Showing 93001 words to 96000 words out of 255288 words
Chapter 32 - Furen Juji Book 1 Hausa Novel Complete
ka daga cikin har kokin ka,
Wata irin karfafan ajiyar zuciya Yusuf ya sake da yaji wanan zancen na Sonny,
Fuskan shi dauke da alamar damuwa mai fayyace mamaki aciki,
Magana Yusuf din ya fara cikin wata irin murya mai ban tausayi don duk mamakin wanan hukuncin na Sonny ya ruda shi,,
Kawai sai yaji Sonny din ya kaure da wani mahaukacin dariya alokaci guda,,
Sai kuma ya koma ya tsuke fuskan shi ya fuskanci Yusuf din karo na biyu yana mai kura mai ido cikin ido,
Yace may zakace min Joe, koka manta cewa da taimakon ka muka kai wanan matsayin da muke aciki ni da abokina
Inda Allah bai hada mu da kai ba ka dage har saida kaga mun gama karatun mu aida ba mu kai haka ba, ko ?
Mikewa yayi ya zagayo har zuwa kujerar da Yusuf yake zaune yadan duko yarankwafo zuwa gare shi yana mai magana kamar cikin rada,
Yace , don't say thanks pls,?
U deserved it
Yusuf wanda kanshi ke a duke don jin zancen yake tankar a mafarki,
Ya dan dago kai ya kalli Sonny din kara na biyu cikin mamaki,
Murmushi na gamsar wa Sonny din yai mai alamar eh,
Haka suka tashi gurin inda Yusuf kewa Sonny adduan fatan shiryuwa hanya madaidaiciya ,
Batare da sanin Sonny ba Yusuf ya gai,yato su jibrin tare da KB inda sukazo mai tare da,Abdulsamad,
Saboda yanzu suyake ji tankar yan uwan shi na jini,
Sunyi mamaki sosai irn dinbin dukiyar da Sonny ya tara a kasar mutane haka bayan ga kasar shi can na haihuwa suna bukatar shi,
Sun yi wa Sonny godiya sosai dafatan kara samun daukaka a dukiyar shi,
Shiko sai mamakin irin yadda suka dauki joe tankar dan uwar haihuwar bawai kawai saboda addini suke nuna mai haka ba,
Sosai Sonny yaji dadin zuwan su inda ya mai dasu kamar wasu manyan guest din shi,
Satin su guda sukadawo gida cike da farinci, dakuma alheri mai yawa,
Saida Yusuf ya tabbatar da cewa komai da ya turo su Jibrin da shi da KB sun kammalla mai
Sannan ya fara shirin komawa gida Nigeria, tare da karfin gwiwa atatare da shi,
Γnty Dije ce zaune a saman tabarman robar da ta shimfida a,waje saboda zafin da akeyi a garin tankar rana zai dafa mutum,
Gefen ta Abubakar ne a kwance cikin net na yara yana barcin shi hankali kwance,
Maryam ce ta fado gida a daidai wanan lokacin, cikin gajiya tashi gida da sallamar ta a bakin ta,
Anty Dije tadan daga kai, takalle ta gami da ajiyar zuciya,
Tacd don Allah maryam, huta kidan taimaka min muyi aikin nan,
Maryam wace tanawo wani farin kujerar roba dake aje a gefe guda, ta zauna,
Tace wai Allah ana dai zafi gaskiya, sosai shi yasa yau ma banko tsaya jiran safiya ba na sa kai kawai na wuto,
Kallon ta Anty Dije tayi cikin yar tuhuma kamar zata daure sai kuma ta kasa
Tace shi A,A din ya daina dauko ku ne yanzu,?
