Showing 141001 words to 144000 words out of 255288 words
Chapter 48 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete
yadaga hannu yanawa Allah godiya da irin baiwar da yai mai ga ta addini ga kuma dukiya,
Sonny ne yafado mai arai inda yaiwa Sonny din adduan shima Allah ya sa ya gane gaskiya,
Ashe har da Abdulsamad sun ziyarta inda yai masu kaca kaca da cewa kada su kara tuna shi daga cikin su,
Sai dai Ejoma ce basu san inda take ba har yanzu tukun,,,
Tun bayan tafiyar Yusuf maganar ta tsayawa maryam arai so sai,
Sai dai kuma ta rasa hanyar da zata fadawa antyn ta cewa ga halin da ake ciki a zancen,
Da bara ce ta fado mata na ta ba wa Anty shawaran zuwa dubo Sadiya din,
Suna zaune a tsakar gida tana,wasa da Abubakar din Anty,
Sai ga kiran yusuf ya ahigo a wayar Anty Dije sun kai wani lokaci dashi su na dan hira,
Inda yake sheda mata cewa ya je gurin ya Iliya mijin Anty yace zai shigo kafin Azumi,
Tai mamakin jin cewa ya tafi gurin shi nan yake sheda mata cewa akwai wasu kayan su da za,a shigo da su sune yaje yin clearing,
Nan yake tambayar lafiyan su Assalam da sauran su amma dai bai tambayi maryam ba,
Itama dai anty sam bata dauki wanan a bakin komai ba ,
Sai zuwa dan lokaci da kare wayan na su ne maryam take cewa Antyn ta
Gaskiya Anty yakamata mu tafi gidan Sadiya mu diba ta kada tace ba ki taba zuwa,
Haka dai tai ta cusawa Anty Dije ra,ayi har dai daga karshe ta amince da cewa zasu, tafi su uku da yara,
Bayan kwana biyu da zancen shiri sosai sukayi i dan ka gansu zaka zata wani guri can zasu,
Ashe wai duk shirin zuwa duban budurwan Yusuf ce,
Kai su akayi a,cikin wata motar da maigidan Anty ya saya ya barta a gida,
Sadiya tana zaune tare da wasu kan,nenta suka kallon tv a dakin mahaifiyar, su,
Suka ji sallaman mutane, kallon su suke yi a cikin rashin sani,
Sadiya din ce tagane su ta ganin Assalam a cikin su,
Nan aka shiga gaisawa a tsakani inda Sadiya din ke nuna yar jin kunya, a tsakani,
Mahaifiyar ta tasa aka kawo masu kunun zaki mai sanyi yaji kayan kamshi sai tashi yakeyi a ciki,
Maryam sai kallon gidan takeyi irin kallon kwam din nan,
Bayan fitar mahaifiyar sadiya da kannen ta ne, suka dan kara gaisawa da Anty
Inda Anty kewa Sadiya kewar Yusuf, din ?
Jin maganar Sadiya tayi kamar don zolaya suka zo mata,
Amma kuma, sai ta tuna da yadda Yusuf ke fada mata halaiyar Anty dakuma irin yadda take son alakar su,
Dago kai tayi tanawa Abubakar dake hannunta wasa,
Sai kuma ta sauke kan ta cikin kwantar da murya tace
Anty Yusuf bai fada maki yana fushi dani bane aiko da ya wuce bamuyi sallama da shi ba,
Kuma nai ta kiran wayan shi bai daga wa,
Nan da nan an nurin fuskan Anty Dije ya sauya lokaci guda,
Cikin damuwa anty ke tambayar sadiya abin da ke faruwa,
Bata boye mata komai ba na yadda kanin mahaifin ta yaiwa Yusuf din daren da yazo zance gurin ta,
Na,imat ba tasan lokacin da tasa kuka ba alokacin,
Tana cewa abin da mutanen su ke yawan fadi ke nan cewa koda Christian ya musulunta gori da hattara da musulumai zasu dinga mai har sai yafi na lokacin da bai shiga cikkn su ba, zΓ fi da ciwo,
Nan kuma hankalin su yakara tashi ganin yadda Na,imat ke fidda hawaye,
Abu ya taru lokaci guda yai wa Anty Dije yawa, tarasa da,wani zataji,
Sai,da suka samu Naimat (Ejoma) tai shiru san nan suka fara magana,
Maryam na zaune a gefe tai shiru tun da akafara zancen ta na mai jin zafin irin kalamin da aka ta jefawa Yusuf din,
Sadiya ki yi hakkuri zan kirashi in ji may ke faruwa ne ai bai kamata yai saurin fushi ba haka,
Mahaifiyar ta wace itace yar uwan Jibrin din tashigo dakin
Inda take kara fada masu halin kanin mahaifin nasu dan cin mutunci,
