Showing 105001 words to 108000 words out of 255288 words

Chapter 36 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

1382

muna son zuwa asubiti da may zamu zo,
Ko yanzu aida taimakon Alhajin nan ne muka samu mukazo in bashi ba ai da saidai yadda Allah yayi kawai,
Kagashi nan da nan yagane cewa sai munzo asibiti ba na gida bane yanzuma gashi tasamu sauki,
Da har zamu koma sai shi Alhajin tace mu bari har gobe sai ta dan kara samun sauki,,
Lokacin jin tana ta cewa Alhaji Alhaji yasa shi waigawa gurin maryam wace ke dan rakube a gefen bango,
Yace waye yake magana halan sai cewa maryam tayi a hankali,
Yusuf ne, yakawo ta,
Nanata sunan yayi yace Yusuf,
Wani Yusuf ke nan, wai halan, ?
Tace mai Yusuf wanda ya musulunta mana, maizuwa gidan mu,
Ok Joseph ?
Kai kawai ta gyada mai alamar eh,
Mijin mama yace a,a a daba musulumi bane shi din,?
AA yace kafiri ne yazo ya musulun ta koda yake har yanzu bawai an yarda da musuluntar nashi ba ne ai,
Sai a lokacin maryam tadaga kai ta kalle shi saboda kalamin da ya fadi,
Sai mijin mama yace a,a kai ko may za,aiwa shakka aciki tunda dai yariga ya musulunta,
Mikewa yayi tsaye da kyau daga rankwafawar da yayi saman karfen gadon da mama take a kwance,
Yace Arne fa ko ya mysulunta ai ba abin yarda bane,
Jin kalamai da yakewa Yusuf ne sai taji kawai bataji dadin su ba sam,
Don haka sai, tadan duka ta dauko wani leda tana kokarin fita daga dakin
Ina zaki tsata mu tafi don gida nake son zuwa indan watsa ruwa wallahi duk nagaji,
A tare suka fita daga dakin inda ta takai mai zuwa gurin motar shi,
A nan suka dan tsaya suna hira a gagauce saboda ita ranan gata nan dai ne kawai,
Shigowar motar suce tare da su jibrin da wasu abokan shi yasa su duka kallon inda suka tsaida motocin su,.
Dakin suka shige gaba dayan su don su diba maijiki,
A,A bai kara wani lokaci ba ya ja motarshi yabar gurin tare da Alkawarin zai dawo ya kara diba ta,
Ba ai wani dadewa ba su jibrin suka fito amma ba da, Yusuf ba,
Tana son taje dakin amma, sai tana jiran su fito saboda duk mazane acikin dakin,

Kan ta na saman ciyar ta, ta dan duka tana tunane,
Bakomai take tunawa ba sai mutumin ta watau A,A
Wai shi wani irin mutum ne, hakana, ta kasa fahintar shi har yanzu,
Gashi a fuska zakace ai baida matsala, sam,
Kafin ta karasa sai jin muryan mijin mama tayi yana cewa,
Maryam aida kinzo ya sauke ki gida ki dan huta tunda gamu nan da yawa ai,
Kamar tace a barta kawai sai taga musu da babba baida dadi,
Kuma ko banza tana da bukatar son watsa ruwa ajikinta, don tadan ji sanyi,
Tafe suke su biyu a motar, a hankali yake tuki don marance ya fara abin hawa sunyi yawa a hanyoyin,
Wani irin sanyi AC da kamshi ya gauraye motar, sai Qira,an dake tashi na Ahmed Suleiman kano,
Kamar daga sama taji muryan shi yana cewa,
Kiyiwa saurayin ki magana yadaina kirana da tubabbe pls,
Batare da ya kalleta ba yake magana, zaka zata mako bada ita yake magana ba,
Da,sauri Maryam, ta dan dube shi tankar zatai magana sai kuma ta fasa kawai tai shiru,,,
Idan kasa zai tsage zata shiga don kunya wanan maganar,
Wai ma ta ya ya ji wanan zancen, da akayi,, don dai baya nan a,lokacin,
A rau,nane ya, yace ban san may guy din nan ke ji dani ba wallahi,
Maryam dai har zuwa yanzu kala batace mai ba,
Sai dai jin da tayi, ya furzar da iska har sautin shi ya iso inda take,
Sai,dai,dai kofar gidan su,ya tsaya da motar shi, a yadda tagani duk rayuwar shi ya baci matuka,
Dan Allah kayi hakkuri ban san lokacin da ya fada ba,
Shima bai yi mata magana ba saidai ko karin Parker motar da yake yi,,
A hankali ta bude, kofar batare da kara kalon inda yake ba,,





ZEEE MAKAWA,,,

[3/12, 10:47 PM] β€ͺ+234 813 139 5577‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
4⃣5⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA,,