Maryam wace tambayar yazo mata a bazata,
Shiru tayi saboda ta rasa ansar da zata ba Anty Dije a lokacin,
Kara maimaita tambayar tayi wa yar kaunar nata,
Wacce dama duk kwanakin nan tana lura da bata acikin walwala tun lokavin da baba yazo da zancen ta,
Dan hawayen da take kokarin makalewa, ne yadan digo daga idon ta,
Ki tashi ki dauki abinci kici inji Anty saboda ta fahinci, cewa kuka kaunar nata take shirin yi,
Tausayin irin hanlin da yar uwan nata take ciki takeyi
Saboda ta san cewa tana cikin wani hali saboda so,
Maryam ta share hawaye ta da bayan hannunta ta mike zuwa cikin da kunar su,
Kallo anty Dije tabi bayanta dashi tana mai mata fatan alheri a rayuwa,
Fatan dai Allah yai wa Maryam din zabi na alheri, a rayuwa,
Tunda maryam tashiga ciki tana zaune, a bakin gadon ta ko, takalma bata cire ba akafar ta,
Wayar ta dake a cikin jakar ta ce tai kara alamar kira,
Kamar ta share kamar kullun saida tace bari yau ta dauka taimai kashedi ya daina kiran ta kwatakwata,
Cikin wani irin murya mai birkita maryam a duk lokacin da taji shi,
Wanda yasa gaba daya duk maryam din ta rikice, alokaci guda ta rasa duniyar da take,
Wani irin taji aranta na yadda sam bazata iya fada mai maganganun da ta shirya fadamai ba,
Maryam ta saki wani irin ajiyar wanda shima A,A din yaji kamar yazo inda maryam din take alokacin yabata hakkuri duk da irin kunyarta da yake ji,
Shima A,A din anashi bangaren ajiyar zuciyar don jin cewa maryam din tadan sauko daga fushin da ta dauki lokaci mai tsawo tana yi dashi,
Yakara cewa cikin wata irin murya ransarauniya maryam yadade ga A, A gaban ki tuba yake yi,
Murmushi ne ya subuce mata tai shi a hankali, duk yadda taso tai magana alokacin ta kasa,
Yace Maryam ina fatan zaki bani dama in zo in maki bayanin irin abin da ake ciki,
Shiru tayi saboda sam bata san may zai ce mata ba idan har yazo din,
Tasan dai bai wuce yace mata kawai tayi hakkuri ya aure su su biyu kamar yadda safiya tace yace,,
Wani irin ajiyar zuciya tasake tace, idan zuwar naka bazai zai haifa min alheri ba kawai kabarshi
Yar dariya tayi irin ta mazan da suka san kan su,
Ya Allah dai ya kai mu anjima ki dubi hanyata nagode,
Idan ta ta lumshe tanamai jin wani iri atare da ita
Ajiyar zuciya tayi mai fitar da sauti tana mai bude idon ta, da suka sauka a saman na Anty Dije,,,,,,
ZEEE. MAKAWA
[3/7, 1:14 PM] βͺ+234 803 381 3188β¬: πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
FUREN JUJI
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
4β£0β£
ZAINAB IDRIS MAKAWA,,,
Yan uwa musulmi barka mu da jumma,a , Ubangiji Allah yasada mu da Rahama da Albarkan da ke cikin wanan ranan,
Allah ka yafe muna kurakuraren mu Allahuma Ameen,ππππππ
Sanye yake cikin wasu, fararen coth, da wani, farare, takalma rufaffu, kayan sun karbi,
jikin shi, sosai, sai idon shi dake saye da dan farin glass karami,
A hankali yake ta,kowa daga matakalar jirgin, guda ,guda, hannun shi,guda yana cikin aljihun wandon shi,
Jirgin su a airport din Lagos ya sauka, inda masu taron shi suka zo,,
Gurin screening yanufa batare da wani bata lokaci ba akai mashi, duk wani screening yadda yakamata,
Daya daga cikin driver s din da suka zo daukan shi yakar bi wata yar case da ke hannun shi,
Bawani bata lokaci su,kabar airport din shi da wa yanda suka zo tariyan shi,
Sannu a hankali yakarewa gidan shi kallo gidan da yakewa kallo tankar wani sabon guri da bai taba zama ba,
Saboda gyaran da ya turu da kudi akai mai,
Anan falon ya zube saboda yana tare da gajiya, ba abin da yake bukata sai ya dan watsa ruwa ajikin shi,
Ko zaiji dan karfi karfi ajikin nashi, kafin ya samu dan abin da zaici,
Motsin da yaji ne ya sanya shi saurin daga kai, don ganewa idon shi kowaye,
Hakan yai daidai da Ejoma, wace ke sauko daga wani dan steps da yafito wani part na gidan,
Da saurin ta tazo daniyar rungumar shi kamar yadda su ka saba idan yadawo koda gurin aiki ne,
Da sauri yadan jaye jikin shi daga gareta amma yana mai,mata murmushi,
Dan yaron dake rike a hannun ta ya daga sama cikjn wasa yana zagaya da shi,
Sauke yaron yayi yana mai kallon Ejoma wace ke saye da wani bakin buje da yafitar mata da surar bayanta baro,baro, gashi dan guntu, daidai iya katarar ta,
Ejoma ce tafara magana bayan taga ya, sauke yaron daga daga shin dayayi,
Tace brother we don base, woo,
Shima murmushi yai mata yana cewa where my grandma ?