Tun a hanya Anty Dije ke ta zabga wa maryam godiya don badon ita da takawo shawaran zuwa diban Sadiyar ba da ba zasu san abin da ke nan ba,,
Cikin ikon Allah ranan Yusuf bai kira anty ba sam tankar yasan da zancen,
Ita ko Na,imat duk hankalin ta ya tashi saboda ji takeyi kawai ta zauna a cikkn yan uwan ta zaifi mata
Kada sai sunyi aure da Ibrahim irin wanan gorin ya biyo baya,
Ji tayi an dafa mata kafada
A hankali ta juya don ganin kowaye maryam ce ke mata murmushi,
A hankali maryam ta zagayo in da Na,imat din take zaune,
Saman hannun kushin din ta zauna a hankali maryam tace
Na imat kada ki sa komai a rayuwan ki pls saboda dama kin san sai an samu irin wanan challenges din,
Saboda wasu basu da tauhidi atare da su just dai suna ansa sunan su musulmai ne kawai,
Ki sani cewa Ibrahim dai kabilar ku guda dashi kin ga ke nan wanan irin challenges din zai zo maki da sauki,
Unlike na ya Yusuf wanda in dai ba haushe mutun ne koda ace shi ya Yusuf din a cikjn musulunci aka haife shi,
Zaman shi na dan kabilar ibo ko bayerabe sai sunyi suka akai,
Kai koma da ace yaren da ke anan cikin arewa ne tare da mu,
Kawai ke dai imani azuciya take ba,a baki ba,
Don haka duk wani tunane ki daina kawai ki sa Allah a gaba kin ji sister,
Kai Naimat ta daga alamar gamsuwa da zancen maryam din duk da tagirmay ma maryam din sosai amma dai yarinyar na bala,in bata shawa saboda irin halaiyar ta,
Ga kuma irin yadda ita da yar ta suke kokarin koya mata addini akoda yaushe acikin sauki,
Sai washe gari ya kira Anty Dije tun daga maganar ta yagane cew akwai matsala don ba haka take mai ba idan suna waya,
Antyna lafiya kuke kuwa naji muryan ki wani iri kamar ba dadi yau azuciyar ki
Anty Dije ce ta katse shi da cewa Yusuf may ke faruwa a tsakanin ka da Sadiya ne ?
Shiru yayi na dan wani lokaci sai kuma can yace tazo gurin ki ne,
Anty Dije bata boye mai komai ba tafada mai yadda maryam taga cewa ya kamata suje su kai mata ziyara,
Nandai ta bashi duk wani bayanin da yadace tai mai alokacin,
Tsawon wani dan lokaci bai yi magana ba sai zuwa can yace,
Γnty Dije gaskiya bazan boye maki ba bazan iya auren Sadiya ba kuma yanzu,
Saboda ko munyi aure za,a samu matsala sosai, daga yan uwan ta,
Katse shi tayi da cewa kai Yusuf yan uwanta zaka aura kodai ita,
? ,
Murmushi yayi kawai yace bazaki gane bane anty kawai abar wanan zancen zai fi,
Yusuf ko da sunyi challenge din ka ne ai ba yarinyar bace tayi ko ?
Zan dai kira ki anty yanzu zan tafi sallah lokaci yayi, pls,,,
Saida ya idar da sallah shi sanan ya kira layin maryam
Maryam wace a lokacin tana daki zaune ta idar da salla itama saboda time akwai dan tazara tsakanin yadda ake sallah a kwantagira da Abuja,
Cikin mamakin ganin layin Yusuf na kiran ta, ta mika hannu akai ta dau ko wayan,
Da muryan nan nata zakwaikwai ta,ansa sallamar tashi,
Gaisuwa ta fara yi mai tana mai kara wayar a,kunnen ta,
Sunan ta yakira cikin wani irin muryan nan cikin golden voice,
Maryam ta amsa da na,am
Yace may ye hikimar ki na kai anty gidan su sadiya pls ?
Shiru tayi kamar bazata ce mai komai ba,
Wani irin nauyi da kunya ne ya lullubeta don may anty zata bari yasan cewa itace ta bada shawaran a,tafi gidan su sadiya,
Karo na biyu ya kara kiran sunan ta cikin wani soft voice da yafi na farko taushi,
Yace kina ji na pls karki boye min komai akai, ki fada min dan Allah,?
Sani sanyi taji don ya hada ta da Allah akai,
Nan take ce mai ya Yusuf a gaskiya dai ka san cewa mutumin bai kyauta maka ba ko ,
Bai kamata ace yai maka wanan cin fuskan ba gaskiya,
Zataci gaba sai ya tare da cewa cikin yar murmushi maryam ai ba karya ya fadi ba ko,?