Assalamu Alaikum yan uwa musulmai tare da fatan kuna liya,
Da plsn girman Allah yan uwa marubuta da makaranta kubani, dan hankalin ku dan pls
Wallahi muji tsoron Allah musan cewa wata rana zamu gammu a gaban shi,
In yanzu in anjima in gobe,
Anytime kwanan mu yakare,
Wallahi littafan batsa sunyi yawa yanzu sai mun kula mun gyara kada barna yai wa a sanadin rubutun mu,,, Amma idan maganata akwai laifi aciki ku yafe min pls,,,,πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘πŸ‘



Alhamdullahi washegari mama tasamu sauki sosai don haka ta samu sallama daga likita amma zata dawo bayan kwana hudu,
Sam Yusuf bai nuna gajiyar shi ba sai ma kokarin nuna tankar shi dan gida ne cikin su,
Duk da bawai magana mai tsawo yake yi da su sosai ba amma zuwa yanzu sun dan fahinci halin shi,
Idan ka gan shi zaka dauka wulakanci ne sai ka dan zauna dashi zaka gane miskilanci ne,
Baban su maryam ne ya umarci Anty Dije da ta bar maryam ta, tafi ta kula da mahaifiyar ta tunda suna hutu, yanzu,
Don haka maryam wace, suke wasan boya da Yusuf tun jiya da ce tafadawa saurayin ta yafita harkan shi,
Sun isa kamfanin Bobi ana, shirin yin sallah azahar ,
Sai fitar su a cikin motar ne maryam taga, ashe duk kayan nan da yasaiya masu na amfani a asibiti suk sun kwaso abinsu sun zo da shi gida,
Sosai ta jin,jina mai saboda bakaramin namijin kokari yayi ba gurin ceto mata mahaifiya daga halaka
Da sauri maryam tashiga don ta gyara dakin mahaifiyar nata, inda sauran matan gidan ke ta mata sannu ya jiki,
Saidai may turus maryam taja ta tsaya saboda ganin wani irin dindimay,may katifa sabo fil a cikin ledar shi,
Da mamaki takarasa gurin inda daya dafa cikin matan ke sheda mata cewa, ai daga can kwantagora akazo da shi ance na mamantace,
Ga sabon randar roba ta ruwa, ga kujerun roba farare guda uku, da filolin su,
Jiki ba kwari zuciya fam da tunane maryam ke aikin dakin,
Ko ba, a tambaya ba tasan cewa aikin Yusuf din ne haka,
Kafin wani lokaci dakin mama yakoma kamar wata yar birni, can,
Sai zuwa dare maryam ta samu dan hutu bayan ta tabbatar cewa mahaifiyar ta tadan yi,wanka tasha magani,
Washegari da safe maryam na idar da sallah, asuba bata zauna ba fitowa tayi don taimakawa kishiyar mama da wasu aiyuka,
Saida ta tabbatar tagama komai ta koma daki don ta taimakawa mahaifiyar ta,
Kafin gari ya karasa haske duk maryam ta kammala komai a nata fan,nin,
Matan kauyen sai shigowa sukeyi da sunan gaida mama da jiki,
Amma azahiri gulma ke kawo su don wasu basu ko iya boye gulman su sai su dinga latsa katifa ko taba wani abu ace irin na wance na wance ne,,,,,

