigida,
Wani mutum tagani dattijo zaune a kofar gidan su, tun daga nesa take kallon mutumin a cikin mamaki, saboda ganin shi da tayi gab da kofar gidan su,,
Saboda a gaskiya bata taba sanin shi acikin masu zuwa gidan su ba,
Koda kuwa gurin mijin yar ta ne, bai daga cikin masu zuwa gidan,,, sam,
Gashi kuma kaman nin sa sun nuna cewa kamar yana tare da lalura,,,
Tafiya take yi a hankali, cikin dan shakku,kamar za,a kamata,
Tana karasowa gab inda mutumin ke zaune sai mutumin ya mike tsaye da sauri ganin cewa gidan maryam ta dosa a lokacin,
Cikin dan tsoro da kuma ladabi maryam ta dan duka kadan tace Baba ina wuni, ?
Yace yauwa "ya ta lafiya kalau,
Dan Allah ko gidan nan kike yan mata, ?
Maryam dake dan ja baya baya kadan da kamar tace mai a,a sai dai ta daure tace mai eh a nan take,
Hausar shi na nuna mata cewa mutumin ba pure hausa ba ne,
Ya ce dan Allah yan mata ina son ki min iso a gurin mai gidan nan,
Cikin mamaki Maryam ke kallon shi tace mai baya gari,
Shiru taga mutumin yayi cikin damuwa yana mai dan ya mutse fuskan shi,,sai kuma taji duk yaba ta tausayi,
Ita a zaton ta ko yazo maula ne irin yadda wasu masu kararen zuciya ke yi a wanan zamanin,
Kaga mutum majiyi karfi amma sai ya kare bi gida jen masu hannu da shuni yana maula,.
Mutumin ya katse maryam da cewa ko zan samu ganin hajiyar gidan don magana ce tazo dani mai muhin manci sosai
Shiru Maryam tayi saidai gaskiya mutumi yabata tausayi sosai don ganin yanayin shi,
Marayam ta fadi cikin ladabi barin shiga in fada mata,
Bayan shigar ta da kaman yan mintina saiga Anty Dije ta leko sanye da hijabin ta,,
Daga nisa kadan suka dan gaisa da mutumin sai kuma yar shiru tabiyo baya,
Don Allah hajiya kiyi hakkuri pa don nasan cewa ba wai kin san,ni bane,,,
Sunana Abdullsamad anan gari nake, ni dan uwan yaron dake yawan zuwa gidan nan ne,
Watau Joseph,,,,,
Daga Anty Dije har maryam dake ta kofa tsaye wace ta takawa yar uwar ta baya don gudun wani abu ya samay ta,
Sai da suka dan kadu jin mutumin ya ambaci sunan Joseph,
Jin haka yasa anty ta dan kara gyara tsayuwar ta tana mai cewa lafiya dai ko malam,
Don a zaton su yazo masu da wani tashin hankali ne, a yadda suka gan shi,,,
Yadan hada hannun shi guri daya ya nuna alamar cewa a,a babu komai gaskiya sai Alheri,
Sai a lokacin anty dije tadan rage jin abinda take ji
Sai yadan waiga kamar may son yin wani maganar ta,siri ko kuma mai muhin manci sosai,
Hakan yaba anty damar gane cewa maganar da yake da ita kamar ta siri ce,
Don haka ba bata lokaci ta dibi inda Maryam take tsaye tun farkon fitowar su tace maryam bude mai kofar falo tukun,,,
Bayan an bude mai yadan shigo daga cikin ya zauna maryam takawo mai ruwa sanyi tare da dan abin tabawa,
Ya dauki yar ledar ruwan goje water da ta aje mai ga plate ya dan tsosa kadan yace Alhamdullah,
Nagode da wanan ruwan da kuka shayar dani Alkah yakara budi da daukaka,
Daga Maryam har Anty sunji dadi sosai da wanan kalamin tashi,
Hakan yakara basu damar sake jiki dashi don dama darrrr suke dashi saboda rashin sani ko da may yazo,
Sai maryam taji kawai mutumin ya kwanta mata arai,, saboda kalaman bakin shi na alheri ne,
Saboda ta lura cewa yana da addini atare da shi ,
Tsabar talauci ne kawai ke damun shi ya koma haka
Wani irin mugun tausayin bawan Allah sukaji cikin lokaci guda,
Maryam sai tunane take yi a ranta cewa,ashe daman wanan mutumin yana da yan uwa musulumai,,,
Maganar bakon ne ya katse ta, da cewa, dan Allah kuyi hakuri nazo maku a bazata, tare da kuma bakon al,amari,