Tunda dai ni din duk yan uwana kafirai ne ni kadaine Allah ya cire a cikin su,
Kinga ii dole ne in ta samun wanan challenges din ko, ?
Ta gumi tayi da hannayen ta bibiyu tana sauraren shi cikin tausayi
Tana ji tankar ace itace a kusa dashi a lokacin a matsayin ta nadan uwan ta,
Amma afili sai tace to ya yusuf dan Allah kayi hakuri bazan sake ba
Abin ne yaci min rai sosai wallahi shi yasa nakai anty taji da kan ta don a dauki mataki akai,
Murmushi yayi yace aa maryam wani mataki kuma kawai na bar masu diyar su kawai,
Cikin sauri tace subbahanallah dan Allah ya Yusuf kadakayi haka pls,
Saboda may maryam kinfi son ta dani yayan ki ke nan,,?
Ya yariny ce wallahi akwai tausayi idan ka ganta
Nan dai yaci gaba da bata musalai akai har ta dan gam su sukayi sallama,,,,,,
ZEEE. MAKAWA,
[3/24, 10:09 PM] Zainab Makawa: πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
FUREN JUJI
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
5β£9β£
ZAINAB IDRIS MAKAWA,
Wanan shafin nasadaukar ga Shahararen Admin of Admins na,COOL NOVEL MAKEUP AND KITCHEN 1,2,3,4,&5
Hayatu Baba Zubuiru (Ya Hayatu), daukacin masoya Novel din FuREN JUJI muna tayaka murnan zagayowar ranan haihuwar ka,πππ Ubangiji Allah yasa albarka ga shekarun da aka diba,
Babu shakka ka kai a yaba maka musanman ta yadda kake ilmantar da koyarwa uwa uba girki da kwaliya ga nishadantarwa mai karatu Allah ya kara daukaka da Basira πππ
Zaune suke su biyu suna karatu inda maryam ke koyawa Na,imat yin tsarki da kuma alwala a musulun ci,
Maryam najin dadi sosai na yadda Na,imat keda saurin haddace karatun da suke yi,
Sallaman mutyn kawai suka ji daga sama saboda duk basu san da zuwan shi ba a,yau din,
Ku san lokaci guda sukai mai sannu da zuwa atare,
Na imata mike da sauri daniyar zuwa ta rugun may shi kamar yadda suke yi ada in ya dawo daga tafiya,
Da sauri Yusuf ya jaye gefe guda yana mai ce mata cikin kakasar murya
I warn you is forbidden in islam pls don't do dis again,
Cikin nuna jin nauyi Na,imat tai dan rau da fuska kamar mai jin ciwo,
Maryam ce ta kawar da shirun da yadan biyo baya da fadin sannu da zuwa ya Yusuf, ya hanya,
Daidai lokacin da yake zama ya karba mata da fadin Alhamdullah,
Sai kuma yadan waiga kamar may nemar wani abu agidan
Maryam ta mike a hankali ta tatara littafan da sukai amfani da shi, zuwa cikin wani dan loka da suke aje littafan addini aciki,
Muryam shi taji yana cewa ina Anty ?
A takaice tace sun tafi, gidan barka haihuwa,
Fridge ta nufa da niyar dauko mai drinks amma sai taji muryan shi yana cewa,
No, no,no iam ok, thanks,
Mun tsaya Bobi gurin su mama an bamu fura da nono mun sha nagode,
Da sauri maryam ta juya inda yake tana mai kallin mamaki don jin abin da yace,
Cikin fuska ba sauki yace yes daga can muke tana gaishe kuma,
Marfin fridge din maryam ta sake a hankali ta koma zuwa gefen kujerar ta zauna,
Na,imat, wace ke kokarin zama kusa da shi take tambayar shi labarin maman Choima,
Sai da ya dan furzan yace mama tana lafiya sai,dai fitina kawai data kara, maryam wace ke gefe guda tai murmushi,
Sallamar mukaji daga kofa gida ko ba,a fada ba sun san cewa masu shigo da tsaraba Yusuf ne,
Saidai wanan karon tsaraban ya sha bambam da na kullun,
Wasu irin set din akwatina aka dinga shigowa da su,
Mamaki karara ga fuskokin su maryam da Na,imat
Da sauri maryam ta shimfida wani dan karamin center carpet a tsakiyar falo suka dinga ajewa a sama ,
Kafin wani dan lokaci duk sun gama shigo da abin da yazo da shi,
Maryam batai mamaki sanin cewa yakanzo da motoci fiye da guda daya idan zai zo da wuya ya,shigo da guda garin,