A, dadafe yafito daga cikin motar shi da taimakon Samuel yasamu yau yafito zuwa shagon,
Inda yakan zauna can nisa kadan saman kujera yadinga kallon masu harkokin su a cikin gari,
Wani dan kabilar su saman wata mashin ta matasa yazo ahan mai,
Ganin Mr Ema a gurin yasa shi zuwa gaida shi har inda yake,
Anan bayan sun gaisai sunyi ya kwana biyu ya jiki mutumin ke tambayar shi cewa a she, Joe yana gari ne, ?
Da mamaki yakara tambaya yana mai kada kai da kafar shi yana rage haushin da maganar ta rasta mai acikin zuciyar shi,
Inda mutumin ke tambayan shi cewa ko suna da mara lafiya ne a asibitin tagwai, ?
Wani sabon mamaki ne ya kara kamashi inda yake cewa, w
Watau Joseph yana nan yana yiwa hausawa da yaran su dawai niya ke nan,
Zaune yake idan kagane shi a lokacin zaka dauka cewa, cikin jin dadi yake
Amma sam cikin tashin hankali yake inda yanzu yasha alwashin cewa, sai ya koyawa Joseph hankali tukun,
Akwai wasu samari yaran hausawa yan wi,wi yan daba su yayi haya,
Inda ya fada masu abin da yake da bukata su yi mashi akan Yusuf,
Shiko Yusuf yana can a unguwar Rimaye ystafi kaiwa wani malami dake unguwar sadaka,
Wanda zai tallafawa almajiran shi da su a gina masu babban daki inda zasu dinga kwana,
Malam Shehu mai almajirai na Rimaye yai mamaki kwarai da wanan alherin da Allah ya basu cikin lokaci guda,
Addau,a na muhinmin yasa ai mashi cikin, dafifin almajirai inda yabisu da sadakan yan hamsin,
Sai wani makarantar matan aure da ke Kan Wuri, bayan sectaria inda yakai masu sadakan abin zama tare da kara masu girman makarantar,
Wanan abin ya jawo magana sosai duk da duk inda yakai alheri sai yace dan Allah kada a fadi a saya shi domin Allah yayi,
Amma ina mutane saboda mamakin irin halaiyar shi sai an fada cewa da ace sauran masu kudin mu zasuyi koyi da shi da sun taimaka wa al,umman musulai, da basu dashi,
Daga hotel din ya ke yana sauri saboda yana son zuwa gurin wani mutum da zasu yi hurdan ,Noma a shekarar bana,
Wasu matasa ne a saman mashin guda uku, suka biyu shi,
Dafari bai kula da cewa shi suke bi ba saidaga baya ya hankalta da su,
Sannu,sannu ya fahinci cewa shi suke bi, a baya a hankali yasa signal, ya tsaya gurin wani katon iccen mangaro,
Security guard din shi ya kunna nan da na signal yakai gurin security din shi da koyaushe a cikin shiri suke suna biye dashi,
Kafin yafito yaji saukar sanda a bayan motar shi duk da hankalin shi ya tashi amma sam bai nuna masu tsoro ba,
Muyan matasan yan daban yayi suna cewa kai karamin dan isaka wa zai yarda da musuluntar ka,
Har yanzu mu kafiri kake a gurin mu. Don bamuga ka iya sallah ba tukun ko sabbi saukan mata baka iya ba,,,,,,
Wasu bakaken motoci ne wulk guda biyu suka gani shake da security cikin bakaken kaya suka tun karo su,
Da gudu suke kokarin haye mashin din dasukayo haya don su gudu,,
Cikin rashin sa,a sai guda yafadi kafin yai wani yunkuri aka cafke shi,
Nan da nan gurin ya cika da jama,a makil, mutane da son ganin gulma,
Shiko dan matashin sai cewa yakeyi
Dan Allah kuyi hakkuri ba nikadai bane turo mu Ema mai manja yayi muyi mashi haka wai yai mashi laifi,
Yusuf najin haka ran shi ya baci sosai bai tsaya ba sai kawai ya shiga motar shi