Grand mother dey for village since, tree months ago,
Murya kasa kasa yake tambayar ta ya akai haka ,
Ejoma tadan tabe baki tukun sai tace,
You know Dad no dey allowed her to go to her church,
A dan tsora ce ya dago fuska cikin mamaki da jin mamakin zancen ta,
Saikuma ya maida mamakin nashi zuwa dan murmushi mai sauti, saboda tunawa, da sanin kowaye mahaifin shi,
Fuska kumshe da murmushi yace ma Ejoma is alright, i, will go and seen soon,
Daga haka ya haura zuwa sama inda dakin shi yake don yadan watsa ruwa,
Cikin daga murya Ejoma ke cewa brother your food is ready on the table,
Yakai wani lokaci a sama sannan ya sauko daidai lokacin da Ibrahim shima yashigo gidan, don taron shi,
Duk atare suka taru suka ci abinci, gabadayan su,
Tsab ya mike yashiga wani dan bayi dake makale a cikin makewayin,
Alwalar sallah azuhur yadauro alokacin amma saboda gajiya nan ya tsaya a falo saman sallaya,
Addu,oin da yajeyi bayan sallah ne ya gabatar alokaci har tsawon wani lokaci,
Brother are still bearing the Muslim,
Idanu ya zuba mata don mamakin kalamin ta, saboda yaji abinda tace kamar a mafarki,
Don haka ya shafa addu,an shi ya fuskan ce ta, da kyau,
Gyaran murya yayi yace mata dama ana canza addini ne anyhow,?
Sai ta girgiza kanta tace ba haka bane kawai dai taji Dad na cewa evils spirit din da suka shige shi har ya juya zuwa Islam,
An, kore su dakarfin addu,oin pastor's masu yawa daga cikin pastocing su,
Wani iri Yusuf din yaji a cikin zuciyar, wanan maganar ya kasance mara misaltuwa agare shi,
Shin dama ashe har yanzu Dad naga bakar shi na cewa sai ya canza addinin shi da yake ra,ayin yi a rayuwar shi,
Gaskiya zai dauki wa Dad duk wani mataki da yakamata yadauka wanan karo,
Ai bashi kadai bane, dan shi yafara zama musulmi, da zai ce ba zai hakkura ba ,
Koda kuwa Dad din zaiyi barazanar kwace mai duk wani dukiya da ya mallaka a rayuwar shi batare da yabar mai koda kwandala ba,
Ya tuna da labarin da Abdul samad yabashi, na,wani matashi , da yai zamani da manzon Allah S,A,W
Maisuns Mus'ab Ibn Umair, matashine, mai ji da kanshi a cikin garin makka,
Matashin ya fito daga wani family mai karfin arziki sannan,sannan ya kasance dangata sosai daga duk wani matashi na zamanin,
A wancan lokacin kaf samarin Makkah suns jin jins mashi wajen ado, don ko turaren ma dayake amfani dashi alokacin abin kallo ne,
Sannan mahaifiyar shi takasance mai tsananin sonshi wanda hakan ya haifar da shakuwa mai karfi gaske a tsakanin su,
Tufafin da Mus,ab Ibn Umair yake sawa, da takalmin shi masu matukar, tsadane so sai,
A lokacin da manzon Allah SAW ya fara wa,azi da kira ga mutanen makkah akan subi addinin Allah, watau musulunci,
Yawan wa,azin da yake saurare daga Annabi yaji ya gamsu zai shiga addinin islama.
Hakan yasa ya fuskanci tsanani da azaba da rashin galihu,
Inda yakoma yakassnce tankar almajiri, duk wanda yaganshi bazai gane shine shiba
Dan yadda ya koma ma abin tausayi don hatta suturar jikin shi duk sun yayyage,
Sai watarana mahaifiyar shi tace ya kai Mus,ab kadawo vikin addinin mu kafita,wanan addinin na islama, da kashiga
Amma sai Mus,ab yaki suka dinga azabatar da shi azaba mai tsanani, amma yaki ya tsaya akan addinin shi na islama,
Daga karshe ya koma gurin Annabi Muhammad, (SAW),
Ya hakkura da duk wani daular duniya da ake kwadaita mashi, anan
Yusuf yanisa ya waiga inda yake tsaye a bakin window,
Yace a ranshi kida Dad zai kwace mai duk wani abu da ya mallaka bazai fita cikin addinin islama ba,
Shi yanzu yasan cewa yafi karfin duk wani barazana da mahaifin shi zai mai akan dukiya,
Kwana biyu kawai yayi da hutawa, ya shirya don zuwa ya dibo, kakarshi wace bai san halin da take ciki ba a yanzu,
Ba karamin tausayi matar yake ji ba a matsayin ta na wanda, ta rage mai yake gani kamar uwar shi,
Tana zaune ta mike kafa a saman wani tabarman roba, a gefen da dan inwa yakai acikin gidan nata ,
Sai ganin shi tayi kamar a mafarki don sam batayi tsan manin cewa zata kara ganin shi arayuwar taba ,
Tadade rungumay dashi a jikin ta tana kuka tana wani gwalanci irin na yare,
Sai kuma komay ta tuna tasake shi da sauri tana ta tatabashi kamar tana tuhumar ko ba shi bane a gabanta,
My child are still in that religion ?