Dama taimako da kuma shawara ne nakawo maku, akan cewa,
Wanan yaron da ke zuwa gidan ku Joseph don Allah tunda har naku yazo daya dashi ina son ku dan tallafa mai ,
Nan da nan daga Anty har maryam suka dan kali junar su,
Suna mamaki har may zasu iya tallafawa Joseph dashi su,,,
Ai kuma sai mutumin yai shiru ,alamar maganar da zai furta tana da nauyi,
Zuwa wani dan lokaci kamar mai tuna ne,,,,,,
Can kuma sai yace, ku yi mai tayin musulunci a hankali pls,
Yafadi cikin taushin murya,
Duk da dai nasan cewa abune mawuyaci , amma nasan cewa zaku iya insha Allah,,,,
Yakara fadi a raunane, cikin nuna damuwa sosai a fuskan shi,
Shiru wurin yayi daga anty har Maryam dake tsaye kamar mai wancin gadin, yar uwar nata, Saida maryam takai zaune a gefen hannun kujera, dake kusa da ita,
Saida Anty tadan nisa sai tadan daga kai zuwa kallon malam,Abdull samad tace
A gaskiya malam kazo muna da mawuya cin abu amma da ace mai gida na yana gari ne kaga sai kuyi magana dashi ta yadda za,a fahinta,
Katseta yayi dace wa ai koku da yake, zama daku a hankali zaku iya dan jan ra,ayin sa don dai yana da bukatar haka din
Idan har kunyi la,akari da yadda rayuwan shi take,,
Yakare zance shi da cewa ina fatan Allah ya baku sa,a
Gaba dayan su alokaci guda suka ansa da Ameen ya Allah,,,
Basu tashiba saida malam Abdullsamad ya basu labarin dalilin musuluntar shi, da kuma irin kalubalin da har gobe yake samu, daga mutanen shi nada,,,watau Christian,
Yace musam man mahaifin Joseph da yafi kowa son kuntata mai,
Saida duk kan su, suka tausaya ma halin da rayuwar ya shiga sukai mai fatan gamawa da duniya lafiya,,
Anan yai masu sallama ,akan cewa idan maigidan yadawo zai zo sukara,tataunawa da shi akan zancen Joseph din In sha Allah,,,,
Da zai tafi Anty Dije ta kawo dubu daya tabashi tace ya hau mashi zuwa gida
Yai ta sa mata albarka yana ta godiya kamar wanda,taba wani abu mai yawa,
Tun fitar wanan bawan Allah, duk sai jikin su,yai sanyi lokaci guda tankar, an aiko masu da wani labari, mai kashe jiki, duk su kai shiru zuwa wani dan lokaci,,,
Kowa da abinda yake sakawa acikin zuciyar shi akan zancen,,,,,,,,
Barci takeyi amma sai juyi takeyi kamar wace aka danne ta daga saman ta,
Sai shure shure take yi da kafarta kamar mai bidan ceto,
Zubur ta samu ta mike tana mai kumar ihu cikin wani irin karaji tace, JUSES crisis,,,,
JOSEPH,,,,, tafadi da karfi tana mai dafe, kirjin ta,
Guda guda take mai da numfashin ta sai wani irin zufa da takeyi kamar wace ke cikin ovon
Wanan mafarki yana damun ta sosai yanzu,
Har takai yanzu sam bata son tai barci asuba saboda , da wuya tai barci a wanan lokacin batai mafarkin nan ba,
Still masu farin kayan da take gani suna kokari jan Joseph din cikin korarayen haki,, ko yaushe yau,ma su din ne dai tagani, suna ta kokarin jan shi,,,,
Sai,dai ta yau mafarkin nata yadan bam,bamta dana kullun,
Don dai yau,taga Joseph sosai a cikin mutanen,,,,
Tana bin shi ta kamo shi amma sai ya kubce daga rikon da tai mai, shine mafarin wanan shure shuren da take ta yi, a lokacin da take mafarkin,
Bible din ta dake gefe tadauko ta gyara daura dankwalin ta da kyau, nan ta fara jefo addu,oi da tasaba yi kamar kullun, har zuwa wani lokaci,,,,
Koda gari ya waye ranan sai ya kasance mama choima ta kasa sake jikin ta sam bata walwala, yau,
Duk abin duniya yadamay ta akan dan jikan na,ta
Tsoro take ji don tasan cewa akwai abin da zai sami Joseph din,
Saidai ta rasa ko may wanan mafarkin ke nufi, haka nan,
Ejoma ta lura da cewa yau mama tana cikin wani yanayi don ko yaron Ejoma da take kokarin rike mata yau sam bata ko kalle shi ba,