A fusace ya isa gidan nasu tun daga wahe yake kwaka wa mahaifin shi kira,
Wanda shiko Ema yana can yana fada da samarin nan yace may yasa suka bishi a cikin gari,
Jin yadda Yusuf ke kiranshi yasa shi katse wayar don jin abin da yazo da shi,
Yana zaune falin shi saye da wata yar babban ringar banga ta lace, baka, kanshi saye hular su ta yan kabilar IBO,
Dad if you want to killed me killed me by yourself pls,
Amma kada ka sa kanka cikin harkan yan daba yaran da basu san komai ba sai kudi,
Su jawo maka magana kawai
Idan da suna da wayo da wallahi bazasu karbi aikin ka ba akaina,
Gaskiya baba wanan abin da ka aikata yabani mamaki,
Dad idan kaso pls kayi hakkuri da musulunta na dan ba zan taba komawa cikin kuba don kuma muna maku fatan dawowa hanya mafi alheri,
Daga haka yasa kai yabar gidan cikin bacin rai, da kunar zuciya,
Direct police station, yanufa don yasa a sake yaran don shi sam baiga lai,fin su ba,
Duk yadda police sukaso a dau,kaka karan bai,yardan masu ba saboda yasan cewa mahaifinshi zai wulakanta akanshi,
Duk abinda ake ciki Mr Ema nada labarin komai saboda yan leken asirin da yasa tabaya,
Tun da yabar police station din yaji kawai ya ma rasa inda zai nufa,
Kai tsaye ya kama hanya sai kamfanin Bobi, inda ya shiga garin bayan la,asar lokacin har maryam sun gama girkin abincin dare ko,
Cikin mutunci mutanen suke gaishe shi tare da nuna kulawar su da jin dadin su,
Sai godiya suke mashi akan irin taimakon da yaiwa mama,
Wani dan dadttijo yace yaro mungode kaji, Allah ya hada hankulan da diyagga kaji,
Sam bai fahici manufar su ba saboda hausan shi bai,kai can ba,
Tare da kanin mijin mama suka shigo cikin gidan shi yai mashi iso,
Harzuwa dakin mama Alhamdullahi don yau mama,azaune take saman tabarman roba da maryam ta shimfida, mata, a can gefen dakin ta,
Kai tsaye inda take zaune suka nufa inda Awalu ke mata sheri yana cewa a,a,a yaukan sauki yasamu kece zaune a waje,
Yusuf yana kokarin zama yana gaushe ta yana kuma yi mata ya jiki,
A cikin gwari,gwarin hausar shi yake ma mama ya jikin yakuma take ji yanzu,
Sai a lokacin maryam ta iso gurin shi cikin sakin fuska taje mai sannu da zuwa, dakuma ya hanya,
A hankali bayan ya furta mata cewa lafiya ya jikin mama sai take ce mai ya su Assalam da Issalam,
Saida yai murmushi sanan yake cewa, gaskiya yau bai samu zuwa gidan su ba,
Amma dai sunyi waya da Anty Dije da safe, kafin ya fito,
Yauce rana ta farko da wani magana mai dan tsawo ya taba shiga tsakanin su,
Maryam na kokarin mikewa ne taji muryan mama tana cewa ke yar baba ki ki bashi abinci a daki,
A razane maryam ta dago kanta don tasan cewa, bazai ci ba,
Amma sai taji baice komai komai alamar zaici,
Muryan Awalu ne ke cewa, haba yaushe Alhaji zai iya cin ,abincin mu,
Maryam ta fahinci zai ci don haka bata kara cewa komai ba ta hada mai a saman tire takai mai dakin mama inda ta dan fito,
Sai cike take da jin kunya kalar abincin nasu da zai gani,
Tuwon dawa ne da miyar danyen karkashi sai, naman kassa na rago da aka zuba, aciki, irin local miya akayi shi bawai da stew daban ba,
Ruwa ta debo mai a,randar kasa mai sanyi cikin kwanon sha,
A hankali taji muryan shi kamar mai rada ya na,cewa,, ki dan taimaka min Maryam da ruwan wanke hannu pls,
Ruwan tadebo,ta,mai a,cikin wani silver mai fadi,
Sautin murmushin shi taji yana cewa, Awalu yatafi ni kadai zan zauna a dakin,
Babu shiri maryam ta koma, can gefen katifa, ta zauna tana dan wasa da yatsun hannun ta,
Daga inda take zaune tana ganin yadda yake cin abincin hankali kwance, yana mai lunshe ido,
Shikam ashe akwai wanan irin abincin har yanzu anayi,
Rabon shi da irin wanan tun suna yara da yake bin su KB da jibri gidan kakan nin su, suna ci,
Saidai daga ita har shi ba mai ma wani magana, shidao kokari yakeyi da farko, yaci kada mama suce yana kyamar su, sai kuma koyi da sunnah dayaji ance yana da kyau,
Amma sai gashi ya buge da ci sosai fiye da tsanmanin shi,
Saida ya kusa gamawa yadago kai yakalle ta inda take zaune a takure,yace,
May sunan wanan abincin,?
A hankali tace tuwon dawa miyar karkashi,
Yana mai tsamay hannuwar shi zuwa cikin ruwan wanke hannu yace,
Dazan dinga samun shi akoda yaushe da bazan ci wani abinci ba sai shi,
Kanta ta gyada almar mamaki, jin maganar shi,da yayi ita da take ganin ba zai iya ciba, sai ga shi ya buge ga santi,
Yunkurin mikewa tayi ta kwashe kwanonin agaban shi,
Amma sai taga ya ciro kudi masu yawa ya aza saman ture din yace pls kiba matan gidan nan su raba,
Muryan ta na rawa tace, kai haba abin ya,yi wa gaskiya,
Kamar ba shi take ba don sai ma kokarin goge hannuwanshi da yakeyi,
A, hankali ya fara kokarin mikewa zuwa bakin kofan dazai fita,daga dakin,
Ya juya da kyau ya fuskan ce ta yace aikin Alheri bai yawa ga inda ake bukatar yi,
Ba rokona sukayi ba can,cantar hakan naga yadace nayi,
Idan nabar wanan taki bazan kara zama free man ba sai lokacin dana dawo kuma,
Cikin nuna kariya tace mai Allah ya saka da alheri Allah yasawa saura albarka,
A, a maryam albarkan iyaye nake bukata ba ta kuba yaran zamani,
Kala maryam batace mai ba don kada maganar su yai nisa sosai,
Da sauri ya nufi hanyar fita waje tun kafin ta gama hada kayan abincin,

Kowa agidan sai murnan kudin da ya raba musu su keyi dubu guda guda kamar a mafarki,
Wasu daga cikin sun ne ke cewa maryam gaskiya kin yi dace,
Da mamaki maryam ke tambayar zuciyar ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login