Mumushi yayi ya jawo goshinta ya man,na da nashi yace mata
Even you mama you will joined me, very soon
Dan tura shi tayi baya yawuce tangal, tangal kamar zai fadi,
Dariya tabashi a yadda yaga tanayi don daga hannun ta tayi tana wani kewaya shi a saman kanta tana cewa over my death body,
Komawa tayi ta zauna tana wani bubuga kafa wai ita tayi fushi,
Direct wuce yayi zuwa cikin dan falon ta na ginar kasa wanda saboda tsufa har yana batun zubewa,
Photo mahaifiyar shi ce yai tozali da shi, wace ke saye da wani zanin irin na matan IBO,ta daura wani dankwali daurin gwagwaro,
Murmushi takeyi da aka dauke ta kamar zatai magana
Yadade yana kallon photo yana maiji dama ace ta musulunta ka fin ta mutu,
Shigowar grandmother, yasa,shi barin gurin zuwa saman tsofin kujerun dake falon,
Itama zama tayi saman kujerar dake gab dashi, tana mai mai kallo cikin da muwa,
Shine yafara magana yana mai tambayar ta may yasa ta dawo kauye da zama,
Bayan tasan cewa babu wani wanda zai kula da ita anan yanzu,
Yace ga gidan shi can abirni babu kowa aciki mai yai hana taje can ta zauna,
Saida mama tadan waiga kamar akwai wani gidan wanda zai ji abin da zata fadi alokacin,
Tadan kara gyarazaman ta har kusa dashi tace,
That your father is very wicked,
He can killed person, woo
Nan take sheda mai cewa bayan tafiyan shi taji mahaifin nashi na waya da wasu cewa a kama Joseph ai masa duk wani horo da ya dace dashi don yadawo cikin Christianity,
Murmushi yai mata don dama yasan cewa shine ke turowa ai mai wanan wulakancin,
A ranan Yusuf bai yarda ya kwana wanan dan kauyen da yar tsohuwar ba dawowa sukayi tare,
Inda taga duk gidan ya canza mata saboda gyare,gyaren da akayi wa gidan,
Sosai gidan ya canza mata cikin dan lokaci har ta rasa gane ko ina ne part din ta na da,,
Ganin Ejoma da tayi tazo taron ta yasa ta gane cewa lalai agidan shi suke,
Wanan karon sosai ya shirya ma shiga garin na kwantagora
Badon komai ba sai don ya tunkari mahaifin shi wanda ke ta yi mashi bita da kulli,
Motorcine har guda uku yatanada don wanan tafiyan,da yake son yi kafin ya fara harkokin gaban shi,
Saidai wanan karon ba,a gidan mahaifin shi zai saukaba kamar yadda ya saba,
Hotel lafiyayye aka kama masu tun kafin su iso garin,
Har abincin da zasu ci an tanadar masu shi, KB ne yai wanan hidimar,
Zaune take tana kwalliya a bakin mirror saboda tana expecting din zuwan A,Adin ta,
Muryarda taji yana sallama tuni zuciyar ta, ta tsinke
Zabura tayi saye a dan tsorace, tadan saurara ko kunnuwar take mata karya,
Bashi bane a zahiri don sam ba su tsan manin cewa zai zo a wanan lokacin ba,
Muryam Anty Dije ce ya kara tabbatar mata da cewa shi din dai ya shigo,
Inda taji Anty na tacewa sannu da zuwa Yusuf
Kaine tafe babu ko labari, zuwa balle a shirya ma,zuwan naka,
Wani murmushi yayi mai sauti yace bana son ku wahala ne ai shiya sa ban fada maki ba,
Sigar dayake magana kawai zai tabbatar ma da ya kara samun canji a rayuwa,
A,hankali yake karasowa zuwa inda anty take dauke da Abubakar a hannun ta,
Ya saye da wani yadi mai laushi baki ajikin shi sai wata yar jar hular dara dayasa wa kanshi,
Gadan gadan yanu yau,fi inda take da yaron dagani duk hankalin shi na gurin yaron, wanda bai taba gani ba, sai
Cak yadauki Abubakar yafara dan wasa dashi ,daidai gitowar Maryam wace kamshin ta kawai kawai, zai saka gane tafito,
A hankali ta iya furta mai sannu da zuwa,daga haka tasa kai da niyar fita kawai,
Gabantane yafadi saboda ganin yadda Yusuf ya canza gabadaya cikin lokaci guda,,,,,,,
ZEEE. MAKAWA
[3/7, 1:14 PM]