Inda take zaune tayi tagumi, Ejoma tazo tazauna gefen ta,
A hankali Ejoma ke kallon mama, sai can tace,
Mama yau may ke damun ki ne, wai ? da naga baki walwala, sam,
Kamar kada ta fadawa Ejoma wanan maganar,
Sai,dai kuma ta fara ba Ejoma labarin tun fara mafalkin nata akan Joseph din,,,
Da irin yanayi da take ganin ahi a ciki yanzu,,
Ejoma,tadan kwan,tar wa mama da hankali ta dan dafa kafadar mama kadan tace
Kinsan cewa shi mutum ne mai harka da mutane kala,kala, mama,
Don haka dole,
yasa ko da yaushe kike ganin shi tare da irin wa yan nan mutane,,
Har wani lokaci Ejoma da mama Choima suna zaune suna zancen duk akan Joseph din,
Joseph din ne ya bugo masu waya yana tambayar lafiyar su,
Anan mama tashiga tambayar shi labarin yaya yake can ya kuma aiyukan shi,,
Inda yake kara mata karfin gwiwar da cewa yana tafe kwanan nan,
Amma ita sam bata,yarda da zancen shi ba, don har yanzu idon ta na hasko mata masu fararen kayan da suka rike mai hannu suka wuce da shi tana ta kurma ihu,a daji,,,,
Shiko Joseph yanzu yakai kusan wata, hudu a can
Har kasar chaina, yake tare da wani abokin karatun shi,
Cikin dan kankanin lokaci mr Sonny, da suke tare ya dan kara gwada mai wasu yan dabarun kasuwan ci,
Allah da ikon shi ya kara daukaka shi sosai, ga harkan business,
Ga harkokin shi na Nigeria su ma suna ci gaba,
A, sannu yasamu ya kulla, a,laka da wayan nan mutanen suka yarda zasu zo Nigeria su kafa irin wanan masana,antar,
Wanan harkan duk ya,samay shi da ga taimakon da hamshakin maikudi a kasar IBO yai mai hanya, abokin karatun shi
Wanda tun kare karatun su shi yana can zaune yana harkokin shi, da turawa da chainawa,
Mr Sonny shine ya basu sunar Joseph saboda yabawa da hankalin shi da yayi,
Don tun a can da yasan halin Joseph sosai da rikon amana,
Abin mamaki,Joseph nadawowa,da wanan harkan,
Saiga shi ya dauki yaran hausawa cikin ma, aikatar company da aka bude Bunue,watau makurdi, wanda su yan kabilar su sam basu so hakan ba,
A, bangaren su maryam da Anty dije kuwa,
Tun bayan tafiyar wanan tsohon sai maganar tazauna ma maryam a zuciyar ta
Tunane takeyi ta yadda zata fara aiwatar da wanan shirin kamar yadda aka basu shawara, su tallafa mai,
Don haka tasawa zuciyar ta cewa zata bada nata gudun mawar amma ba tare da sanin kowa ba,,
Don haka shiri na farko da tafara yi shi sayen sabon sim card na layin,MTN,
Sabanin wanda kowa yasan ta dashi a da tana amfani dashi,
A cikin wayar anty Dije ta samu nobar wayan shi tai serving a sim din ta,,,
A wani dare bayan ta gama komai tana shirin kwanciya ne
Sai zance malam Abdulsamad yafado mata arai,
Tashi tayi tsam daga inda take kwance,ta dauko wayanta,
Ta rasa may zata rubuta da farko,sai can wanan
Sakon farko da tafara tuwa shine,
Come to the light of life, islam,,,,,
Joseph dake zaune yana searching din wasu kaya a cikin laptop din shi yaji sako ya shigo mai a wayar shi,,
Kamar ya share kada ya karanta saidai ya mika hannun shi yadauko wayar, a hankali,
Da niyar,yadan diba sakon yaci gaba da aikin shi,
Sosai yai mamakin ganin wanan sakon awayar shi batare kuma da da sanin mai nobar ba,, Nan da nan duk wani abin da ke gaban shi ya dushe mai,
Kafin wani lokaci idon shi ya kada yai jajir kamar yaci gauta ja,
A hankali ya runtse idon shi, yana sauke numfashi a hankali, ya fida wani huci ta bakin shi,
Tsayin lokaci babu abin da ya iya yi ko tunawa, wayar ya kara dauka ya diba sakon,
Ahankali, maganar mahaifinshi ya fado mai a rai,
Inda yake yawan ce mai hausawa basu da