Shigowar Anty Dije gida,ne ya sa shi dakatarwa da dogon wayan da yake yi tun zaman shi acikin yaren su,
Nan suka shiga gaisawa da ita tana mamakin ko ina yafito da wanan kayan,
Bai mata wani bayani ba akai ya mike yana cewa zai tafi ya watsa ruwa sai yadawo,
Fitar Yusuf Anty Dije ke tambayar mu ko kayan may ye wanan yazo da su,
Maryam wace ke kokarin mikewa don shiga kitchen bata, tace komai ba don in ma har sanin ko na may ye ai itace ya kamata tasani,
Tunda Yusuf yabar gidan bai dawo ba har suka gama duk wani aikin da yakamata suyi,
Sai zuwa bayan sallah isha,i Yusuf ya shigo gidan,
Wanda zuwa lokacin maryam ta fahinci Anty ta ta matsu tasan ko kayan may Yusuf yashigo gari da su,
Don ita azaton ta kayan lefen shine yashigo da su tun da ba shi hakkuri a kai,
Sun kara gaisawa da sister Dije inda take mai ya aiki ya bayan rabo,
A hankali maryam tai magana kamar wace ke, jin ciwon baki,
Tace mai a kawo maka abinci ne,
Haba dai maryam wanan ai tayin rowa ne ko,
Ina kin hada mai komai ko basai kawai ki kawo ba,
Anya Maryam za muko, sha ruwa agidan ki kuwa tana wa Maryam din ba,a,
Maryam ta dan turo baki gaba tace to anty idan kace zakaiwa mutum abu sai yace shi ai ya koshi,
Ido kawai ya bita da shi yasan cewa don dazu zata bashi ruwa ne yace ya gode shine takewa wanan zancen,
A bincin ta dauko mai har zuwa inda yake ta dora saman dan karamin stol,
Ita da kan ta tai serving din shi da kuma kawo mai ruwa,
Sai a lokacin ne ya fara yiwa anty bayani kamar haka,
Anty ki samu time ki bude boxes din nan ki duba kiga abinda ke cikki,
Idan da akwai abin da za,a saye akara sai ki fada min akaro,
Maryam najin sun fara zancen akan akwatinan tai saurin mikewa daga gurin da take cikin niyae wuce wa ciki,
Amma sai ji tayi anty na cewa maryam zo ki bude ke da Na,imat ku diba min pls,
Ai bata san lokacin da ta dago kai ta kallo yae ta tace wa ni Anty,?
A kwai wata maryam ce agidan bayan ke maryam, inji Anty,
Kala batace ba sai wucewa da tayi direct gurin akwatinar,
Da babban nasu daga ciki ta soma budewa don yafi tare guri,
Zannuwa atamfa zube a ciki tankar shago, saida su kala,kala,
Sai da gaban maryam ya fadi saboda irin kayan da aka jibga acikin akwatin
Da aduke take sai takai tsugun ne saboda kafar ta ba zai iya daukanta ba,
Haka tai ta daga kayan daya bayan daya har su ka kai karshe yana zaune bai ko kula da abinda sukeyi ba,
Γnty angama inji maryam wace duk tagaji da dagawa,
Wanan ai ba wanin abin da zamu kara aciki a kai masu haka kawai Allah dai yasa albar ka,
Sai alokacin yadago yana kallon anty yace cikkn gyaran murya,
Anty wanan kayan kayan auren Na,imat ce da Ibrahim,
Wani ajiyan zuciya maryam tayi ta yadda ba wanda zai jita,
Amma da fada takeyi don may zasu zageshi haka kuma ya wani zage ya kashe masu dukiya haka ,
Muryan shi ce taji yana cewa anty a,gaskiya
, bana son Ibrahim yai komai anty, saboda ba wai yadade da fara aiki bane,
Kayan daki nake son ki samu time sai aje azaba mata duk inda kikaga yafi,
Cikin watan azumin nan nake son ko da an fara ne ayi auren pls,
Saosai kowa ke kallon shi da mamaki yanzu duk wanan kayan ba akan shi ya sawa ba,
Kawai don jin dadin wasu yayi shi,
Shin anya kuwa ba zancen mutane gaskiya bane da suke cewa Yusuf wai furen kan juji,
Don dai sam halaiyar shi duk abin ayabane baka taba ganin yayi wani abin assha,
Bayan kuma mhaifin shi yana can a matsayin shi na kursungumin kafiri wanda ko da,wasa bsi kaunar yaji kalman musulunci,
Sallamar wani yaron makwabtar su ne ya sa kowa shi,
Yaron yace Assalamu Alaikum wai ance maryam ta zo ga A,A a waje gida,
Wani irin